Sashe 58
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abbansu kuwa, shi dai har yau yana rasa me yakeji a kan ƴaƴan nashi, Especially Sheykh, yana jin zuciyarshi na mishi nauyi duk sanda yaron baya kusa dashi, sai dai kuma in yana kusa dashi sai yaji tamkar bai taɓa wani farin cikiba a rayuwarsa.
Ya sani tabbas su abun tausayawa ne, suna buƙatar kulawarshi fiye data kowa a duniya, to amman ya rasa meyasa yake jin kamar baya son kusancisa dasu.
Maimartaba kuwa, suna cikin sahun na forko bayan liman,
Sai da sauran malaman fada.
A cikin gida kuwa, jin sautin zazzaƙar miryarshi yana rere karatun al'ƙur'ani, ya ida fatiha, kana ya ɗaura, Arrahama,
daga bisani ya rufe da lakadja'akum, kafin ya tafi zuwa ruku'uh.
Haka nan Juwairiyya ta tsinci kanta da zubda wasu zafafan hawaye, masu ƙuna a rai, tabbas ta sani.
Kasan cewar Sheykh a masarautar nanne kaɗai yasa, suke a ciki.
Ta sani in badon daraja da al'farmarsa ba, da tun tuni, an tabbatar da sunan mijinta mahaukaci.
Hannu tasa ta share hawayenta cikin sanyi ta miƙe dan gabatar da sallan asuba, a zahiri tace.
"Allah ne gatanmu, kaine GARKUWAR mu, Sheykh in baka nan gidan kanyi mana duhu, ƙasar tanayi mana zafi."
Daga nan ta tada kabbara.
Ummi Jakadiyarsu kuwa,
Tana bayan gida, tana al'wala ta jiyo muryarshi, wani irin murmushi tayi tare da yin mgna a baiyane.
"Dan Halak kaƙi ambato, ɗa ɗaya tamkar dubu, maƙiyanka fadawanka, sunyi sake ɗan zaki ya girma, in sha Allah zaka dawo da farin cikin masarautarnan, sunyi sake, sun bar kari tun ran tubani,
Muhammad Jabeer bawan Allah".
Haka ta fito tana wasu irin kalamai masu wuyar fahimta.
A can sashin Hajia Mama kuwa,
Wata kekyawar budurwa, ce.
Konce kan gado gefen Mama, datake zaune bisa sallaya.
jiyo muryashine ya sasu saurin juyowa, suka kalli juna,
Cikin tsananin farin ciki da tarin shauƙi budurwar ta diro daga kan gadon gaban Mama ta zauna cikin zaƙuwa tace.
"Lah Mama, yaushe ya dawo! Muryar Sheykh Jabeer nake jifa! Mama ko dai dama yana nanne?".
Wani irin kallo Mama tayi mata cikin sanyi da murmushi a fuskarta tace.
"Batul shine, ya dawo!."
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe cikin tarin shauƙi tace.
"Yes Mama, farin cikina ya dawo, kamar yasan, nazo.
Alhamdulillah, Mama Allah yana sona, ki gani ina zuwa, na samu baya nan, naji baƙin ciki kamar in mutu jiya kafin inyi bacci, sai gashi Allah ya turo minshi cikin dare ɗaya."
Murmushi Mama tayi, tana mai jin mmkin yadda Batul ke masifar son Sheykh har take gaza ɓoyewa.
cikin haɗe fuska tace.
"To yanzu dai, sai ki tashi kiyi salla, tunda kinji muryar da kikafi so a duniya, kin sauƙo kan gadon, sau nawa ina tadake, sai kiyi miƙa ki kuma konciya".
Cikin jin dadi tace,
"Wayyo Mama baccinne bai isheniba Allah ko jiya kwana nai ina zulumi, sai 3:44 na asuba na samu bacci."
Murmushi Mama tayi kana ta miƙe ta kabbarta sallan.
Ita kuwa Batul, miƙewa tayi da sauri ta shige, bathroom tana cewa.
"Bari inyi wonka inyi salla, in shiga kitchin yau nida kaina zan mishi breakfast."
Tana faɗin haka ta shige ciki.
A masallaci kuwa, ana idar da salla kamar koda yaushe, da yawa basu fitaba saida sunata lazumi.
Yayinda Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da kuma Sarki Nuruddeen Bubayero, da Habibullah Nuruddeen Bubayero, suka jero, suka fito a jere, domin su kullum ana idar da sallan asuba, suke fitowa su koma cikin masarautar, inda kowa zai wuce Side ɗinsa,
Yayi karatun qur'ani da kuma, Dua Azkar, inda har sai rana ta fito, kana suke ɗan maida bacci, to kuma sudayin breakfast sai 11.
