Sashe 33
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A ƙalla yayi sawon daƙiƙu ashirin a bathroom ɗin kafin, ya fito,
yana ɗaure da wani babban towel mai ɗan karen kyau da taushi bayan ya matse wancan ya shanya.
Yana saƙo ƙafarshi cikin bedroom ɗin ya...!
Solo-salo-salon GARKUWA na dabanne!
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 13
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘
FREE PAGE
Littafin GARKUWA na kuɗine, Special Group 1k Normal 300, in kina buƙatar karanta lbrin GARKUWA turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276. Gareku mutanen Special Group turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.
*Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki, in kin san zaki sayi littafinane dan ki fitar dashi, na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki saya bana son kuɗinki, ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina. Dan Allah nace badon niba.*
Yaji anata bubbuga mishi ƙofar ɗakin,
bai kulaba, yazo a zauna bisa kujerar dreesing mirror, a hankali yake tsane ruwan jikinshi, bayan ya gama ɗan tsane ruwanne ya busar da tattausan sumar kanshi, ta hanyar na'urar busar da gashi.
Mai ya ɗan shafa, kana ya gyara gashin da kyau, sannan ya miƙe yaje gaban.
Drower'n, a nitse ya buɗe, wasu datsatstsun kaya riga da wondo na yadin Lamud, yadin Sky blue ne mai masifar kyau. Sai kuma ya zaro wata farar al'kyabbar fara ƙal. Da farin hirami.
Rufe wannan gefen yayi, kana ya buɗe ɗaya gefen.
Ƙananan kayan ne a ciki kamarsu Jallabiya da boxes vest dasu zagayen baƙin abin da yake ɗaurawa kam hiraminshi.
Suma duk mafi akasari su fararene.
A bakin gadon ya ajiyesu.
Kana ya fara kimtsawa.
Bayan ya gama shirinsa ya fito ras cikin kalar sky blue and white sai Black half cover da kuma baƙin zagayen saman hiramin.
Ya fito ras tamkar dai yadda zuriyar mahaifiyarshi da suke tsatson limamen Harami suke fita.
Ko yaya ka ganshi dole kace shi balarabene, sabida komai nashi irin nasune. Kyau, fari, gashi, ilimin addini, nitsuwa, imani, da kuma irin shigarsu, da shima ya rainu da hakan tunda a cikinsu ya girma.
Wani turaren Oud Kareem ya feshe jikinshi dashi.
Lumshe ido yayi sabida shida kanshi ya shaida ƙamshin wannan turaren nashi iyakane.
A hankali ya nufi ƙofar fita yana tafe yana tasbihi.
"Astagafirullaha wa'atubu ilaik.
Astagafirullaha zunuba jami'an. Subahanallahi Wal'hamdulillah wa la'ilahaillahu Allahu Akbar."
Da wuya ka iya jin abinda yake faɗin, sai dai ina ka lura da motsawan jajayen laɓɓansa, masu kama da jajayen kunnen fire masu taushi zaka fahimci tasbihi yakeyi.
Ba kowa a wurin sabida haka ya nufi falo a nitse,
A falon ya samu Sitti bisa dukkan alamu, shirin tafiya harami tayi.
Tana ganinshi ta miƙe tare da cewa.
"Muje ko". Kai ya gyaɗa mata, kana ya ɗan kalleta bayan ya ɗan tsagaita tasbihin bakinshi yace.
"Zan shiga wurin Sheykh Abdulkareem".
Cikin kula tace.
"Muje sai mun dawo mana".
Kanshi ya jujjuya mata kana yace.
"Zan sanar dashi batun komawarmu".
Gyara matafinta tayi tare da cewa.
"Na sani ai, muje sai mun dawo".
Fuskarshi ya ɗan haɗe tare da cewa.
"Ni a harami zan kwana".
Ganin ya kafe tasan fa duk yadda tayi, hakan zaiyi,
binshi kawai tayi,
suna shiga suka samu kamilin dottijon nan, bisa tsakiyar yaranshi, da alamun suma ɗin anjima zasu taho masallacin.
Yana hanƙoshi ya miƙa mishi, hannunshi na dama, da sauri ya isa gareshi, ya kama hannunshi tare da rusunawa, ɗaura hannun yayi bisa tsakiyar kanshi, sannan yayi shiru yanajin yadda dottijon ke zuba mishi addu'o'in.
