Sashe 76
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ƙalla awa ɗaya yayi kafin ya tashi kan sallayan
Gaban gadonshin ya dawo ya zauna bisa tattausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a wurin mai kalar Sky blue and white.
Sosai yaji daɗin jikinshi, sai dai har yanzu yana jin raɗaɗin bulalin.
Tea kawai ya iya sha.
Kana a hankali yace wa Haroon.
"Canza min beshit ɗin nan da blanket ɗin."
Hararanshi Haroon yayi tare da cewa.
"Zan koma, yaseen na gaji da mulkinka da sarautar da kake ji dashi. Ji yadda ka medani tamkar wani bawanka ko hadimin gidanku, kuma duk abinda zanyi maka sai ka cini gyara, mutum ba'a iya mishi sai masifa kake min kamar dai nine nace a zaneka".
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye tare da gimtse dariyarshi, sabida ganin kallon da Jabeer ke mishi.
A haka dai ya sauya komai na gadon kafin suka, hau suka konta.
Tsaki Jabeer yaja tare da cewa.
"Ni dama ka tafi wancan ɗakin sabida zancen gsky kasan ni bana son takura.
Sabida zaka hanani sakewa yadda nakeso".
Cikin gajiya Haroon yace.
"Allah babu inda zan fita inje".
Da haka dai Haroon yayi bacci.
Shi kuwa Sheykh Jabeer karatu yayi tayi har biyu da rabi tayi kana, ya buɗe tafin hannunshi yayi addu'o'in bacci.
Falaƙi 3 Nasi 3 ƙulhuwa 3 Ayatulkursi'u 1 kana amarrasulu 1 tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikinshi.
Kana ya kuma yi. Haka ya tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikin Haroon Wanda tuni ya ɓingire,
Shi kuwa Jabeer wannan al'adar rayuwarsa ce daya saba, kan Jalal da Jamil sabida suma haka suke bingirewa, shikeyi tofi ya shafa musu.
Washe gari Lamiɗo baiyi zaton Jabeer zai samu fitowa masallaci ba,
Shiyasa limamin dake jansu salla in baya nan ya fito ya jasu salla,
yayinda Jabeer ke cikin sahun forko.
Wannan yasa mutane sukayi zaton ciwon ne yayi tsamari bai samu ya fitoba.
Ana idar da salla kuma ya fito yayi cikin gida sabida.
Fushi yakeyi da wannan tsohon ya sani in ya tsaya kuma zai dameshi da wata falsafarshi da zaici karo da addini.
Ƙarfe takwas dai-dai. Barrister Kamal da Ya Jafar, da kuma Baba Basiru ne zaune dashi a falon shi.
Suna zaune anan Jalal ya shigo cikin yanayin damuwa yace.
"Hamma Jabeer, Umma na falo tazo dubaka da jiki."
Cikin yamutsa fuska yace.
"Wacece hakan?".
Cikin fusata Baba Basiru yace.
"Ashe uwarka ma bazaka santa ba, ina dai baka san wacece Umma ba".
Wani irin kallon ido cikin ido Sheykh yayiwa Baba Basiru,
sai kuma ya ɗora ƙafarshi ɗaya kan ɗaya, cikin ƙasaita ya kalli Jalal tare da cewa.
"Mene Umman!?". Ya sani sarari Gimbiya Saudatu ake cewa Ummu .
Gyara tsayuwa Jalal yayi tare da gyara zaman belt ɗin ƙugunshi yace.
"Matar tsohon Galadima marigayi, Baba Muhammad ce Ummar Gimbiya Saudatu."
Da sauri Baba Basiru yayiwa Jalal daƙuwa tare da cewa.
"Kan uwarka hegen yaro ɗan shila".
Shi kuwa Jabeer ƙafarshi ya fara kaɗawa.
Barrister Kamal kuwa ido ya zubawa Fuskarta Jabeer da Jalal. Cikin sanyi da tausasan laffuza yace.
"Jabeer tashi muje ka gaisa da ita tunda ta taso tazo har nan dubaka da jiki".
