Sashe 31
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin garin Bonon kuwa, gaba ɗaya, matasan garin dama ƙauyuka gefensu na ƙabulun Ɓachamawa, duk sun hallara wuri ɗaya, suna cike gaban dodon tsafinsu, wato Bonon ɗin, giyar burkutu mai ɗan karen tsami da wari, suketa sha, tamkar zasu fasa cikkunansu.
Yayinda gefe guda kuma, maƙerar dake gefe wasu matasa su ne maƙera keta wasa ababen faɗansu, kamarsu wuƙaƙe, Adda, sitaka, barandami, mashi, kibau, da dai sauran mugayen makamai, sai sheƙi sukeyi.
Suna cike a wurin, Ba'ana ya iso, cikin wata shigar rigar saƙi.
Hanya suka rinƙa buɗa mishi, hardai ya isa ga sarkinsu, dake zaune gefen dodo sun. Zama yayi kusa da sarkin nasu ya sasu a gaba,
Cikin harshen ɓacamancin yace.
"Ku hanzarta, ku shiga, duk matasansu majiya ƙarfi, sun tafi kiwo. Dottijan su kuma sun tafi, kai gulmarku, ga Sarkin su wannan karon basu tsaya ga sarkinku na nanba, ina da yaƙinin kuma za'a sauraresu a can.
Yanzu matansu da ƴaƴansu, ƙanana mata da mazane suka rage a garin.
Sai wasu dattawansu dake, dakon dawowar magulmatan can.
Kuyi maza, kushiha kafin su dawo, ku share garin kab.
Ku kashesu gaba ɗaya babba da yaro mace dana miji."
Da sauri wani daga cikin su yace.
"Harda gidansu Shatu?".
Cikin izaya yace.
"Harda su, domin Mata, bata nan, ku kashe kowa nata, ta hakane zata dogara dani kaɗai tunda bata da kowa nata a duniya, dole Ni zan zama mijinta ubanta yayunta ƙannenta uwarta, in zama Garkuwarta in zame mata duniyarta ta hakane zata yarda nine ɗaya gatanta kuma duniyarta, ba tare da ta zargeniba, a hankali wata rana in sata tayi ridda, musha giya, muyi tsafi tare da ita, bazatayi min musuba, mu haifi ɗanmu na forko mu bawa dodonmu yasha jininshi yasa mana al'barka a aurenmu".
Wani irin ihu da sowa na tsantsar jin daɗin bayaninshi sukayi baki ɗayansu.
Hakama dodonsun, saida ihunshi ya firgitasu baki ɗayansu.
Dariya mai amo mara daɗin ji. Sarkin nasu yayi, kana ya busa ƙahon dodonsun, alamun ya basu izinin tafiya.
Nan fa duk suka rinƙa shiga, cikin maƙerarnan suna ɗaukan makamai, suna nufar garin Rugar Kikan (Rugar Bani) kenan a guje...
Cikin garin Shikan kuwa, Bani rana ta fara tasawa, mata masu zuwa tallan nono cikin garin Numan, suka fara ɗaukar ƙorarensu, suna fita garin.
Yara maza da mata kuwa, wasu na wasa wasu na ɗebo ruwa, wasu na ɗebo kayan lamɓu.
Yayinda wasu kuma suka dawo break dan tara tayi.
Cikinsu kuwa harda Junainah.
Tafe take da saurinta da ɗan tsalle-tsallenta tana rataye da yar jakarta,
da sauri ta tsaya ganin Junaidu a gabanta rike da kwanɗon zabari wanda yake cike da ƴaƴan itatuwa.
Murmushi ta ɗanyi tare da sunkuyar da kanta cikin surutunta tace.
"Har naji tsoro!".
ta ƙarishe mgnar tana kallonshi,
Murmushi yayi mata shima cikin son ƴarinyar yace.
"Haba dai, tsoron me kuma zakiji, tunda gani, babu abinda zai sameki muddin ina raye, zan zame miki Garkuwa".
Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta tare da cewa.
"Kai! Kai! Ya Junaidu, sunan Babanmufa ka kira".
Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace.
"Au na manta ashe sunan surki nane".
Kai ta gyaɗa mishi kana tasa hannu ta amshi, nonon inabin da yake miƙa mata,
baki ta buɗe da nufin sawa a baki,
sai kuma ta tsaya tare da tura baki jin yana ce mata.
"No kada kici ba'a wonke bafa."
