Sashe 137
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ita kuwa Aysha Anan falon ta zauna tana tunani kala-kala musamman akan masarautar sam ta kasa gane mata.
A kullum da kalar surƙullen da zai bayyanar mata, ko meye ma'anar zantukan da suke yawan yi wanda bata gane masa ba?.
Dazu tajiyo Gimbiya Saudatau da Sheikh maganganunta sun bata mamaki, lallai akwai wani babban al'amari a cikin gidan nan, wanda da sannu zata fahimci menene wannan abu.
Kuma zata tambayi Ummi wani abu ko zata gaya mata, ko ta samu sauƙin Tsarkakkiyar dakw cinnzuciyarta.
Tana nan zaune har aka kira sallar la'asar ta tashi daƙyar don har yanzun bata jin dadin jikinta.
Bedroom ɗin ta ta wuce.
Kai tsaye Bathroom ta nufa.
Al'wala ta ɗauro don har masallacin masarautar sun tada kabbara.
A hankali take taku sabida har yanzu tanajin jikinta na mata zafin rabuwa da budurci.
Sallaya ta shimfiɗa kana itama ta tada kabbara.
Bayan ta idar da sallah ne,
ta kuma miƙewa a hankali ta fito falo, sabida ta gaji da baccin kwanciya tayi bisa kujera da wayarta a hannunta, tana mgna da Junaidu.
Ummi kuwa tana kitchen.
Murmushi ta ɗanyi jin Junaidun na cewa.
"Dan Allah Adda Shatu kicewa su Bappa su dawo haka nan, zamansu a waccar ƙasar ya isa.
Ina kewar Junainah, Rugar Bani gaba ɗaya muna kewarsu dan Allah su dawo".
Gyara konciyarta tayi tare da cewa.
"To Junaidu in sha Allah zan gaya musu, su dawo maka da masoyiyarka dan nima nayi kewar Junnu ina kewar Ummey na".
Ummu dake kitchin ne ta ɗan tsagaita daga motsa naman da take fasawa Aysha
Sabida jiyo sallamar Hajiya Mama da Aunty Zuwairiyya.
Haka yasa ta fito tai musu barka da zuwa kana suka gaisa tare.
Sannan tace su isa Aysha na ciki.
To Juwairiyya tace kana tai gaba Hajia Mama na biye da ita a baya.
Ita kuma Ummi ta koma Kitchen dan kawo musu ruwa.
Ba a jima ba sosai Ummi ta debo drinks ta fito da nufin kai musu.
Sai kuma sukayi kiciɓis a bakin ƙofar falon Ayshan. Sun fito falon Shatu fuskarsu a murtuke, da alamun ransu a ɓace, suka wuce ta.
A hankali ta bisu da ido, tare da tambayarsu.
"Har kun fito ko ruwa baku shaba".
Dukansu babu wacce ta kulata suka fice.
Ajiyan zuciya ta ja ciki da mamaki, sai kuma ta juya ta nufi falon Ayshan.
Tana gab da shiga falon ta ji sautin muryar Aysha na faɗa da ɗan ɗaga murya take cewa. "Mitssssss munafukan banza masu fuska biyu mugaye masu baƙaƙen zuciya. In sha Allah sai Allah ya toni asirinku!".
Da sauri Ummi ta ƙaraso gareta tare da ajiye tray'n hannnunta bisa stoll cikin kula tace.
"Lafiya dai Shatu Meya faru?".
Girgiza kai Shatun ta yi cikin jin haushi ta ce
"Ummi nace bana son su, bana son ganin sun shiga rayuwata, bana son su rinƙa zuwa inda nake saboda na tsani mu'amala da mai fuska biyu."
Ajiyar zuciya Ummi ta yi tana jujjuya zancen Shatun, da kuma tsananin mamakin takun sakar dake tsakanin Aysha da Hajiya Mama.
Numfashin ta ɗan fesar tare da dafa kafaɗarta kana a hankali tace.
"Shike nan ki yi hakuri yanzu ai sun fita."
Ƙwafa Aysha ta yi tare da kishingiɗa sosai tana mamakin yanda mutanen gidan suka kasa fahimtar komai tana matuƙar mmkin in ance wai Hajia Mama itace Mamansu Sheykh kuma ita har yau bata yardaba bata kuma jin zata yarda har gaban abadan.