Suna isowa tsakiyar masallaci, Sheykh yaji an ruggumeshi ta baya, yasan mutun ɗaya ne rak zai mishi haka a cikin masallacin,
Ya Jafar ɗinsu.
Yana juyowa kuwa yaga shiɗin ne.
Ruggumeshi yayi gam-gam Jalal, kuwa ido ya zuba musu,
shi kuwa Sheykh hannu yasa shima ya ruggume ɗan uwan nashi.
Yayinda ya zubawa Jalal kwayar idanunshi, ya rame sosai, hancinsa ya ƙara fitowa, sai sajenshi daya ƙara yin lib, da uban gashin daya tara, yayi wani kafurin aski.
Ramar da Jalal yayi ta daki zuciyarsa sosai baya son ganin ƙannen nashi cikin halin matsala,
a hankali ya janye kwayar idanunshi ya maidasu kan Jamil da Affan dake gefen damanshi,
Calikan ƙanenneshi kenan ba,
sheƙiyancinsu ɗaya, baki suka haɗa wurin cewa.
"Sabahul Noor Al'Sheykh".
A hankali ya ɗan motsa laɓɓansa, yana mai kallonsu yace.
"Sabahul khair ya Uktih".
murmushi sukayi, suna mai jin son ɗan uwan nasu,
Abbs da Maimartaba kuwa, kai suka ɗan jinjina kana sukayi gaba,
Ganin hakane suma suka bisu, a baya,
shi kuwa Sheykh hannu yasa ya shafa kan Imran da yanzu ya iso gabanshi cikin sanyi yace.
"Hamma Jabeer barka da safiya".
jin yana shafa kanshine ya sashi lumshe ido, inama ace yadda Hammanshi ke nuna mishi so haka zai shirya da Mom ɗin shi, yana masifar son ɗan uwanshi baya jin daɗin yadda yake ganin wata iriyar mu'amala tsakanin Mom da yayunshi.
Ganin Sheykh yaja hannun Ya Jafar sun tafine yasashi bin bayansu.
Ƙofar dake cikin masallacin wacce zata ɓulla cikin masarautarsu sukabi.
Suna shiga, kowa yayi sashinsa sabida sun sani ko sunbi Sheykh yanzu ba lokacin mgna bane, karatu zaije yayi.
Shi kuwa Sheykh yana riƙe da hannun Ya Jafar ɗinsa suka shiga side ɗinsa,
inda ya samu hadimai masu tsaron ƙofar, suna tsaye.
Suna shiga, tamtsetsen falon nashi kai tsaye ya nufi wannan babbar kusurwar da zata sadashi da.
Big part ɗin shi,
Suna shiga suka ɓulla cikin wani mashahurin, falo, wanda yaketa tashin ƙamshi mai masifar sanyi da daɗin shaƙa,
a hankali ya zauna bisa kujerar 3 str kana yaja hannun Ya Jafar ɗin suka zauna, tare.
A hankali ya juyo kanshi ya zuwa ɗan uwanshi idonu,
Karatu yakeyi kamar koda yaushe, yanayi cikin tsantsar lugga da tajwid, kana ga kushu'i,
Suratul yaseen yake karanta,
bisa alamu kenan ya kusa yayi sauƙa, domin step by step yake bin surorin, in yayi sauƙa sai ya sako daga sama, baya mancewa, kuma baya birkitashi,
Wannan rahamar da Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina, amman banda gefen addininshi.
Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi,
sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za'ayi ya sama mushi farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi.
Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi,
Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon suratul. Noor ya farayin ƙasa.
Saida sukayi awa ɗaya cur kana,
Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu'o'in cikin harshen dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga.
Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam.
Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi.
Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana,
ya miƙa tare da jawo hannunshi,
yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne,
Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu.
A babban falon suka samu Juwairiyya.
Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da hawaye tace.
"Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar".
Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta,
Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi,
cikin murmushi ta nitsuwa yace.
"Mimina anyi sallako?".
Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh,
Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa.
"Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu'o'in Allah ya bashi lfy ko?".
Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa.
"Eh nayi mishi".
A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace.
"Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu'a, in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi.
Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy, kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar, ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu".
Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta.
Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi,
bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya.
"Yasha mgninshi ne?".
Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa.
"Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba,
Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba,
sai ya bishi,
Kullum sai Jalal yayi kuka".
Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido,
A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba.
Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka.
Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan munafurci da kukan gulma dana ha'inci da yaudara,
shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa.
Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa.
Ya sani tabbas su abun tausayawa ne, suna buƙatar kulawarshi fiye data kowa a duniya, to amman ya rasa meyasa yake jin kamar baya son kusancisa dasu.
Maimartaba kuwa, suna cikin sahun na forko bayan liman,
Sai da sauran malaman fada.
A cikin gida kuwa, jin sautin zazzaƙar miryarshi yana rere karatun al'ƙur'ani, ya ida fatiha, kana ya ɗaura, Arrahama,
daga bisani ya rufe da lakadja'akum, kafin ya tafi zuwa ruku'uh.
Haka nan Juwairiyya ta tsinci kanta da zubda wasu zafafan hawaye, masu ƙuna a rai, tabbas ta sani.
Kasan cewar Sheykh a masarautar nanne kaɗai yasa, suke a ciki.
Ta sani in badon daraja da al'farmarsa ba, da tun tuni, an tabbatar da sunan mijinta mahaukaci.
Hannu tasa ta share hawayenta cikin sanyi ta miƙe dan gabatar da sallan asuba, a zahiri tace.
"Allah ne gatanmu, kaine GARKUWAR mu, Sheykh in baka nan gidan kanyi mana duhu, ƙasar tanayi mana zafi."
Daga nan ta tada kabbara.
Ummi Jakadiyarsu kuwa,
Tana bayan gida, tana al'wala ta jiyo muryarshi, wani irin murmushi tayi tare da yin mgna a baiyane.
"Dan Halak kaƙi ambato, ɗa ɗaya tamkar dubu, maƙiyanka fadawanka, sunyi sake ɗan zaki ya girma, in sha Allah zaka dawo da farin cikin masarautarnan, sunyi sake, sun bar kari tun ran tubani,
Muhammad Jabeer bawan Allah".
Haka ta fito tana wasu irin kalamai masu wuyar fahimta.
A can sashin Hajia Mama kuwa,
Wata kekyawar budurwa, ce.
Konce kan gado gefen Mama, datake zaune bisa sallaya.
jiyo muryashine ya sasu saurin juyowa, suka kalli juna,
Cikin tsananin farin ciki da tarin shauƙi budurwar ta diro daga kan gadon gaban Mama ta zauna cikin zaƙuwa tace.
"Lah Mama, yaushe ya dawo! Muryar Sheykh Jabeer nake jifa! Mama ko dai dama yana nanne?".
Wani irin kallo Mama tayi mata cikin sanyi da murmushi a fuskarta tace.
"Batul shine, ya dawo!."
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe cikin tarin shauƙi tace.
"Yes Mama, farin cikina ya dawo, kamar yasan, nazo.
Alhamdulillah, Mama Allah yana sona, ki gani ina zuwa, na samu baya nan, naji baƙin ciki kamar in mutu jiya kafin inyi bacci, sai gashi Allah ya turo minshi cikin dare ɗaya."
Murmushi Mama tayi, tana mai jin mmkin yadda Batul ke masifar son Sheykh har take gaza ɓoyewa.
cikin haɗe fuska tace.
"To yanzu dai, sai ki tashi kiyi salla, tunda kinji muryar da kikafi so a duniya, kin sauƙo kan gadon, sau nawa ina tadake, sai kiyi miƙa ki kuma konciya".
Cikin jin dadi tace,
"Wayyo Mama baccinne bai isheniba Allah ko jiya kwana nai ina zulumi, sai 3:44 na asuba na samu bacci."
Murmushi Mama tayi kana ta miƙe ta kabbarta sallan.
Ita kuwa Batul, miƙewa tayi da sauri ta shige, bathroom tana cewa.
"Bari inyi wonka inyi salla, in shiga kitchin yau nida kaina zan mishi breakfast."
Tana faɗin haka ta shige ciki.
A masallaci kuwa, ana idar da salla kamar koda yaushe, da yawa basu fitaba saida sunata lazumi.
Yayinda Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da kuma Sarki Nuruddeen Bubayero, da Habibullah Nuruddeen Bubayero, suka jero, suka fito a jere, domin su kullum ana idar da sallan asuba, suke fitowa su koma cikin masarautar, inda kowa zai wuce Side ɗinsa,
Yayi karatun qur'ani da kuma, Dua Azkar, inda har sai rana ta fito, kana suke ɗan maida bacci, to kuma sudayin breakfast sai 11.