Yayinda kamilan yaranshi ke amsawa da.
"Ahmeehn! Ahmeehnn!! Ahmeehnn!!!."
Bayan ya gama mishi addu'o'in ne, ya juyo ya gaida kakanun nashi, baki ɗayansu.
Kana ya shaida musu tafiyarsu data taso cikin gaggawa ya kuma sanar musu dalilin tafiyan.
Sun gamsu da hakan, kasan cewar sun ɗan ɓata lokaci a nanne yasa. Tare suka tafi masallacin baki ɗayansu.
Haroon kuwa cikin kwana biyu ya gama musu komai na tafiyarsu, gida dan shima dama yana son tafiya gida shida Jannart ɗinshi duka.
A cikin makarantar su Aysha kuwa.
Sam bata samu lbrin abinda ya faru a rugarsuba.
Sai da yamma, nanma Rafi'a ce, dake riƙe da wayarta tana chatting.
A nan ne ta gani a kafafen yaɗa labarai cewa.
Anyi faɗa a tsakanin MAKIYAYA da manoman, a garin Kikan dake gaɓar kokin Namun.
Koda ta sanarwar Aysha.
Taga tashin hankali ya wuce zatonta,
hakane yasa ta bita suka tafi tare.
Su Bappa kuwa bayan sun nufi, rugar tasune, sukaci karo da motar police officers, da kuma Ambulance ɗin, daya ɗebo su Ummiy dasu Junaidun da Junainah, kana. Da wasu wadanda ake ganin kamar sunada ɗan sauran numfarfashi.
Da sauri C.P Daniyel yasa, drevernsu Arɗo Bani, ya juya dasu, dan suka nufi cikin Genaral Hospital Numan ɗin, sabida yasan in sukaje suka, ga irin kisan gillar da ƙabilun nan sukayiwa yan uwansu, tashin hankali zaiyi yawa ya kuma san A.S.P Kabir da rundunarsa na, can, to zasuyi mishi bayanin da zaisa ya iya korarshi a aikinshi.
Shiyasa ya jasu suka koma, cikin asibitin.
A cewarsa su kula da mutanen su, saura kuma, kuma, akwai hukuma na, kula dasu a can.
To wannan dalilin ne, yasa suka koma cikin asibitin,
Hakane yayi sanadin da koda Waziri da Matawalle da rundunar Hadiman da Sarki ya aiko,
Suka zo, basu ga su Arɗo ba a cikin Rugar, kana kusan wuni sukayi a nan dan sai yamma, suka juya suka koma masarautarsu.
Ita kuwa Aysha, suna zuwa, kai tsaye cikin asibitin suka nufa, dan tayi waya da Bappa.
Koda suka iso, sosai hankalin ta ya tsananta gaba hankalinta ya tashi, ganin gaba ɗaya asibitin a cike yake da mutane su,
sai dai ta ɗan samu nitsuwa kaɗan ganin Ummiy da Junainah sun farfaɗo,
sai dai duk basa mgna sunyi zurui dasu hakama sauran waɗanda suka samu suka farfaɗo ɗin.
Koda ta tambayi Bappa inasu ya Giɗi sai cemata yayi suna gida, ya ɗaura da cemata.
"Yauwa Shatu ku zauna nan, ku kula da marasa lfyan, bari mu kuma mu ƙarasa can Rugar tamu, mu duba meke faruwa a gidan".
Hannu tasa ta share hawayenta dake shatata daga cikin kumburarrun idanunta cikin disashewar muryar da kuka yasa ta dishe tace.
"To Bappa kuje, zamu kuladasu, ga can Ya Salmanu ma, ya turo mana abokanshi, ga kuma ƴan agaji, zamu zauna dasu".
Cikin tarin ƙuna da tafasar zuciya, Alhaji Haro, ya gyara gariyarsa tare da cewa.
"Mu tafi".
Arɗo Bani ne ya miƙe tsaye tare da yin gaba kana duk suka bishi a baya suka fita suka tafi.
A hankali Rafi'a tasa hannu ta tallabi Aysha daketa kuka mai sosa zuciya, kuka mai cike da rauni da taraddadi.