Bayan ta idar da sallar isha har yanzun jikinta ba kwari haka tana jin ciwo a gabanta musamman in ta miƙe tana tattakawa, miƙewa ta yi a ciccije, "Wash Allah na!".
Ta faɗa haɗe da miƙewar ta fara tafiya tana gwale-gwale kamar ƴar kaciya, kallonta Ummi ta yi tana nazarinta, bayan ta shige ɗaki ta tashi ta bita ɗakin.
A tsaye ta sameta gaban drower'nta.
Juyowa tayi ta kalli Ummin dake matsowa kusa da ita tare da cewa.
"Aysha kin sake shiga ruwan ɗumi kuwa?".
Kai ta jujjuya mata a hankali tace.
"Ɗazu da yamma dai na shiga".
Kai Ummi ta jinjina kana tace.
"Yauwa to kije yanzuma ki shiga ruwan ɗumi zakiji sauƙin abin sosai."
Ya mutsa fuska ta yi irin na mai jin ba daɗi kana cikin sanyi tsce.
"Ummi bana jin daɗi kwata-kwata."
Kusa da ita ta matso cikkn kula tace.
"Na sani, amma shiga ruwan ɗumin zai tai maka kwarai wajen jin daɗinki, don zaki sake sosai, duk wannan ciwo-ciwon zaki daina ji." Kwafe fuska ta yi kamar zata yi kuka.
Yanayinta Ummi ta kalla, ta so yin dariya sai dai kuma danne tare da cewa.
"Yi haƙuri kin ji Ayshs, daure kada ki zama raguwa mana."
"Uhmm".
kawai tace ta miƙe ta shige cikin bathroom.
Ita kuma Ummi ta wuce kitchen tare da ɗauko haɗaɗɗen kunun gero wanda ake yinsa na musamman kuma shi ake bawa amaren masarautar haɗe da farfesun farararen tattabaru, wanda shi ma wani haɗi ne na sirri mai tsuma mace, da yajin da ake barbaɗawa akan tattabarun wanda yake ƙarawa mace wani ɗanɗano na musamman.
Ita kuwa Aysha ta daɗe cikin ruwan ɗumin tana jin wani irin daɗi na ratsa ta, lumshe ido ta yi, tare da miƙewa tayi wanko fes kana ta fito.
Tana buɗe toilet ɗin ta ji ɗakin na ƙamshin wannan gashin tattabarun da Ummi ta kawo mata su har ɗaki.
A hankali ta matso gefen Ummi dake cewa.
"Yauwa kin fito ko Aysha?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh Ummi".
"To yanzu ya kikaji jikin naki?".
Ummi ta kuma tambayarta.
A kunyace tace.
"Alhamdulillah naji sauƙin".
Cikin gamsuwa Ummi tace.
"Toh zo ki zauna ga wannan kici duk za su ƙara miki ƙwarin jiki." Girgiza kai tayi alamar bazata ciba.
"Yi haƙuri ki daure kici." Ummi ta daɗi mata cikin lallami.
Zama Ummi tayi tare da janyo flask ɗin ta zuba mata mai ɗan yawa.
Kana ta turo mata plate ɗin gabanta, kunu ta tsiyaya mata a cup mai ɗan girma ta miƙa mata tare da cewa.
"Yauwa maza kici zakiji daɗin jikinki".
A hankali ta gyaɗa mata kai, dan bacci ya fara kashe mata jiki.
Cikin lumshe ido ta fara sawa a bakinta.
Jin wani irin ɗanɗano mai daɗi ya ziyarce harshenta ne yasata, lumshe ido tare da haɗiye tsinkekken yawun bakinta ta cigaba da taunawa tana haɗiyewa tare da korawa da kunun geron.
Ummi kuwa tana ganin ta faraci ne ta wuce ta fita.
Bayan ta gama ta shanye kunun don shi ma ya yi mata daɗi sosai.
Cike da bacci ta ɗaura plate ɗin kan kofin ta turasu gefe kana a kasalance.
Ta wonke hannunta.
hamma mai sanyi tayi kana ta kwanta nan bacci ya yayi awon gaba da ita.
Shi kuwa Sheikh yana dawowa daga sallar isha ɓangarensa ya wuce kai tsaye.
Yana shiga bedroom ɗin sa ya zare al,kyabbarsa tare ta ajiye hirami gefen gadonsa ya zauna, yana ajiyar zuciya tare da lumshe idonsa.
Wayarsa ce ta yi suwa,
Ido ya zubawa wayar yana kallon mai kiran, kamar ba zai ɗaga ba,
Sai kuma dai ya janyota hade da murza screen ɗin wayar.
Da sallama ya amsa. Cikin zolaya Haroon ya ce.
"Barka da dare angon Shatu."
Wani ɗan guntun Murmushi Sheikh ya yi, haka nan yaji sunan yamishi raɗau yayi masa a kunne a zahiri kuwa ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Bana son surutu fa." Cikin Murmushi shi ma Haroon yace.
"Kasan dai ba ƙarya na yi ba, balle ka fara yi min wa'azi."
Gyada kansa yayi tare da cewa.
"To ina jinka menene zaka kirani da daren nan?".
Murmushi nan Haroon ya cigaba da tsokanarshi har ya gaji ya katse kiran.
Dai-dai lokacin kuma ya ya fara jin yunwa haɗe da zazzabi mai zafin gaske wanda ya jisa atake.
A hankali ya miƙe yana jin zazzaɓin tamkar wanda ake ƙarawa tun daga kan yatsansa har zuwa saman kansa, cikin tafiya a hankali ya fito daga bedroom ɗin zazzaɓin na cigaba da fisgarsa da ƙyar ya kai tsaƙiyar falon ya zauna kan kujerun dake falon, a hankali ya kwantar da kansa jikin kujerar yana furzar da numfashi mai zafi, lumshe ido ya yi, saboda ƙugin yunwa da cikinsa ke yi, zaman da ya yi, so yake ya ji dama-dama ya ci abincin ya kwanta, tun yana iya jujjuya jikinsa har ya gagara yin hakan saboda ilahirin gaɓoɓinsa sun amsa da zazzafan zazzaɓin ji yakeyi gaba ɗaya gabban jikinsa kamar allurai ake sokawa mushi, yana nan kwance har wajen ƙarfe ɗaya na dare jikinsa na karkarwa.
Cikin rawan sanyi daƙyar ya lallaɓa ya samu ya shiga bedroom ya kwanta a kan gadon a gicciye, hannunsa na rawar ɗari ya janyo blanket ya rufe dukkan jikinsa, shi kansa yana jiyo hucin numfashinsa da zafi, yana yi yana ɗan nishin azaba ƙadan,
a haka ya samu yayi baccin wahala mai cike da rikitaccen mafarki mara kan gado.
Kiran sallan farko ne ya tashe shi, cikin yanayi wanda bai saba tsintar kansa ciki ba ya miƙe, kasala-kasala gajiya-gajiya, ga mamakinsa zazzaɓin ya sauka, don yana ga ɗumin da jikinsa ya fitar da gumi alamun sauƙan zazzaɓi duk da akwai sanyi ac, addu'a ya yi ya miƙe a hankali ya shige toilet sai da yayi wonka da ruwa mai sanyi sannan yaji jikinsa ya yi masa daɗi.
Da sauri ya fito ya fara shirin zuwa masallacin masarautar don har sun fara kiran assalatu.
Bayan sun idar da sallan acan ya yi zamansa don gabatar da azkar da sauran addu'o'in da yake gabatarwa a dai-dai lokacin, sai da gari ya yi washe sannan ya dawo ya wuce falonsa kai tsaye.
Da hantsi ya fito daga falon. Cikin shigarsa ta yau da kullum.
A nan ya taradda su ita da Ummi suna zaune.
Da alamun Ummi nata lallashinta akan ta yi breakfast ne.
Tsayuwa ya ɗan yi gefensu tare da cewa.
"Ummi yunwa".
murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Dama yanzu nakeso Aysha taci, sai ta kai maka nakan."
A hankali ya ɗan yi taku biyu zuwa uku, ya kana ya zauna bisa kujerar dake fuskantar tasu.
Ido ya ɗan zuba mata, tare da jingina kansa jikin kujera.
Cike da wani irin mayataccen shauƙi.
A kullum da kalar surƙullen da zai bayyanar mata, ko meye ma'anar zantukan da suke yawan yi wanda bata gane masa ba?.
Dazu tajiyo Gimbiya Saudatau da Sheikh maganganunta sun bata mamaki, lallai akwai wani babban al'amari a cikin gidan nan, wanda da sannu zata fahimci menene wannan abu.
Kuma zata tambayi Ummi wani abu ko zata gaya mata, ko ta samu sauƙin Tsarkakkiyar dakw cinnzuciyarta.
Tana nan zaune har aka kira sallar la'asar ta tashi daƙyar don har yanzun bata jin dadin jikinta.
Bedroom ɗin ta ta wuce.
Kai tsaye Bathroom ta nufa.
Al'wala ta ɗauro don har masallacin masarautar sun tada kabbara.
A hankali take taku sabida har yanzu tanajin jikinta na mata zafin rabuwa da budurci.
Sallaya ta shimfiɗa kana itama ta tada kabbara.
Bayan ta idar da sallah ne,
ta kuma miƙewa a hankali ta fito falo, sabida ta gaji da baccin kwanciya tayi bisa kujera da wayarta a hannunta, tana mgna da Junaidu.
Ummi kuwa tana kitchen.
Murmushi ta ɗanyi jin Junaidun na cewa.
"Dan Allah Adda Shatu kicewa su Bappa su dawo haka nan, zamansu a waccar ƙasar ya isa.
Ina kewar Junainah, Rugar Bani gaba ɗaya muna kewarsu dan Allah su dawo".
Gyara konciyarta tayi tare da cewa.
"To Junaidu in sha Allah zan gaya musu, su dawo maka da masoyiyarka dan nima nayi kewar Junnu ina kewar Ummey na".
Ummu dake kitchin ne ta ɗan tsagaita daga motsa naman da take fasawa Aysha
Sabida jiyo sallamar Hajiya Mama da Aunty Zuwairiyya.
Haka yasa ta fito tai musu barka da zuwa kana suka gaisa tare.
Sannan tace su isa Aysha na ciki.
To Juwairiyya tace kana tai gaba Hajia Mama na biye da ita a baya.
Ita kuma Ummi ta koma Kitchen dan kawo musu ruwa.
Ba a jima ba sosai Ummi ta debo drinks ta fito da nufin kai musu.
Sai kuma sukayi kiciɓis a bakin ƙofar falon Ayshan. Sun fito falon Shatu fuskarsu a murtuke, da alamun ransu a ɓace, suka wuce ta.
A hankali ta bisu da ido, tare da tambayarsu.
"Har kun fito ko ruwa baku shaba".
Dukansu babu wacce ta kulata suka fice.
Ajiyan zuciya ta ja ciki da mamaki, sai kuma ta juya ta nufi falon Ayshan.
Tana gab da shiga falon ta ji sautin muryar Aysha na faɗa da ɗan ɗaga murya take cewa. "Mitssssss munafukan banza masu fuska biyu mugaye masu baƙaƙen zuciya. In sha Allah sai Allah ya toni asirinku!".
Da sauri Ummi ta ƙaraso gareta tare da ajiye tray'n hannnunta bisa stoll cikin kula tace.
"Lafiya dai Shatu Meya faru?".
Girgiza kai Shatun ta yi cikin jin haushi ta ce
"Ummi nace bana son su, bana son ganin sun shiga rayuwata, bana son su rinƙa zuwa inda nake saboda na tsani mu'amala da mai fuska biyu."
Ajiyar zuciya Ummi ta yi tana jujjuya zancen Shatun, da kuma tsananin mamakin takun sakar dake tsakanin Aysha da Hajiya Mama.
Numfashin ta ɗan fesar tare da dafa kafaɗarta kana a hankali tace.
"Shike nan ki yi hakuri yanzu ai sun fita."
Ƙwafa Aysha ta yi tare da kishingiɗa sosai tana mamakin yanda mutanen gidan suka kasa fahimtar komai tana matuƙar mmkin in ance wai Hajia Mama itace Mamansu Sheykh kuma ita har yau bata yardaba bata kuma jin zata yarda har gaban abadan.
Bayan ta idar da sallar isha har yanzun jikinta ba kwari haka tana jin ciwo a gabanta musamman in ta miƙe tana tattakawa, miƙewa ta yi a ciccije, "Wash Allah na!".
Ta faɗa haɗe da miƙewar ta fara tafiya tana gwale-gwale kamar ƴar kaciya, kallonta Ummi ta yi tana nazarinta, bayan ta shige ɗaki ta tashi ta bita ɗakin.
A tsaye ta sameta gaban drower'nta.
Juyowa tayi ta kalli Ummin dake matsowa kusa da ita tare da cewa.
"Aysha kin sake shiga ruwan ɗumi kuwa?".
Kai ta jujjuya mata a hankali tace.
"Ɗazu da yamma dai na shiga".
Kai Ummi ta jinjina kana tace.
"Yauwa to kije yanzuma ki shiga ruwan ɗumi zakiji sauƙin abin sosai."
Ya mutsa fuska ta yi irin na mai jin ba daɗi kana cikin sanyi tsce.
"Ummi bana jin daɗi kwata-kwata."
Kusa da ita ta matso cikkn kula tace.
"Na sani, amma shiga ruwan ɗumin zai tai maka kwarai wajen jin daɗinki, don zaki sake sosai, duk wannan ciwo-ciwon zaki daina ji." Kwafe fuska ta yi kamar zata yi kuka.
Yanayinta Ummi ta kalla, ta so yin dariya sai dai kuma danne tare da cewa.
"Yi haƙuri kin ji Ayshs, daure kada ki zama raguwa mana."
"Uhmm".
kawai tace ta miƙe ta shige cikin bathroom.
Ita kuma Ummi ta wuce kitchen tare da ɗauko haɗaɗɗen kunun gero wanda ake yinsa na musamman kuma shi ake bawa amaren masarautar haɗe da farfesun farararen tattabaru, wanda shi ma wani haɗi ne na sirri mai tsuma mace, da yajin da ake barbaɗawa akan tattabarun wanda yake ƙarawa mace wani ɗanɗano na musamman.
Ita kuwa Aysha ta daɗe cikin ruwan ɗumin tana jin wani irin daɗi na ratsa ta, lumshe ido ta yi, tare da miƙewa tayi wanko fes kana ta fito.
Tana buɗe toilet ɗin ta ji ɗakin na ƙamshin wannan gashin tattabarun da Ummi ta kawo mata su har ɗaki.
A hankali ta matso gefen Ummi dake cewa.
"Yauwa kin fito ko Aysha?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Eh Ummi".
"To yanzu ya kikaji jikin naki?".
Ummi ta kuma tambayarta.
A kunyace tace.
"Alhamdulillah naji sauƙin".
Cikin gamsuwa Ummi tace.
"Toh zo ki zauna ga wannan kici duk za su ƙara miki ƙwarin jiki." Girgiza kai tayi alamar bazata ciba.
"Yi haƙuri ki daure kici." Ummi ta daɗi mata cikin lallami.
Zama Ummi tayi tare da janyo flask ɗin ta zuba mata mai ɗan yawa.
Kana ta turo mata plate ɗin gabanta, kunu ta tsiyaya mata a cup mai ɗan girma ta miƙa mata tare da cewa.
"Yauwa maza kici zakiji daɗin jikinki".
A hankali ta gyaɗa mata kai, dan bacci ya fara kashe mata jiki.
Cikin lumshe ido ta fara sawa a bakinta.
Jin wani irin ɗanɗano mai daɗi ya ziyarce harshenta ne yasata, lumshe ido tare da haɗiye tsinkekken yawun bakinta ta cigaba da taunawa tana haɗiyewa tare da korawa da kunun geron.
Ummi kuwa tana ganin ta faraci ne ta wuce ta fita.
Bayan ta gama ta shanye kunun don shi ma ya yi mata daɗi sosai.
Cike da bacci ta ɗaura plate ɗin kan kofin ta turasu gefe kana a kasalance.
Ta wonke hannunta.
hamma mai sanyi tayi kana ta kwanta nan bacci ya yayi awon gaba da ita.
Shi kuwa Sheikh yana dawowa daga sallar isha ɓangarensa ya wuce kai tsaye.
Yana shiga bedroom ɗin sa ya zare al,kyabbarsa tare ta ajiye hirami gefen gadonsa ya zauna, yana ajiyar zuciya tare da lumshe idonsa.
Wayarsa ce ta yi suwa,
Ido ya zubawa wayar yana kallon mai kiran, kamar ba zai ɗaga ba,
Sai kuma dai ya janyota hade da murza screen ɗin wayar.
Da sallama ya amsa. Cikin zolaya Haroon ya ce.
"Barka da dare angon Shatu."
Wani ɗan guntun Murmushi Sheikh ya yi, haka nan yaji sunan yamishi raɗau yayi masa a kunne a zahiri kuwa ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Bana son surutu fa." Cikin Murmushi shi ma Haroon yace.
"Kasan dai ba ƙarya na yi ba, balle ka fara yi min wa'azi."
Gyada kansa yayi tare da cewa.
"To ina jinka menene zaka kirani da daren nan?".
Murmushi nan Haroon ya cigaba da tsokanarshi har ya gaji ya katse kiran.
Dai-dai lokacin kuma ya ya fara jin yunwa haɗe da zazzabi mai zafin gaske wanda ya jisa atake.
A hankali ya miƙe yana jin zazzaɓin tamkar wanda ake ƙarawa tun daga kan yatsansa har zuwa saman kansa, cikin tafiya a hankali ya fito daga bedroom ɗin zazzaɓin na cigaba da fisgarsa da ƙyar ya kai tsaƙiyar falon ya zauna kan kujerun dake falon, a hankali ya kwantar da kansa jikin kujerar yana furzar da numfashi mai zafi, lumshe ido ya yi, saboda ƙugin yunwa da cikinsa ke yi, zaman da ya yi, so yake ya ji dama-dama ya ci abincin ya kwanta, tun yana iya jujjuya jikinsa har ya gagara yin hakan saboda ilahirin gaɓoɓinsa sun amsa da zazzafan zazzaɓin ji yakeyi gaba ɗaya gabban jikinsa kamar allurai ake sokawa mushi, yana nan kwance har wajen ƙarfe ɗaya na dare jikinsa na karkarwa.
Cikin rawan sanyi daƙyar ya lallaɓa ya samu ya shiga bedroom ya kwanta a kan gadon a gicciye, hannunsa na rawar ɗari ya janyo blanket ya rufe dukkan jikinsa, shi kansa yana jiyo hucin numfashinsa da zafi, yana yi yana ɗan nishin azaba ƙadan,
a haka ya samu yayi baccin wahala mai cike da rikitaccen mafarki mara kan gado.
Kiran sallan farko ne ya tashe shi, cikin yanayi wanda bai saba tsintar kansa ciki ba ya miƙe, kasala-kasala gajiya-gajiya, ga mamakinsa zazzaɓin ya sauka, don yana ga ɗumin da jikinsa ya fitar da gumi alamun sauƙan zazzaɓi duk da akwai sanyi ac, addu'a ya yi ya miƙe a hankali ya shige toilet sai da yayi wonka da ruwa mai sanyi sannan yaji jikinsa ya yi masa daɗi.
Da sauri ya fito ya fara shirin zuwa masallacin masarautar don har sun fara kiran assalatu.
Bayan sun idar da sallan acan ya yi zamansa don gabatar da azkar da sauran addu'o'in da yake gabatarwa a dai-dai lokacin, sai da gari ya yi washe sannan ya dawo ya wuce falonsa kai tsaye.
Da hantsi ya fito daga falon. Cikin shigarsa ta yau da kullum.
A nan ya taradda su ita da Ummi suna zaune.
Da alamun Ummi nata lallashinta akan ta yi breakfast ne.
Tsayuwa ya ɗan yi gefensu tare da cewa.
"Ummi yunwa".
murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Dama yanzu nakeso Aysha taci, sai ta kai maka nakan."
A hankali ya ɗan yi taku biyu zuwa uku, ya kana ya zauna bisa kujerar dake fuskantar tasu.
Ido ya ɗan zuba mata, tare da jingina kansa jikin kujera.
Cike da wani irin mayataccen shauƙi.