Sai kuma ya ajiye kondon, ya amshi inabin ya ɗan gangara, gefe kaɗan ya wonkeshi a bakin ruwan wutsiyar Kogin da yayiwa Rugar tasu ƙawanya.
Ya tahowa tana kallonshi.
Koda ya iso miƙa mata yayi,
kana ya ɗauki kondon, ganin still tanata kallonshi ne ya sashi cewa.
"Ya dai?".
Kai ta kauda tare da fara tsinkar ƴaƴan inabin tana afawa a baki tana taunawa,
Murmushi ya kumayi ganin yadda ta lumshe idonta.
A hankali tace.
"Ya Junaidu kayi kyau sosai yau, har kamar ka fini kyau".
Dariya ya ɗanyi kana yace.
"Yo dama ai na fiki kyau".
Maƙe kafaɗa tayi tare da cewa.
"Uhum a a kam".
A haka dai suna tafe suna hira.
Can cikin gida kuwa, Ummiy ce zaune bisa kujera ƴar tsuguno da buta a gabanta, alamun al'walan sallan walaha, zatayi.
Inna kuwa, da wasu maƙotansu uku Biba, Hari, da Innawuro. suna zaune bisa taburma a tsakar gidan. Suna amsar gaisuwa.
Can cikin garin kuwa su Alhamdulillah Manu dasu Siddine da dai sauran dattawan garin ne zaune a fada.
Sai yara daketa kai komo.
Da sauri su Siddi suka miƙe tsaye ganin, matasan mayaƙan ƙabilar ɓachama, sunata shigowa garin tako ina gabas da yamma kudu da Arewa, bisa dukkan alamu zobe sukayiwa garin
Kana ga zurma-zurman makamai masu tsawo tamkar raƙumai. Sai sheƙi sukeyi.
Cikin ɗaga murya, Alhaji Manu yace.
"Kai lfy? me haka?".
Ganin sun nufosu gadan-gadan ne yasa, suka miƙe gaba ɗayansu, kowa ya fara, neman makari, to amman ina, basu da zato ko sanin za'a far musu, shiyasa basu da shirin komai na kare kai.
Ɗaya daga cikin sune, yace.
"Mu gudu kashemu sukeda shirin yi ba tare da laifin komaiba".
Siddine ya kuma ɗaga murya tare da cewa.
"To in mun gudu matanmu da yaranmu fa".
Ihun da sukajiyo tako wani sashi na garinne ya tambatar musu, ana karkashe su.
Gudu suka farayi kowa ya nufi hanyar gidanshi dan ɗaukar matakan kare kai.
Sai dai ina basu da hanya duk inda suka ɓullo sai sunci karo da, mayaƙan.
Lokaci ɗaya garin ya ruɗe ya birkice kota ina sai ife-ife da gudun ceton rai da makiyayan Rugar Kikan keyi.
Wani irin sauti mai baiyana azabar fitan rai Alhaji Manu yayi, lokacin da wani kafurin ya caka mushi sitaka a ƙahon zuciyarshi.
Siddine ne ya juyo da azaban razani, amman sai shima ya saki wani sauti mai gigitarwa jin azaban sara da sukan da akeyi mishi.
Garifa ya kacame,
Hadi ne babban ɗa ga Alhaji Haro mahaifinsu Junaidun Junainah, ya nufi cikin gidansu da azama,
Yana cike da fargaba, da tashin hankali domin wasu irin ihu da yake jiyowa a cikin gidan nasu.
Yana kusa kai ya samu, makasan suna cike a gidan.
Suna ta'addanci, sun kashe kowa na gidan.
Ganin haka ya juyo yana juyowa. Yayi kiciɓis da abokinshi Sale, yana tafe jini na zuba an farka mishi ciki.
Cikin magagin mutuwa yake cewa.
"Hadi sun kashe kowa na garin nan sai wanda baya nan.
Hadi na kira Hukumar yan sanda ta nan cikin Numan na shaida musu, amman kafuran nan maƙiya Allah da Manzonsa sai cewa sukayi,
A kashe mu mana, ai an rage musu aikine.
Na kira su Arɗo Bani, suna ɗagawa katin wayata ya ƙare.
Hadi sun kashe kowa na gidanmu.
Taroshi Hadi yayi suka faɗa nan suna kuka mai cike da taraddadin rabuwa.
Cikin ƙarfin hali Sale ya ture Hadi tare da cewa.