Zama sukayi cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Ki dena kuka Aysha, in sha Allah babu komai."
Murya na rawa hawaye na kwaranya ta buɗe manyan idanunta da suka rine sukayi jazir da kuka da tashin hankali, cikin rauni tace.
"Rafi'a babu komai kuma?, ko dai komai ya faru, kalli fa halin da yan uwana da maƙotanmu suke ciki, kinjifa ance an kashe mutun kusan 40, kuma kin san gidajen rediyo suna ragewa nema wasu lokutan sabida kada, hankali mutanen duniya ya tashi.
Rafi'a banga Yayuna ba, ko ɗaya ban ganiba, banga Inna ba, kalli Junaidu, kalli can Ya Mati yayansu Ya Salmanu. Kowa baya cikin haiyacinsa,
Ummiy ta zama kamar kurma meta gani ya gigitata haka, kalli yadda Junainah keta fizge-fizge alamun taga mugun abun daya firgitane ya ɗimautata.
Rafi'a ga tozarci da cin fuskar da akeyi mana, kallifa babu likitan da yazo ya kula mutanenmu, an barsu ciwukansu nata tsami,
sai Nurses keta, hararanmu.
Rafi'a ya zanyi in banyi kukaba, ina zansa raina, Ina Yah Giɗi, ina Yah Gaini, Ina Yah Seyo? Rafi'a sun kasarani sun rabani da yan uwana."
Kife kanta tayi jikin gadon da Ummiy ke kwance a kai, cikin murya mai cike da rauni tace.
"Ummiy kiyi min mgna mana, Ummiy na inasu Ya Giɗi na ina Ya Gaini, ina Ya Lado, ina ya Seyo, meya hanasu zuwa wurinki na tabbar in suna raye cikin ƙishin lfy, dole zan samu ɗaya daga cikinsu a wurinki".
Mari matar Arɗo Bani ce wacce ta ɗan dawo haiyacinta ne, ta rumtse idanunta wasu zafafan hawaye ne suka silalo mata, cikin sanyi tace.
"Shatu sun tafi kiwo ne, zaki gansu".
Jajayen idanunta ta zura mata,
Alamun tana son tabbatar da abinda tace matan.
Fahimtar hakane yasa ta gyaɗa mata kai alamar eh hakane.
Cikin son kontar mata hanlali ne, Rafi'a, tace.
"Kinjiko Aysha, to kiyi haƙuri ki nitsu in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi".
Kife kanta ta kumayi tana mai sake kuka mai ciwo a zuciya, gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Haka dai sukaci gaba da bata baki, wai dan ta samu nitsuwa amman ina, fargabanta sai tsananta yakeyi.
Su Bappa kuwa, isarsu Rugar Kikan ya ƙara tada hankali matasansu da suka dawo kiwo da matansu da suka dawo tallan nono wanda sanadin basa nanne yasa suka tsira.
Gaba ɗaya Rugar ta birkice ta kiɗime.
Hankali dattawan nan yayi masifar tashi, ganin duk an karkashe musu, mafiya yawan matansu yaransu da jikokinsu.
Especially Alhaji Haro, da iya cikin gidansa kawai saida aka samu gawar mutun goma sha uku.
Koda aka jera masa gawakin suma yayi. Sai ga Tsoffin nan suna kuka cur-cur da hawayensu, gwanin ban tausayi.
Ganin yamma na rufawane yasa,
Dattawan maƙotansu, mazansu suka fara wonke gawakin maza kamar yadda addininmu ya koyar da mu.
Mata kuma sukayiwa mata wonka,
Kana suka sallaci Gawarwakin da a ƙalla sun kai mutun Settin da uku 63.
Kana suka rinƙa binnesu da taimakon Hausawa musulman cikin Numan da maƙotansu fulani.
Gaba ɗaya garin yayi tsit ya koma tamkar kufayi. Sauran rayayyun sunyi Kuka har muryoyinsu. Sun disashe.
A cikin Genaral Hospital Numan kuwa.
Musulmai Hausawa da Fulani, sune suka rinƙa kawai Fulanin Rugar Kikan taimakon abinci.
Hankalin Aysha ya ƙara tashi ganin, har dare babu wanda yazo.