Suna isowa tsakiyar masallaci, Sheykh yaji an ruggumeshi ta baya, yasan mutun ɗaya ne rak zai mishi haka a cikin masallacin,
Ya Jafar ɗinsu.
Yana juyowa kuwa yaga shiɗin ne.
Ruggumeshi yayi gam-gam Jalal, kuwa ido ya zuba musu,
shi kuwa Sheykh hannu yasa shima ya ruggume ɗan uwan nashi.
Yayinda ya zubawa Jalal kwayar idanunshi, ya rame sosai, hancinsa ya ƙara fitowa, sai sajenshi daya ƙara yin lib, da uban gashin daya tara, yayi wani kafurin aski.
Ramar da Jalal yayi ta daki zuciyarsa sosai baya son ganin ƙannen nashi cikin halin matsala,
a hankali ya janye kwayar idanunshi ya maidasu kan Jamil da Affan dake gefen damanshi,
Calikan ƙanenneshi kenan ba,
sheƙiyancinsu ɗaya, baki suka haɗa wurin cewa.
"Sabahul Noor Al'Sheykh".
A hankali ya ɗan motsa laɓɓansa, yana mai kallonsu yace.
"Sabahul khair ya Uktih".
murmushi sukayi, suna mai jin son ɗan uwan nasu,
Abbs da Maimartaba kuwa, kai suka ɗan jinjina kana sukayi gaba,
Ganin hakane suma suka bisu, a baya,
shi kuwa Sheykh hannu yasa ya shafa kan Imran da yanzu ya iso gabanshi cikin sanyi yace.
"Hamma Jabeer barka da safiya".
jin yana shafa kanshine ya sashi lumshe ido, inama ace yadda Hammanshi ke nuna mishi so haka zai shirya da Mom ɗin shi, yana masifar son ɗan uwanshi baya jin daɗin yadda yake ganin wata iriyar mu'amala tsakanin Mom da yayunshi.
Ganin Sheykh yaja hannun Ya Jafar sun tafine yasashi bin bayansu.
Ƙofar dake cikin masallacin wacce zata ɓulla cikin masarautarsu sukabi.
Suna shiga, kowa yayi sashinsa sabida sun sani ko sunbi Sheykh yanzu ba lokacin mgna bane, karatu zaije yayi.
Shi kuwa Sheykh yana riƙe da hannun Ya Jafar ɗinsa suka shiga side ɗinsa,
inda ya samu hadimai masu tsaron ƙofar, suna tsaye.
Suna shiga, tamtsetsen falon nashi kai tsaye ya nufi wannan babbar kusurwar da zata sadashi da.
Big part ɗin shi,
Suna shiga suka ɓulla cikin wani mashahurin, falo, wanda yaketa tashin ƙamshi mai masifar sanyi da daɗin shaƙa,
a hankali ya zauna bisa kujerar 3 str kana yaja hannun Ya Jafar ɗin suka zauna, tare.
A hankali ya juyo kanshi ya zuwa ɗan uwanshi idonu,
Karatu yakeyi kamar koda yaushe, yanayi cikin tsantsar lugga da tajwid, kana ga kushu'i,
Suratul yaseen yake karanta,
bisa alamu kenan ya kusa yayi sauƙa, domin step by step yake bin surorin, in yayi sauƙa sai ya sako daga sama, baya mancewa, kuma baya birkitashi,
Wannan rahamar da Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina, amman banda gefen addininshi.
Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan idanunshi,
sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za'ayi ya sama mushi farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi.
Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi,
Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon suratul. Noor ya farayin ƙasa.
Saida sukayi awa ɗaya cur kana,
Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu'o'in cikin harshen dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga.
Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam.
Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi.
Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana,
ya miƙa tare da jawo hannunshi,
yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne,
Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu.
A babban falon suka samu Juwairiyya.
Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da hawaye tace.
"Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar".
Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta,
Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi,
cikin murmushi ta nitsuwa yace.
"Mimina anyi sallako?".
Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh,
Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa.
"Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu'o'in Allah ya bashi lfy ko?".
Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa.
"Eh nayi mishi".
A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace.
"Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu'a, in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi.
Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy, kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar, ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu".
Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta.
Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi,
bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya.
"Yasha mgninshi ne?".
Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa.
"Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba,
Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba,
sai ya bishi,
Kullum sai Jalal yayi kuka".
Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido,
A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba.
Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka.
Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan munafurci da kukan gulma dana ha'inci da yaudara,
shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa.
Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa.