← Book details Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 142

Sashe 47

Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da sauri suka juyo suna. Kallon gungun wasu matasa wanda suka kece da dariyar ƙeta cikin hausarsu ta ƙabilu suke cewa.
"To ku ɗan naku ko yadda ake gudanar da gasar ma bai sani bane? Ya zaiyi zaton da wannan shigar tasa za'a dakeshi, to ai ko bulali dubu za'ayi mishi ba jinsu zaiba,
Kai Ɗan kazagi, ka gaya mishi nan ba cikin masallaci bane.
Nan wurin shaɗi ne".
Jiyo hakane ya sa ran dukkan musulman wurin ɓaci.
Sabida sun fahimci kafuraine masuyin wannan zancen.
Galadima kuwa da Ɗan buram sun ɗauka abin wasane, a zatonsu zasu shawo kan Jabeer a sauƙaƙe, amman ina ya tiƙe yace babu wani zinɗiƙin ƙaton da zai sashi ya yaye suturar dake jikinshi.
Dariyar da su Arɗo da sauran mutane keyine ya hautsuna lissafin Lamiɗo.
Cikin harzuƙa ya taso, har kamar zaiyi tuntuɓe ya nufi inda su. Waziri, Wambai, Ɗan buram, Ɗurɓi, Da Galadiman, cikin tashin hankalin alamun akwai wata babbar manufa da Galadima ke son cimmawa cikin lamarin ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa.
"Haba Jabeer kai wanne irin mutun ne mai kafiya da taurin kan tsiya, yaya muna binka kana zillawa, muna haɗaka da Allah da Manzonsa amma kana tunzuramu, wallahi da yau sai anyi gasar nan!".
Cikin tsananin ɓacin rai yace.
"In tsaya a tozarta ni kuke so.
Ayimin tijara kukeso, da wanne idon zan kalli al'ummar Annabi da jiki tsirara".
Cikin kufula Waziri yace.
"Waya ce maka tsirarane?".
Murya a sama yace.
"Tsirara ne mana! Tunda sunce wai dagani sai Boxes zan tsaya, ka kuwa san ko Mahaifiyata data haifeni tun ina shekaru shida a duniya bana tsayuwa a gabanta dagani sai ɗan kamfai, tunda nake Mahaifiyata, Mahaifina, Yayuna, Uncles, na Aunty's na, babu wanda ya taɓa dukana, sabida ban cutar dasu da komaiba bare su hukuntani da duka haka kurum rana tsaka kunce in tsaya a dakeni, na yarda, sannan yanzu kuma ace nai tsirara, kai bafa wanda zan yiwa mubaya'a akan hakan..!."
Tas! Yaji sauƙan wani irin gigitaccen mari sai dai babu wanda ya ga sauƙan marin sabida suna tsakiyarsu Waziri ne, kuma sauran mutanen garin duk kowa bayan su Waziri suke iya gani.
A harzuƙe ya ɗago kanshi,
Lamiɗo ne ya gani tsaye a gabanshi.
Jan hannunshi yayi da iya ƙarfin shi na tsufa.
Tsakiyar filin suka koma, cikin fushi yace.
"Galadima zoka cire mishi kayan."
Da sauri Galadima ya motso gabanshi.

Su Waziri kuwa duk suka koma cikin Rufarsu masauƙinsu.
Wani irin tsuma da karkarwa jikin Jabeer ya farayi, tun sanda yaji sauƙan marin.
A take idanunshi nan su kaɗa sunyi wani irin masifeffen juyewa sunyi jazir,
Hatta lips ɗinshi karkarwa sukeyi. Wani irin tarin baƙin cikin da bai taɓa jin irinsa ba a duniya ne, ya lulluɓe masa zuciya.
Koda randa Ya Jafar ɗinsu ya zauce, baiji makamancin wannan ɓakin cikinba.
Ji yakeyi Tamkar ya haɗiyi zuciyarshi ya mace ya bar duniyar kowama ya huta,
Rumtse idonshi yayi da azaban ƙarfi lokacin da yaji, Galadima ya gama komce masaƙalan al'kyabbar jikinshi,
kana ya buɗe shi, yayi ƙasa dashi, har saida ya cire hannayenshi a ciki.
Haroon dake gefensu ya miƙa wa al'kyabbar, kana a hankali ya kuma matsowa gareshi, hannunshi yasa saman kanshi ya ɗage zagayen baƙin abin da yake kan Hiramin, kana yasa hannunshi ya janye hiramin.
Kekyawar fuskarshi ta fito ras, tattausan baƙin gashin kansa dake kwance lib-lib ya baiyana, wanda hakan yasa kaso 70 cikin ɗari na dubban mutanen dake wurin suka zuba ƙwayar idanunsu kanshi, da yawa tasbihi da ta'ajjudin irin kyau da haibar da Allah ma ɗauka kin sarki yayi mishi sukeyi.

Jalal kuwa ji yake tamkar ya rinƙa kurma ihu, Allah yasani baya son abinda zai cutar musu da Hammansun,
Jamil kuwa tuni hawaye yake zubdawa,
Ya Hashim, Imran, Sulaiman, kuwa dukkansu sunkuyar da kawunansu sukayi ƙasa.

Laminu kuwa wani irin masifeffen jin daɗi yakeyi, hakan yasa ya ƙara kutsowa cikin filin hakan ya bashi daman yin viewing da kyau.

Shi kuwa Jabeer tafarfasar da zuciyarshi keyi yayi masifar tsananta lokacin da yaji, Galadima ya zare mishi tattausar rigar shaddar dake jikinshi.
jin yasa hannunshi yana shirin zare mishi singlet ɗin jinshi ne yasashi, ƙara ambaton sunan Allah da sauri-sauri, sabida ji yakeyi tamkar ya buɗe ido ya shaƙo moƙoshin Galadima sai ya sumar dashi, tabbas da ace al'ƙalin gasarne ke cire mishi kaya da tuni ya daku.
Cak ɓari da karkarwan da jikinshi keyi ya bari,
Lokacin da yaji Galadima yasa hannunshi ya kwance zariyar dogon wondon jikinsa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil.
Allahumma ajjirni fi musubati!!.."
Ƙasa idawa yayi, jin an saɓule wondon jikinsa yayi ƙasa,
da ƙarfi ya buɗe kwayar idanunshi da suka koma tamkar garwashin wuta. Tafarfasar da jininshi keyi shine abu mafi tartsatsi a rayuwarsa.
Hannunshi Galadima ya jawo da ƙarfi wanda dole yasa ya ɗaga sawunshi ya tsallake wondon ya zama babu komai a jikinshi dagashi sai Boxes wanda Allah yayi mai ɗan tsawone yazo har kusa da guiwarsa saidai a matse yake.

A tsakiyar filin ya tsaidashi kana ya juya ya koma ya zauna kusa da Lamiɗo.
Jalal ne ya sunkuya ya ɗauki wondon da sauri ya miƙa wa, Haroon.

Shi kam Jabeer zuwa yanzu,
Ya sani a duniya ba'a taɓa yi mishi tozarci sama da wannan ba, ji yakeyi a duk faɗin duniya babu garin daya tsana sama da garin Rugar Bani, bai taɓa jin haushi da tsanar wani abu a duniya ba sama da mutanen garin Bani, ji yakeyi ya tsanesu gaba ɗayansu, ya tsani komai nasu, baya so da fata da sha'awan komai nasu.
ƙasar garin ma da yake tsaye a kai ya zuba mata ido ji yake tamkar ya ƙonata ta sauya launi daga farin yashi zuwa baƙin yashi.

A tsakiyar taron kuwa, da sauri al'ƙalin gasar ya jawo hannun Ba'ana da ya zaro wata asirtaciyar bulalar tsamiya, daga cikin randar bulalinshi
sai wani motsi bulalar keyi tamkar tanada rai.

Bayan Jabeer al'ƙalin gasar ya kawoshi. Yana sake hannunshi masu busar al'gaita da sarewa suka farayi da ƙarfin su.

Lokaci ɗaya kuma ranar data take buɗe tarwal ta lumshe.
Mutanen kuwa sai tasowa da ife-ife akeyi. Kallo kuma kab ya dawo kan farar kekyawar fatarshi da kekyawan baƙin tattausan gargasa yayi mishi ƙawanya, iya kyan fatarshi kaɗai ya ishi ɗan adam kallo.
Da ƙarfi Jabeer ya taune lips ɗinshi, yana maiji tamkar zai hudasu sai ambaton sunan Allah yakeyi, babbar yatsar ƙafarshi ta dama yasa yana caka ƙasar garin, kana yatsunshi na hannun kuwa yasa babban yana zagaye kan ƴar manuniyarshi.
A yadda yake jin zafi da ƙuna da baƙin ciki a cikin zuciyarshi ya tabbatar babu wani abu da za'ayi mishi a yanzu yaji zafinsa fiye dashi, to me za'ayi mishi mai zafi sama da tsiraiceshi da akayi.

Ba'ana kuwa cikin dariyar mugunta da sautin amo mara daɗin ji, ya taƙar-kara ya ɗago bulaliyar asirin nan, da iya ƙarfin shi ya zabga mishi ita a tattausar fatar tsakiyar bayanshi.
Da ƙarfi su Jalal kab suka rumtse idanunsu.
Lamiɗo kuwa wani irin kallo yayiwa Jabeer da yayi.
Wani ir.....!

Biya darinki uku kacal domin jin wannan labari har ƙarshe.
Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina.

Wannan shafin nakune gaba ɗaya waɗanda suka karanta FREE PAGE🤝🏻😘🥰

By
*GARKUWAR FULANI*📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘

*GARKUWA*

PAGE 10

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘

LITTAFIN GARKUWA NA KUƊINE, TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta number 09097853276 domin samun cikekken labarin, ko kiyi min transfer ɗin 1k ɗan samun SP GROUP ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276

FREE PAGE

Cikin tashin hankali tace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ya Ba'ana me wannan, abu kamar macizai". Da sauri ya meda ya rufe kana ya miƙe cikin yin ƙasa da murya yace.
"Kinga ni kada ki tayarmin da hankali kinsan bana son ganinki cikin tashin hankali, in sha Allah nine da nasara ko dai bakya so nane".
Da sauri ta girgiza kanta tare dasa tafin hannunta ta rufe bakinta.
Ganin haka ya kwashi abinshi ya tafi.

Ita kuwa koda ta shiga gida, gefen Inna ta zauna tare da cewa.
"Inna ku cewa Bappa ya cewa Arɗo ya hana gasar nan, kada a cutar da Ya Salmanu".
Cikin sanyin jikin da duk kwanan haka inna ta zama, a hankali tace.
"Uhumm ba komai Shatu in sha Allah duk abinda zai faru da sanin Allah.
Yanzu ke yaushe nema zaki koma hutunmu?".
Kanta ta gyaɗa a hankali tace.
"Rana ita yau zan koma kimga saura mako ɗaya kenan".
Ummey ce dake gefe ta ɗanyi ajiyan zuciya gami da cewa.
"Alhamdulillah ni in kin komama hankalinmu zaifi konci, domin muddin kinanen sai Ba'ana yayi ta kalato fitina".

Shiru sukayi baki ɗayansu, jin an fara kiran sallane tasa, duk kowa yayi al'wala haraman salla.

A daren ranar kuwa Ya Salmanu da abokinshi Sale suka zo, wurinta, nan take ce musu ita kam bata son wannan gasar da za'ayi kuma tunda an kafe sai anyi sam ita bazata jeba.
Haka dai sukayi ta hira daga bisani suka tafi.

Washe gari ranar Monday kuwa, tun da sanyin asuba aketa gangamin.
Haɗuwa a filin da za'ayi shaɗi.
Mutanen sun cika maƙil dan anfi yawan yin gasar da safe, sabida da rana duk makiyaya sun tafi kiwo manoma sun tafi daji.
Tuni matasan Fulani na rugogin nesa da Bani ma sun zo.
Chapter 47 · 0% Book details