Hakama da gari ya waye.
yana ɗaure da wani babban towel mai ɗan karen kyau da taushi bayan ya matse wancan ya shanya.
Yana saƙo ƙafarshi cikin bedroom ɗin ya...!
Solo-salo-salon GARKUWA na dabanne!
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 13
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘
FREE PAGE
Littafin GARKUWA na kuɗine, Special Group 1k Normal 300, in kina buƙatar karanta lbrin GARKUWA turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276. Gareku mutanen Special Group turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.
*Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki, in kin san zaki sayi littafinane dan ki fitar dashi, na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki saya bana son kuɗinki, ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina. Dan Allah nace badon niba.*
Yaji anata bubbuga mishi ƙofar ɗakin,
bai kulaba, yazo a zauna bisa kujerar dreesing mirror, a hankali yake tsane ruwan jikinshi, bayan ya gama ɗan tsane ruwanne ya busar da tattausan sumar kanshi, ta hanyar na'urar busar da gashi.
Mai ya ɗan shafa, kana ya gyara gashin da kyau, sannan ya miƙe yaje gaban.
Drower'n, a nitse ya buɗe, wasu datsatstsun kaya riga da wondo na yadin Lamud, yadin Sky blue ne mai masifar kyau. Sai kuma ya zaro wata farar al'kyabbar fara ƙal. Da farin hirami.
Rufe wannan gefen yayi, kana ya buɗe ɗaya gefen.
Ƙananan kayan ne a ciki kamarsu Jallabiya da boxes vest dasu zagayen baƙin abin da yake ɗaurawa kam hiraminshi.
Suma duk mafi akasari su fararene.
A bakin gadon ya ajiyesu.
Kana ya fara kimtsawa.
Bayan ya gama shirinsa ya fito ras cikin kalar sky blue and white sai Black half cover da kuma baƙin zagayen saman hiramin.
Ya fito ras tamkar dai yadda zuriyar mahaifiyarshi da suke tsatson limamen Harami suke fita.
Ko yaya ka ganshi dole kace shi balarabene, sabida komai nashi irin nasune. Kyau, fari, gashi, ilimin addini, nitsuwa, imani, da kuma irin shigarsu, da shima ya rainu da hakan tunda a cikinsu ya girma.
Wani turaren Oud Kareem ya feshe jikinshi dashi.
Lumshe ido yayi sabida shida kanshi ya shaida ƙamshin wannan turaren nashi iyakane.
A hankali ya nufi ƙofar fita yana tafe yana tasbihi.
"Astagafirullaha wa'atubu ilaik.
Astagafirullaha zunuba jami'an. Subahanallahi Wal'hamdulillah wa la'ilahaillahu Allahu Akbar."
Da wuya ka iya jin abinda yake faɗin, sai dai ina ka lura da motsawan jajayen laɓɓansa, masu kama da jajayen kunnen fire masu taushi zaka fahimci tasbihi yakeyi.
Ba kowa a wurin sabida haka ya nufi falo a nitse,
A falon ya samu Sitti bisa dukkan alamu, shirin tafiya harami tayi.
Tana ganinshi ta miƙe tare da cewa.
"Muje ko". Kai ya gyaɗa mata, kana ya ɗan kalleta bayan ya ɗan tsagaita tasbihin bakinshi yace.
"Zan shiga wurin Sheykh Abdulkareem".
Cikin kula tace.
"Muje sai mun dawo mana".
Kanshi ya jujjuya mata kana yace.
"Zan sanar dashi batun komawarmu".
Gyara matafinta tayi tare da cewa.
"Na sani ai, muje sai mun dawo".
Fuskarshi ya ɗan haɗe tare da cewa.
"Ni a harami zan kwana".
Ganin ya kafe tasan fa duk yadda tayi, hakan zaiyi,
binshi kawai tayi,
suna shiga suka samu kamilin dottijon nan, bisa tsakiyar yaranshi, da alamun suma ɗin anjima zasu taho masallacin.
Yana hanƙoshi ya miƙa mishi, hannunshi na dama, da sauri ya isa gareshi, ya kama hannunshi tare da rusunawa, ɗaura hannun yayi bisa tsakiyar kanshi, sannan yayi shiru yanajin yadda dottijon ke zuba mishi addu'o'in.