"Ka gudu Hadi ku gudu, Ni nasan bazan rayuba.
Ka gudu.
Sun kashe min Kowa har jariren tagwayen da aka haifa min shekaran jiya, sun kashesu.
Cikin kuka Hadi yace.
"Bazan iya guduba Sale su kasheni kawai, ina zanje bayan sunyiwa garin zobe.
Da ƙarfi Hadi ya abka jikin Sale Jin ansa gatari an sari kafaɗarsa ta dama,
Juyowar da zaiyi kuma aka tsira mishi mashi a ƙirji.
Nan take ya cika, hakama Sale.
Cikin gidansu Shatu kuwa.
Ummiy ta sallame sallan kenan, taji.
Inna dasu Innawuro suna kurma ihu da salati.
Yunƙurawa tayi da azama jiki na rawa ta nufo woje.
Fitowanta yayi dai-dai da lokacin da aka sare kan Innawuro, wanda kan yayi tsalle ya faɗo kanta, kana ya gangara ya faɗa gabanta.
Wani irin ihu mai cike da karaji gauraye da salati ta kurma lokacin da taga an burmawa Inna mashi a ciki.
Ihunta da salatinta ya jawo hankalin su, sukayo kanta.
Sai dai kafin su isoma ta yanki jiki ta faɗi babu numfarfashi tamkar matacciya.
Koda suka iso, dariya suka kece da ita cikin rashin imani ɗayansu yasa ƙafa, ya taka ruwan cikinta, tare da cewa.
"Shegun FULANI ku mutu, mu huta, da ganinku a garinmu, gonakinku da dabobbin ku duk sun zama namu.
Mu ɗauke yaranku mata mu maidasu karuwanmu, muyi musu ciki su haihu mu bawa dodo.
Muji daɗi dasu.
Ganin kamar ta mutune yasa suka tattakata suka wuce suka fita daga gidan.
Junainah kuwa da Junaidun, suna gab da shigowa garin suka fara jiyo ihun mutanen garin.
Cikin azaban firgici Junaidu ya wurgar da kondon ƴaƴan itatuwan dake hannunshi,
da gudu yabi bayan Junainah data ruga a guje sabida hango, anata kashe mutane a gabansu.
Cikin kuka da tarin kiɗima da fita haiyacinta take cewa.
"Wayyo Ummiy Wayyo Inna Wayyo Bappa, zasu kashemu.
Wayyoooooooo Adda Shatu zasu kashemu".
Riƙo hannunta yayi da ƙarfi cikin rawan jiki da murya yace.
"Junainah bazasu kashekiba, zan kareki da izinin ubangiji, zaki rayu, Shatu bazata rasa kowa duniya ba.
Junainah zan zame miki Garkuwa zan fanshi ranki da nawa ran.
Ki zama tamkar yar tsira, Shatu ta zama tamkar yar jarida, ta rubutawa mutanen duniya su karanta, kisan gillan da akeyiwa Fulani mazauna daji.
Da ƙarfi yasa hannu ya zaro wukar dake ƙugunshi wanda da ita ya yayyanki nonunan ayaba dasu inabi.
Wayarshi ya kuma zarowa
Ya Salmanu ya kira,
Salmanu kuma dake, kwance a gadon asibitin nan Genaral Hospital Numan.
Wanda bai workeba tun dukan shaɗi da ba'ana ya mishi.
A hankali yasa hannunshin ya amsa kiran wayarshi ganin Junaidu ke kiranshi.
Cikin kiɗima da firgici Junaidu yace.
"Ya Salmanu, mayaƙan ƙabilar ɓachama sun shigo Rugar mu, sunata kashemu, mazanmu da matanmu.
Ya Salmanu Junainah ina son ta tsira, ko dan ran Junainah ka kira mana hukumar yan sandan cikin Adamawa, ina son su iso su ceci Junainah kada Shatu ta rasa kowa a duniya.
Ban saniba ko zan gazawa bawa Junainah tsaro".
Gaba ɗaya jikin Salmanu rawa da tsuma yakeyi, katse kiran yayi da sauri ya kira.
"A.S.P Kabiru Nasir. Wanda yake, Hetkotan Adamawa.
Koda ya mishi jawabin abinda ke faruwa, a take. A.S.P ya kira.