Kanshi ya gyaɗawa Barrister Kamal ɗin wanda suke cewa Baba Kamal wanda yake mahaifin Sulaiman, sa'an Jabeer.
Da hannu yayiwa Jalal alamun yaje yace, yana zuwa.
Shi kam Baba Basiru bayan Jalal yabi.
A babban falon suka zauna shida Gimbiya Saudatu da Laminu da kuma Baba Nasiru.
Jalal, Jamil, Haroon, Jafar, kuwa duk suna can Dinning area kan dinning table sunayin breakfast.
A jere suka fito falon shida Barrister Kamal.
Suna isowa tsakiyar falon.
Cikin wani irin taku mai cike da ƙasaita da rashin tsoro.
Ya kalli Gimbiya Saudatu dake zaune bisa kujerar zamanshi.
Yatsunshi biyu ya haɗa ya kaɗa mata tare da mata alamun tashi min kan kujera.
Cikin wani irin kallo mai nuna tsantsar fushi da tsana da zazzafan ƙiyayya ta fara mgna cikin ɗaga sauti tace.
"Hegen yaro mai idanun mujiya, Ni kakeyiwa wannan iskancin dan kan uwar..!".
Kasa ƙarisa zagin da tayi nufin yi tayi jin yana cewa.
"Kan uwarki ko? Ki ƙara sa mana kikaga ikon wanda ya hana mata gemu ya baiwa maza!
Maza tashi min kan kujerar zama tunda ba wancan jiɓeɓɓen tsohon akun bane seyota".
Wani irin zabura Baba Nasiru yayi tare da ɗaga hannu zai kifeshi da mari, kamar a mafarki yaji an riƙe mishi hannunshi da sauri ya juyo.
Ido ya zaro cike da mamakin ganin wanda ya riƙe mishi hannunshi cikin tafasar zuciya da ƙuna yace.
"J....."
By
*GARKUWAR FULANI*
Cikin wani zare ido na masifa yace.
"Jalal ni ka riƙe wa hannu".
Shima idon ya zare tare da cewa.
"Ba iya rikeshi kaɗai zanyi ba, in dai zai taɓa lfyar ɗan uwana a gaban idona, datseshi zanyi gaba ɗaya in wurgar". Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da yarfa hannunshi.
Wani irin asirtaccen murmushi Barrister Kamal, yayi tare da kallon ɗan shi Sulaiman hannunshi ya dunƙule ya jinjina wa Sulaiman ɗin.
Kana suka koma suka zauna bisa kujera.
Shi kuwa Jabeer hannun ya nunawa Gimbiya Saudatu alamun ta tashi.
Mirtsitsi tayi tare da gyara zamanta.
Wani irin firgitacen tsawan da Jalal ya danna matane yasa, ta miƙe tsaye ba tare datasan ta miƙa ɗin ba.
Cikin ƙasaita Jabeer ya baza tattausar al'kyabbar jikinshi,
Kana ya matso ya zauna bisa kujerar ƙafarshi ɗaya ya ɗora bisa ɗaya.
Gyara hiramin kanshi yayi tare dayin gyaran murya kana ya kalli ƙannen mahaifin nashi kauda kanshi yayi ganin yadda suke wani irin cika da batse sun cika sunyi tamtsan da fushi.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu zama tayi a kujerar dake kallon tashi
kujerar.
Itama ɗaura ƙafa ɗaya tayi kan ɗaya.
Cikin iya tijara ta watso sabbin jaridu gabanshi.
Jaridar bankaɗa da kuma kamfanin jaridar hantsi wato leƙa gidan kuwa.
Murmushin muguntan tayi tare da cewa.
"Ga sakamakon sa insa da kayi dani jiya, na yau kuma shima yana nan tafe.
Nayi maka murna darajar labarin ya kai matsayin da shine a shafin forko na jaridun".
Da sauri Jalal ya sunkuyo yasa hannunshi ya ɗauki jaridar banƙaɗa.
Jiki na tsuma ya ɗago ya kalli Gimbiya Saudatu cikin tashin hankali yace.
"Wannan ƙarya ne, da babu jahilin da zai yarda dashi, wlh bazaku taɓa cin nasara ba."
Hankali a tashe ya miƙawa Haroon jaridar tare da cewa.
"Ya Haroon gani zancen banzan da aka rubuta kan hotunan Hamma."
Da sauri Haroon dake sauƙowa kan stpes ɗin sauƙowa falon daga dinning area,
ya ƙaraso. Hannuyasa ya amshi jaridar.
Wani irin azabebben zufane ya fara keto mishin ganin abinda aka rubuta a jikin jaridar.
Jin jikinshi na rawane ya sashi zama kusa da Sulaiman.
Ummi kuwa dake tsaye a dinning area tana haɗawa.
Jafar abin da zaici, gaba ɗaya ido ta zubo musu cikin taraddadin me aka rubuta.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu wata iriyar shaƙiyiyar dariya tayi tare da cewa.
"Ya haka dai ƴan kanzagi, ku bawa shi uban gidan naku, jaridar yage me aka rubuta, daga nan sai inga bakinshi da baya mutuwa da bada amsa ko zai iya cewa wani abu."
Baba Nasiru da Baba Basiru, ma fuska cike da farin ciki suka zauna.
Laminu kuwa miƙewa tsaye yayi tsakiyar faffaɗan falon cikin ɗaga sauti yace.
"To tunda bazaka iya bashi ba, bani ni in karanta mishi."
Yana ƙarishe mgnar yasa hannunshi ya amshi jaridar.
Cikin ɗaga sauti ya fara karanta rubutun dake rubuce a ƙasan hoton da gefe da gefenshi.
"Abun kunya, ya baiyana jikan sarki Nuruddeen Bubayero ɗaga Habibullah,
Yayiwa ɗiyar Fulani fyaɗen da yasa.
Hanun Sarki Lamiɗo ya kama hannun Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero wanda yake limamin masalacin ƙofar sarki ya miƙa shi ga hukumar addini musulunci.
Gashi anayi mishi bulalin haddi kamar dai yadda Musulunci ya wajabta.
Wani irin murmushi Jabeer yayi, hannunshi yasa ya shafa tattausan gemunshi.
Cikin rashin karaya ya kalli Haroon cikin nitsuwa yace.
"Ɗan wannan abun ne kuke zaton zai kashe wannan bakin nawa da yake rayuwa da ambaton Allah!?
Shin ko kun mance tsawon shekaru da dama ana fataucin rufe bakin Ya Jafar, shima har yau baku samu nasarar hanashi ambaton Allah ba,
Duk sharrinku ya zame mushi al'khairi, tunda baya wani motsi ba tare daya kira sunan Allah ba, ikirarin ku na ya zauce, ya tabbata kune zautattun".
Sai kuma ya ɗan kalli Gimbiya Saudatu, murmusawa yayi tare da cewa.
"Baki nafa bazai mutuba sai in nufashina ya bar jikina, batun shiga ɗakin sirri kuma, nifa wannan abin da kuketa haƙilo a kai ba wani baƙon abun bane a wurina.
sarauta a cikin jin jikina yake."
Sai ya kuma juyo ya kalli Haroon da jikinsa yayi la'asar da lamarin su, miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Haroon wai ɗan wannan makircin nasune ya kashema jiki.
To kontar da hankalinka. Ni nan Muhammad Jabeer ƙi gudune sa gudu.
Tun kan suyi tunanin yin abu a kaina na nazarci abun."
Juyowa yayi ya kalli Baba Nasiru cikin tsareshi da ido yace.
"Kaje duk inda ake saida jarudu ka bada farashin one million akan ko wanne jarida kaga in za'a fito maka da wannan jaridar, in bada wannan ƙwaya ɗayar kaga dai itama kuma gata a gabana."
Cikin tarin mamaki suka zuba mishi ido.
Shi kuwa gaban Laminu ya isa cikin isa ya miƙa mishi hannunshi tare da cewa.
"Bani shi nan".
Cikin tsananin tsoro da firgici ƙarara. Jiki na rawa Laminu ya miƙa mishi. Sabida kwarjin Jabeer ya mishi nauyi a idonshi ya kuma san artabu dashi ba daɗi.
Gaban gadonshin ya dawo ya zauna bisa tattausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a wurin mai kalar Sky blue and white.
Sosai yaji daɗin jikinshi, sai dai har yanzu yana jin raɗaɗin bulalin.
Tea kawai ya iya sha.
Kana a hankali yace wa Haroon.
"Canza min beshit ɗin nan da blanket ɗin."
Hararanshi Haroon yayi tare da cewa.
"Zan koma, yaseen na gaji da mulkinka da sarautar da kake ji dashi. Ji yadda ka medani tamkar wani bawanka ko hadimin gidanku, kuma duk abinda zanyi maka sai ka cini gyara, mutum ba'a iya mishi sai masifa kake min kamar dai nine nace a zaneka".
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye tare da gimtse dariyarshi, sabida ganin kallon da Jabeer ke mishi.
A haka dai ya sauya komai na gadon kafin suka, hau suka konta.
Tsaki Jabeer yaja tare da cewa.
"Ni dama ka tafi wancan ɗakin sabida zancen gsky kasan ni bana son takura.
Sabida zaka hanani sakewa yadda nakeso".
Cikin gajiya Haroon yace.
"Allah babu inda zan fita inje".
Da haka dai Haroon yayi bacci.
Shi kuwa Sheykh Jabeer karatu yayi tayi har biyu da rabi tayi kana, ya buɗe tafin hannunshi yayi addu'o'in bacci.
Falaƙi 3 Nasi 3 ƙulhuwa 3 Ayatulkursi'u 1 kana amarrasulu 1 tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikinshi.
Kana ya kuma yi. Haka ya tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikin Haroon Wanda tuni ya ɓingire,
Shi kuwa Jabeer wannan al'adar rayuwarsa ce daya saba, kan Jalal da Jamil sabida suma haka suke bingirewa, shikeyi tofi ya shafa musu.
Washe gari Lamiɗo baiyi zaton Jabeer zai samu fitowa masallaci ba,
Shiyasa limamin dake jansu salla in baya nan ya fito ya jasu salla,
yayinda Jabeer ke cikin sahun forko.
Wannan yasa mutane sukayi zaton ciwon ne yayi tsamari bai samu ya fitoba.
Ana idar da salla kuma ya fito yayi cikin gida sabida.
Fushi yakeyi da wannan tsohon ya sani in ya tsaya kuma zai dameshi da wata falsafarshi da zaici karo da addini.
Ƙarfe takwas dai-dai. Barrister Kamal da Ya Jafar, da kuma Baba Basiru ne zaune dashi a falon shi.
Suna zaune anan Jalal ya shigo cikin yanayin damuwa yace.
"Hamma Jabeer, Umma na falo tazo dubaka da jiki."
Cikin yamutsa fuska yace.
"Wacece hakan?".
Cikin fusata Baba Basiru yace.
"Ashe uwarka ma bazaka santa ba, ina dai baka san wacece Umma ba".
Wani irin kallon ido cikin ido Sheykh yayiwa Baba Basiru,
sai kuma ya ɗora ƙafarshi ɗaya kan ɗaya, cikin ƙasaita ya kalli Jalal tare da cewa.
"Mene Umman!?". Ya sani sarari Gimbiya Saudatu ake cewa Ummu .
Gyara tsayuwa Jalal yayi tare da gyara zaman belt ɗin ƙugunshi yace.
"Matar tsohon Galadima marigayi, Baba Muhammad ce Ummar Gimbiya Saudatu."
Da sauri Baba Basiru yayiwa Jalal daƙuwa tare da cewa.
"Kan uwarka hegen yaro ɗan shila".
Shi kuwa Jabeer ƙafarshi ya fara kaɗawa.
Barrister Kamal kuwa ido ya zubawa Fuskarta Jabeer da Jalal. Cikin sanyi da tausasan laffuza yace.
"Jabeer tashi muje ka gaisa da ita tunda ta taso tazo har nan dubaka da jiki".
Kanshi ya gyaɗawa Barrister Kamal ɗin wanda suke cewa Baba Kamal wanda yake mahaifin Sulaiman, sa'an Jabeer.
Da hannu yayiwa Jalal alamun yaje yace, yana zuwa.
Shi kam Baba Basiru bayan Jalal yabi.
A babban falon suka zauna shida Gimbiya Saudatu da Laminu da kuma Baba Nasiru.
Jalal, Jamil, Haroon, Jafar, kuwa duk suna can Dinning area kan dinning table sunayin breakfast.
A jere suka fito falon shida Barrister Kamal.
Suna isowa tsakiyar falon.
Cikin wani irin taku mai cike da ƙasaita da rashin tsoro.
Ya kalli Gimbiya Saudatu dake zaune bisa kujerar zamanshi.
Yatsunshi biyu ya haɗa ya kaɗa mata tare da mata alamun tashi min kan kujera.
Cikin wani irin kallo mai nuna tsantsar fushi da tsana da zazzafan ƙiyayya ta fara mgna cikin ɗaga sauti tace.
"Hegen yaro mai idanun mujiya, Ni kakeyiwa wannan iskancin dan kan uwar..!".
Kasa ƙarisa zagin da tayi nufin yi tayi jin yana cewa.
"Kan uwarki ko? Ki ƙara sa mana kikaga ikon wanda ya hana mata gemu ya baiwa maza!
Maza tashi min kan kujerar zama tunda ba wancan jiɓeɓɓen tsohon akun bane seyota".
Wani irin zabura Baba Nasiru yayi tare da ɗaga hannu zai kifeshi da mari, kamar a mafarki yaji an riƙe mishi hannunshi da sauri ya juyo.
Ido ya zaro cike da mamakin ganin wanda ya riƙe mishi hannunshi cikin tafasar zuciya da ƙuna yace.
"J....."
By
*GARKUWAR FULANI*
Cikin wani zare ido na masifa yace.
"Jalal ni ka riƙe wa hannu".
Shima idon ya zare tare da cewa.
"Ba iya rikeshi kaɗai zanyi ba, in dai zai taɓa lfyar ɗan uwana a gaban idona, datseshi zanyi gaba ɗaya in wurgar". Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da yarfa hannunshi.
Wani irin asirtaccen murmushi Barrister Kamal, yayi tare da kallon ɗan shi Sulaiman hannunshi ya dunƙule ya jinjina wa Sulaiman ɗin.
Kana suka koma suka zauna bisa kujera.
Shi kuwa Jabeer hannun ya nunawa Gimbiya Saudatu alamun ta tashi.
Mirtsitsi tayi tare da gyara zamanta.
Wani irin firgitacen tsawan da Jalal ya danna matane yasa, ta miƙe tsaye ba tare datasan ta miƙa ɗin ba.
Cikin ƙasaita Jabeer ya baza tattausar al'kyabbar jikinshi,
Kana ya matso ya zauna bisa kujerar ƙafarshi ɗaya ya ɗora bisa ɗaya.
Gyara hiramin kanshi yayi tare dayin gyaran murya kana ya kalli ƙannen mahaifin nashi kauda kanshi yayi ganin yadda suke wani irin cika da batse sun cika sunyi tamtsan da fushi.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu zama tayi a kujerar dake kallon tashi
kujerar.
Itama ɗaura ƙafa ɗaya tayi kan ɗaya.
Cikin iya tijara ta watso sabbin jaridu gabanshi.
Jaridar bankaɗa da kuma kamfanin jaridar hantsi wato leƙa gidan kuwa.
Murmushin muguntan tayi tare da cewa.
"Ga sakamakon sa insa da kayi dani jiya, na yau kuma shima yana nan tafe.
Nayi maka murna darajar labarin ya kai matsayin da shine a shafin forko na jaridun".
Da sauri Jalal ya sunkuyo yasa hannunshi ya ɗauki jaridar banƙaɗa.
Jiki na tsuma ya ɗago ya kalli Gimbiya Saudatu cikin tashin hankali yace.
"Wannan ƙarya ne, da babu jahilin da zai yarda dashi, wlh bazaku taɓa cin nasara ba."