Yayinda kamilan yaranshi ke amsawa da.
"Ahmeehn! Ahmeehnn!! Ahmeehnn!!!."
Bayan ya gama mishi addu'o'in ne, ya juyo ya gaida kakanun nashi, baki ɗayansu.
Kana ya shaida musu tafiyarsu data taso cikin gaggawa ya kuma sanar musu dalilin tafiyan.
Sun gamsu da hakan, kasan cewar sun ɗan ɓata lokaci a nanne yasa. Tare suka tafi masallacin baki ɗayansu.
Haroon kuwa cikin kwana biyu ya gama musu komai na tafiyarsu, gida dan shima dama yana son tafiya gida shida Jannart ɗinshi duka.
A cikin makarantar su Aysha kuwa.
Sam bata samu lbrin abinda ya faru a rugarsuba.
Sai da yamma, nanma Rafi'a ce, dake riƙe da wayarta tana chatting.
A nan ne ta gani a kafafen yaɗa labarai cewa.
Anyi faɗa a tsakanin MAKIYAYA da manoman, a garin Kikan dake gaɓar kokin Namun.
Koda ta sanarwar Aysha.
Taga tashin hankali ya wuce zatonta,
hakane yasa ta bita suka tafi tare.
Su Bappa kuwa bayan sun nufi, rugar tasune, sukaci karo da motar police officers, da kuma Ambulance ɗin, daya ɗebo su Ummiy dasu Junaidun da Junainah, kana. Da wasu wadanda ake ganin kamar sunada ɗan sauran numfarfashi.
Da sauri C.P Daniyel yasa, drevernsu Arɗo Bani, ya juya dasu, dan suka nufi cikin Genaral Hospital Numan ɗin, sabida yasan in sukaje suka, ga irin kisan gillar da ƙabilun nan sukayiwa yan uwansu, tashin hankali zaiyi yawa ya kuma san A.S.P Kabir da rundunarsa na, can, to zasuyi mishi bayanin da zaisa ya iya korarshi a aikinshi.
Shiyasa ya jasu suka koma, cikin asibitin.
A cewarsa su kula da mutanen su, saura kuma, kuma, akwai hukuma na, kula dasu a can.
To wannan dalilin ne, yasa suka koma cikin asibitin,
Hakane yayi sanadin da koda Waziri da Matawalle da rundunar Hadiman da Sarki ya aiko,
Suka zo, basu ga su Arɗo ba a cikin Rugar, kana kusan wuni sukayi a nan dan sai yamma, suka juya suka koma masarautarsu.
Ita kuwa Aysha, suna zuwa, kai tsaye cikin asibitin suka nufa, dan tayi waya da Bappa.
Koda suka iso, sosai hankalin ta ya tsananta gaba hankalinta ya tashi, ganin gaba ɗaya asibitin a cike yake da mutane su,
sai dai ta ɗan samu nitsuwa kaɗan ganin Ummiy da Junainah sun farfaɗo,
sai dai duk basa mgna sunyi zurui dasu hakama sauran waɗanda suka samu suka farfaɗo ɗin.
Koda ta tambayi Bappa inasu ya Giɗi sai cemata yayi suna gida, ya ɗaura da cemata.
"Yauwa Shatu ku zauna nan, ku kula da marasa lfyan, bari mu kuma mu ƙarasa can Rugar tamu, mu duba meke faruwa a gidan".
Hannu tasa ta share hawayenta dake shatata daga cikin kumburarrun idanunta cikin disashewar muryar da kuka yasa ta dishe tace.
"To Bappa kuje, zamu kuladasu, ga can Ya Salmanu ma, ya turo mana abokanshi, ga kuma ƴan agaji, zamu zauna dasu".
Cikin tarin ƙuna da tafasar zuciya, Alhaji Haro, ya gyara gariyarsa tare da cewa.
"Mu tafi".
Arɗo Bani ne ya miƙe tsaye tare da yin gaba kana duk suka bishi a baya suka fita suka tafi.
A hankali Rafi'a tasa hannu ta tallabi Aysha daketa kuka mai sosa zuciya, kuka mai cike da rauni da taraddadi.
Zama sukayi cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Ki dena kuka Aysha, in sha Allah babu komai."