S.P Daniyel dake Numan ya bashi doka da oda maza-maza su bawa fulanin Rugar Kikan tsaro gaggawa, shima yana nan tafe da rundunar sa. Ya bashi umarni mai ƙarfi ya ƙara da cewa, muddin yazo ya samu ba dai-dai ba ta ɓanƙaren tsaro, to akan aikinshi.
Yayinda gefe guda kuma, maƙerar dake gefe wasu matasa su ne maƙera keta wasa ababen faɗansu, kamarsu wuƙaƙe, Adda, sitaka, barandami, mashi, kibau, da dai sauran mugayen makamai, sai sheƙi sukeyi.
Suna cike a wurin, Ba'ana ya iso, cikin wata shigar rigar saƙi.
Hanya suka rinƙa buɗa mishi, hardai ya isa ga sarkinsu, dake zaune gefen dodo sun. Zama yayi kusa da sarkin nasu ya sasu a gaba,
Cikin harshen ɓacamancin yace.
"Ku hanzarta, ku shiga, duk matasansu majiya ƙarfi, sun tafi kiwo. Dottijan su kuma sun tafi, kai gulmarku, ga Sarkin su wannan karon basu tsaya ga sarkinku na nanba, ina da yaƙinin kuma za'a sauraresu a can.
Yanzu matansu da ƴaƴansu, ƙanana mata da mazane suka rage a garin.
Sai wasu dattawansu dake, dakon dawowar magulmatan can.
Kuyi maza, kushiha kafin su dawo, ku share garin kab.
Ku kashesu gaba ɗaya babba da yaro mace dana miji."
Da sauri wani daga cikin su yace.
"Harda gidansu Shatu?".
Cikin izaya yace.
"Harda su, domin Mata, bata nan, ku kashe kowa nata, ta hakane zata dogara dani kaɗai tunda bata da kowa nata a duniya, dole Ni zan zama mijinta ubanta yayunta ƙannenta uwarta, in zama Garkuwarta in zame mata duniyarta ta hakane zata yarda nine ɗaya gatanta kuma duniyarta, ba tare da ta zargeniba, a hankali wata rana in sata tayi ridda, musha giya, muyi tsafi tare da ita, bazatayi min musuba, mu haifi ɗanmu na forko mu bawa dodonmu yasha jininshi yasa mana al'barka a aurenmu".
Wani irin ihu da sowa na tsantsar jin daɗin bayaninshi sukayi baki ɗayansu.
Hakama dodonsun, saida ihunshi ya firgitasu baki ɗayansu.
Dariya mai amo mara daɗin ji. Sarkin nasu yayi, kana ya busa ƙahon dodonsun, alamun ya basu izinin tafiya.
Nan fa duk suka rinƙa shiga, cikin maƙerarnan suna ɗaukan makamai, suna nufar garin Rugar Kikan (Rugar Bani) kenan a guje...
Cikin garin Shikan kuwa, Bani rana ta fara tasawa, mata masu zuwa tallan nono cikin garin Numan, suka fara ɗaukar ƙorarensu, suna fita garin.
Yara maza da mata kuwa, wasu na wasa wasu na ɗebo ruwa, wasu na ɗebo kayan lamɓu.
Yayinda wasu kuma suka dawo break dan tara tayi.
Cikinsu kuwa harda Junainah.
Tafe take da saurinta da ɗan tsalle-tsallenta tana rataye da yar jakarta,
da sauri ta tsaya ganin Junaidu a gabanta rike da kwanɗon zabari wanda yake cike da ƴaƴan itatuwa.
Murmushi ta ɗanyi tare da sunkuyar da kanta cikin surutunta tace.
"Har naji tsoro!".
ta ƙarishe mgnar tana kallonshi,
Murmushi yayi mata shima cikin son ƴarinyar yace.
"Haba dai, tsoron me kuma zakiji, tunda gani, babu abinda zai sameki muddin ina raye, zan zame miki Garkuwa".
Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta tare da cewa.
"Kai! Kai! Ya Junaidu, sunan Babanmufa ka kira".
Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace.
"Au na manta ashe sunan surki nane".
Kai ta gyaɗa mishi kana tasa hannu ta amshi, nonon inabin da yake miƙa mata,
baki ta buɗe da nufin sawa a baki,
sai kuma ta tsaya tare da tura baki jin yana ce mata.
"No kada kici ba'a wonke bafa."
Sai kuma ya ajiye kondon, ya amshi inabin ya ɗan gangara, gefe kaɗan ya wonkeshi a bakin ruwan wutsiyar Kogin da yayiwa Rugar tasu ƙawanya.
Ya tahowa tana kallonshi.
Koda ya iso miƙa mata yayi,
kana ya ɗauki kondon, ganin still tanata kallonshi ne ya sashi cewa.
"Ya dai?".
Kai ta kauda tare da fara tsinkar ƴaƴan inabin tana afawa a baki tana taunawa,
Murmushi ya kumayi ganin yadda ta lumshe idonta.
A hankali tace.
"Ya Junaidu kayi kyau sosai yau, har kamar ka fini kyau".
Dariya ya ɗanyi kana yace.
"Yo dama ai na fiki kyau".
Maƙe kafaɗa tayi tare da cewa.
"Uhum a a kam".
A haka dai suna tafe suna hira.
Can cikin gida kuwa, Ummiy ce zaune bisa kujera ƴar tsuguno da buta a gabanta, alamun al'walan sallan walaha, zatayi.
Inna kuwa, da wasu maƙotansu uku Biba, Hari, da Innawuro. suna zaune bisa taburma a tsakar gidan. Suna amsar gaisuwa.
Can cikin garin kuwa su Alhamdulillah Manu dasu Siddine da dai sauran dattawan garin ne zaune a fada.
Sai yara daketa kai komo.
Da sauri su Siddi suka miƙe tsaye ganin, matasan mayaƙan ƙabilar ɓachama, sunata shigowa garin tako ina gabas da yamma kudu da Arewa, bisa dukkan alamu zobe sukayiwa garin
Kana ga zurma-zurman makamai masu tsawo tamkar raƙumai. Sai sheƙi sukeyi.
Cikin ɗaga murya, Alhaji Manu yace.
"Kai lfy? me haka?".
Ganin sun nufosu gadan-gadan ne yasa, suka miƙe gaba ɗayansu, kowa ya fara, neman makari, to amman ina, basu da zato ko sanin za'a far musu, shiyasa basu da shirin komai na kare kai.
Ɗaya daga cikin sune, yace.
"Mu gudu kashemu sukeda shirin yi ba tare da laifin komaiba".
Siddine ya kuma ɗaga murya tare da cewa.
"To in mun gudu matanmu da yaranmu fa".
Ihun da sukajiyo tako wani sashi na garinne ya tambatar musu, ana karkashe su.
Gudu suka farayi kowa ya nufi hanyar gidanshi dan ɗaukar matakan kare kai.
Sai dai ina basu da hanya duk inda suka ɓullo sai sunci karo da, mayaƙan.
Lokaci ɗaya garin ya ruɗe ya birkice kota ina sai ife-ife da gudun ceton rai da makiyayan Rugar Kikan keyi.
Wani irin sauti mai baiyana azabar fitan rai Alhaji Manu yayi, lokacin da wani kafurin ya caka mushi sitaka a ƙahon zuciyarshi.
Siddine ne ya juyo da azaban razani, amman sai shima ya saki wani sauti mai gigitarwa jin azaban sara da sukan da akeyi mishi.
Garifa ya kacame,
Hadi ne babban ɗa ga Alhaji Haro mahaifinsu Junaidun Junainah, ya nufi cikin gidansu da azama,
Yana cike da fargaba, da tashin hankali domin wasu irin ihu da yake jiyowa a cikin gidan nasu.
Yana kusa kai ya samu, makasan suna cike a gidan.
Suna ta'addanci, sun kashe kowa na gidan.
Ganin haka ya juyo yana juyowa. Yayi kiciɓis da abokinshi Sale, yana tafe jini na zuba an farka mishi ciki.
Cikin magagin mutuwa yake cewa.
"Hadi sun kashe kowa na garin nan sai wanda baya nan.
Hadi na kira Hukumar yan sanda ta nan cikin Numan na shaida musu, amman kafuran nan maƙiya Allah da Manzonsa sai cewa sukayi,
A kashe mu mana, ai an rage musu aikine.
Na kira su Arɗo Bani, suna ɗagawa katin wayata ya ƙare.
Hadi sun kashe kowa na gidanmu.
Taroshi Hadi yayi suka faɗa nan suna kuka mai cike da taraddadin rabuwa.
Cikin ƙarfin hali Sale ya ture Hadi tare da cewa.
"Ka gudu Hadi ku gudu, Ni nasan bazan rayuba.
Ka gudu.
Sun kashe min Kowa har jariren tagwayen da aka haifa min shekaran jiya, sun kashesu.