Hankali a tashe ya miƙawa Haroon jaridar tare da cewa.
"Ya Haroon gani zancen banzan da aka rubuta kan hotunan Hamma."
Da sauri Haroon dake sauƙowa kan stpes ɗin sauƙowa falon daga dinning area,
ya ƙaraso. Hannuyasa ya amshi jaridar.
Wani irin azabebben zufane ya fara keto mishin ganin abinda aka rubuta a jikin jaridar.
Jin jikinshi na rawane ya sashi zama kusa da Sulaiman.
Ummi kuwa dake tsaye a dinning area tana haɗawa.
Jafar abin da zaici, gaba ɗaya ido ta zubo musu cikin taraddadin me aka rubuta.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu wata iriyar shaƙiyiyar dariya tayi tare da cewa.
"Ya haka dai ƴan kanzagi, ku bawa shi uban gidan naku, jaridar yage me aka rubuta, daga nan sai inga bakinshi da baya mutuwa da bada amsa ko zai iya cewa wani abu."
Baba Nasiru da Baba Basiru, ma fuska cike da farin ciki suka zauna.
Laminu kuwa miƙewa tsaye yayi tsakiyar faffaɗan falon cikin ɗaga sauti yace.
"To tunda bazaka iya bashi ba, bani ni in karanta mishi."
Yana ƙarishe mgnar yasa hannunshi ya amshi jaridar.
Cikin ɗaga sauti ya fara karanta rubutun dake rubuce a ƙasan hoton da gefe da gefenshi.
"Abun kunya, ya baiyana jikan sarki Nuruddeen Bubayero ɗaga Habibullah,
Yayiwa ɗiyar Fulani fyaɗen da yasa.
Hanun Sarki Lamiɗo ya kama hannun Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero wanda yake limamin masalacin ƙofar sarki ya miƙa shi ga hukumar addini musulunci.
Gashi anayi mishi bulalin haddi kamar dai yadda Musulunci ya wajabta.
Wani irin murmushi Jabeer yayi, hannunshi yasa ya shafa tattausan gemunshi.
Cikin rashin karaya ya kalli Haroon cikin nitsuwa yace.
"Ɗan wannan abun ne kuke zaton zai kashe wannan bakin nawa da yake rayuwa da ambaton Allah!?
Shin ko kun mance tsawon shekaru da dama ana fataucin rufe bakin Ya Jafar, shima har yau baku samu nasarar hanashi ambaton Allah ba,
Duk sharrinku ya zame mushi al'khairi, tunda baya wani motsi ba tare daya kira sunan Allah ba, ikirarin ku na ya zauce, ya tabbata kune zautattun".
Sai kuma ya ɗan kalli Gimbiya Saudatu, murmusawa yayi tare da cewa.
"Baki nafa bazai mutuba sai in nufashina ya bar jikina, batun shiga ɗakin sirri kuma, nifa wannan abin da kuketa haƙilo a kai ba wani baƙon abun bane a wurina.
sarauta a cikin jin jikina yake."
Sai ya kuma juyo ya kalli Haroon da jikinsa yayi la'asar da lamarin su, miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Haroon wai ɗan wannan makircin nasune ya kashema jiki.
To kontar da hankalinka. Ni nan Muhammad Jabeer ƙi gudune sa gudu.
Tun kan suyi tunanin yin abu a kaina na nazarci abun."
Juyowa yayi ya kalli Baba Nasiru cikin tsareshi da ido yace.
"Kaje duk inda ake saida jarudu ka bada farashin one million akan ko wanne jarida kaga in za'a fito maka da wannan jaridar, in bada wannan ƙwaya ɗayar kaga dai itama kuma gata a gabana."
Cikin tarin mamaki suka zuba mishi ido.
Shi kuwa gaban Laminu ya isa cikin isa ya miƙa mishi hannunshi tare da cewa.
"Bani shi nan".
Cikin tsananin tsoro da firgici ƙarara. Jiki na rawa Laminu ya miƙa mishi. Sabida kwarjin Jabeer ya mishi nauyi a idonshi ya kuma san artabu dashi ba daɗi.