Murya na rawa hawaye na kwaranya ta buɗe manyan idanunta da suka rine sukayi jazir da kuka da tashin hankali, cikin rauni tace.
"Rafi'a babu komai kuma?, ko dai komai ya faru, kalli fa halin da yan uwana da maƙotanmu suke ciki, kinjifa ance an kashe mutun kusan 40, kuma kin san gidajen rediyo suna ragewa nema wasu lokutan sabida kada, hankali mutanen duniya ya tashi.
Rafi'a banga Yayuna ba, ko ɗaya ban ganiba, banga Inna ba, kalli Junaidu, kalli can Ya Mati yayansu Ya Salmanu. Kowa baya cikin haiyacinsa,
Ummiy ta zama kamar kurma meta gani ya gigitata haka, kalli yadda Junainah keta fizge-fizge alamun taga mugun abun daya firgitane ya ɗimautata.
Rafi'a ga tozarci da cin fuskar da akeyi mana, kallifa babu likitan da yazo ya kula mutanenmu, an barsu ciwukansu nata tsami,
sai Nurses keta, hararanmu.
Rafi'a ya zanyi in banyi kukaba, ina zansa raina, Ina Yah Giɗi, ina Yah Gaini, Ina Yah Seyo? Rafi'a sun kasarani sun rabani da yan uwana."
Kife kanta tayi jikin gadon da Ummiy ke kwance a kai, cikin murya mai cike da rauni tace.
"Ummiy kiyi min mgna mana, Ummiy na inasu Ya Giɗi na ina Ya Gaini, ina Ya Lado, ina ya Seyo, meya hanasu zuwa wurinki na tabbar in suna raye cikin ƙishin lfy, dole zan samu ɗaya daga cikinsu a wurinki".
Mari matar Arɗo Bani ce wacce ta ɗan dawo haiyacinta ne, ta rumtse idanunta wasu zafafan hawaye ne suka silalo mata, cikin sanyi tace.
"Shatu sun tafi kiwo ne, zaki gansu".
Jajayen idanunta ta zura mata,
Alamun tana son tabbatar da abinda tace matan.
Fahimtar hakane yasa ta gyaɗa mata kai alamar eh hakane.
Cikin son kontar mata hanlali ne, Rafi'a, tace.
"Kinjiko Aysha, to kiyi haƙuri ki nitsu in sha Allah dukkan tsanani yana tare da sauƙi".
Kife kanta ta kumayi tana mai sake kuka mai ciwo a zuciya, gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Haka dai sukaci gaba da bata baki, wai dan ta samu nitsuwa amman ina, fargabanta sai tsananta yakeyi.
Su Bappa kuwa, isarsu Rugar Kikan ya ƙara tada hankali matasansu da suka dawo kiwo da matansu da suka dawo tallan nono wanda sanadin basa nanne yasa suka tsira.
Gaba ɗaya Rugar ta birkice ta kiɗime.
Hankali dattawan nan yayi masifar tashi, ganin duk an karkashe musu, mafiya yawan matansu yaransu da jikokinsu.
Especially Alhaji Haro, da iya cikin gidansa kawai saida aka samu gawar mutun goma sha uku.
Koda aka jera masa gawakin suma yayi. Sai ga Tsoffin nan suna kuka cur-cur da hawayensu, gwanin ban tausayi.
Ganin yamma na rufawane yasa,
Dattawan maƙotansu, mazansu suka fara wonke gawakin maza kamar yadda addininmu ya koyar da mu.
Mata kuma sukayiwa mata wonka,
Kana suka sallaci Gawarwakin da a ƙalla sun kai mutun Settin da uku 63.
Kana suka rinƙa binnesu da taimakon Hausawa musulman cikin Numan da maƙotansu fulani.
Gaba ɗaya garin yayi tsit ya koma tamkar kufayi. Sauran rayayyun sunyi Kuka har muryoyinsu. Sun disashe.
A cikin Genaral Hospital Numan kuwa.
Musulmai Hausawa da Fulani, sune suka rinƙa kawai Fulanin Rugar Kikan taimakon abinci.
Hankalin Aysha ya ƙara tashi ganin, har dare babu wanda yazo.
Hakama da gari ya waye.