Cikin kuka Hadi yace.
"Bazan iya guduba Sale su kasheni kawai, ina zanje bayan sunyiwa garin zobe.
Da ƙarfi Hadi ya abka jikin Sale Jin ansa gatari an sari kafaɗarsa ta dama,
Juyowar da zaiyi kuma aka tsira mishi mashi a ƙirji.
Nan take ya cika, hakama Sale.
Cikin gidansu Shatu kuwa.
Ummiy ta sallame sallan kenan, taji.
Inna dasu Innawuro suna kurma ihu da salati.
Yunƙurawa tayi da azama jiki na rawa ta nufo woje.
Fitowanta yayi dai-dai da lokacin da aka sare kan Innawuro, wanda kan yayi tsalle ya faɗo kanta, kana ya gangara ya faɗa gabanta.
Wani irin ihu mai cike da karaji gauraye da salati ta kurma lokacin da taga an burmawa Inna mashi a ciki.
Ihunta da salatinta ya jawo hankalin su, sukayo kanta.
Sai dai kafin su isoma ta yanki jiki ta faɗi babu numfarfashi tamkar matacciya.
Koda suka iso, dariya suka kece da ita cikin rashin imani ɗayansu yasa ƙafa, ya taka ruwan cikinta, tare da cewa.
"Shegun FULANI ku mutu, mu huta, da ganinku a garinmu, gonakinku da dabobbin ku duk sun zama namu.
Mu ɗauke yaranku mata mu maidasu karuwanmu, muyi musu ciki su haihu mu bawa dodo.
Muji daɗi dasu.
Ganin kamar ta mutune yasa suka tattakata suka wuce suka fita daga gidan.
Junainah kuwa da Junaidun, suna gab da shigowa garin suka fara jiyo ihun mutanen garin.
Cikin azaban firgici Junaidu ya wurgar da kondon ƴaƴan itatuwan dake hannunshi,
da gudu yabi bayan Junainah data ruga a guje sabida hango, anata kashe mutane a gabansu.
Cikin kuka da tarin kiɗima da fita haiyacinta take cewa.
"Wayyo Ummiy Wayyo Inna Wayyo Bappa, zasu kashemu.
Wayyoooooooo Adda Shatu zasu kashemu".
Riƙo hannunta yayi da ƙarfi cikin rawan jiki da murya yace.
"Junainah bazasu kashekiba, zan kareki da izinin ubangiji, zaki rayu, Shatu bazata rasa kowa duniya ba.
Junainah zan zame miki Garkuwa zan fanshi ranki da nawa ran.
Ki zama tamkar yar tsira, Shatu ta zama tamkar yar jarida, ta rubutawa mutanen duniya su karanta, kisan gillan da akeyiwa Fulani mazauna daji.
Da ƙarfi yasa hannu ya zaro wukar dake ƙugunshi wanda da ita ya yayyanki nonunan ayaba dasu inabi.
Wayarshi ya kuma zarowa
Ya Salmanu ya kira,
Salmanu kuma dake, kwance a gadon asibitin nan Genaral Hospital Numan.
Wanda bai workeba tun dukan shaɗi da ba'ana ya mishi.
A hankali yasa hannunshin ya amsa kiran wayarshi ganin Junaidu ke kiranshi.
Cikin kiɗima da firgici Junaidu yace.
"Ya Salmanu, mayaƙan ƙabilar ɓachama sun shigo Rugar mu, sunata kashemu, mazanmu da matanmu.
Ya Salmanu Junainah ina son ta tsira, ko dan ran Junainah ka kira mana hukumar yan sandan cikin Adamawa, ina son su iso su ceci Junainah kada Shatu ta rasa kowa a duniya.
Ban saniba ko zan gazawa bawa Junainah tsaro".
Gaba ɗaya jikin Salmanu rawa da tsuma yakeyi, katse kiran yayi da sauri ya kira.
"A.S.P Kabiru Nasir. Wanda yake, Hetkotan Adamawa.
Koda ya mishi jawabin abinda ke faruwa, a take. A.S.P ya kira.
S.P Daniyel dake Numan ya bashi doka da oda maza-maza su bawa fulanin Rugar Kikan tsaro gaggawa, shima yana nan tafe da rundunar sa. Ya bashi umarni mai ƙarfi ya ƙara da cewa, muddin yazo ya samu ba dai-dai ba ta ɓanƙaren tsaro, to akan aikinshi.