Sashe 130
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Hibba kuwa ruwa ta kawo mishi.
Murmushi yayi tare da amsar goran zam-zam ɗin yace.
"Baku shanye tsohon ba Ummi ni gashi na samo sabo".
Hibba ce ta ɗan kalleshi tare da cewa.
"Hamma Jabeer, su Sitti ma sun dawo ne?".
Kai ya gyaɗa mata alamar eh.
Kana ya miƙe tare da cewa.
"Ummi bari inje in ɗan huta".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ai dole kam saida hutu dan gajiya da rashin bacci kam ka kwasosu dole kayi ramuwar bacci".
Ta ƙarishe mgnar tana kollonshi tuni ya shiga corridor'n shiga cikin falonshi.
Dama kuma tuni ita da kanta ta kai mishi abinci a Dinning table ɗinshi.
Nan sukaci gaba da hira.
Hibba na cewa.
"Umaymah na ta dawo na kusa komawa".
Cikin taɓe fuska Jalal ya kalleta a fakaice.
Jamil kuwa dariya yayi tare da cewa.
"Za dai ki gudu yarinya faɗi gskyarki".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Ba wani tsoro ai na gaya mata ta kontar da hankalinta."
Jafar kuwa karatunshi yakeyi.
A hankali saɓanin baya da in zai karatun da ɗan ƙarfi yakeyi.
Sosai suka ɗan yi hira kana suka watse kowa ya tafi makoncinsa.
Shi kuwa Sheykh yana shiga.
Ya rinƙa sauƙe numfashin gajiya tare da rage kayan jikinshi.
Wonka ya shiga yayi kana yasa wasu riga da wondo masu taushi yazo ya konta.
Ba tare da yasha ko ruwaba, sabida tarin gajiya da bacci.
Gaba ɗaya wunin yau a zaune yayi yishi ko a ɗan tsaye.
Gashi rabonsa da bacci tun jiya da safe da ya ɗanyi kaɗan kafin ya tafi harami sallan walaha.
Yana konciya kuwa yayi addu'o'in ya shafa jikinsa.
Kana ya fuskanci allon majigi dake liƙe a bongon ɗakin wanda yake ɗauke da full ƙura'an. Karatu ya farayi daga ƙasa zuwa sama wato nasi.
Ɗaga nan bacci yayi awon gaba dashi ko inna'alzzan bai jeba.
Ummi da Hibba kuwa suna isa falon Shatu cikin kula Ummi tace.
"Kije ku kwana kinji ko Hibba babu abinda zai sameki,
Bazata miki komaiba, bata da lfy bai dace mu barta ita ɗaya ba".
Cikin sanyi Hibba tace.
"Gsky Ummi bazan iyaba wlh ina tsoro".
Cikin hikima Ummi tace.
"To muje ki hau gado ku kwanta ni kuma sai in kwanta a ƙasa kam carpet ɗin.
Gyada tayi cikin gamsuwa da hakan.
Haka sukayi Ummi ta kwanta a ƙasa ita kuma Hibba ta konta gefenta a ɗan tsorace.
Ita kam Shatu batama san sunayi ba, domin bacci mai nauyi takeyi.
Haka dai Ummi tai shiru saida ta tabbatar Hibba tayi bacci kana ta koma ɗakinta.
Washe gari da safe bayan Ummi, Saratu, da Hibba sun gama karyawa ne.
Shatu da tunda tai sallan asuba ta koma ta konta kan sallayar sai yanzu ta fito.
Tayi wonkanta fes ta ƙenƙesa ado da kolliyar ta ba irin mai ramɓatsau ɗin nan ba.
Komai dai-dai tayi abunta.
Riga da siket ne na Mateyal mai taushin gaske, White Coffee mai kyau.
sai ɗan ƙaramin gyale ta yafa a kanta, cikin nitsuwa ta fito.
A falo ta zauna tare da juyowa ta kalli Ummi dake shirya abinci a Dinning table.
"Ina kwana Ummi".
Tace cikin muryarta Normal.
Cikin kulawa Ummi ta juyo tare da cewa.
"Lafiya lau Shatu. Kin taso kenan".
Murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"Ummi meyasa baki tadani ba, kika shiga kitchen da kanki".
Kai ta jinjina tare da ɗaukan cup mai ɗan girma,
Tea mai kauri ta haɗa a ciki kana,
ta taho inda take miƙa mata cup ɗin tayi tare da cewa.
"Gashi amshi kisha, aiki kam ai saida lfy".
Amsa tayi tana murmushi a hankali tace.
"Lfyata lau ai Ummi kawai dai baccin ne ban san meyasa nake ta yinshi ba".
Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata,
Kana ta juyo tace.
"Hibba kawo mana namu abincin nan muci.
Najiyo Muryar Jamil suna zuwa, kuwa wata ƙil dasu Imran zasu zo".
To tace kana ta ɗauko musu nasu Foodflaks ɗin da plate and spoons da ta kawo musu.
Jolof ɗin taliyace da kifin banɗa dasu Kabeji da karas da green beans da dai sauran kayan haɗin.
Sai kuma, ferfesun kayan ciki.
A plate ɗaya Hibba tasa musu, da ita kana ta sawa Ummi.
Kana tasa musu fork, tare da cewa.
"Bismillah Aunty Shatu sauƙo muci ko".
To tace kana ta sauƙo,
suka fara cin abincin.
Amman ina tayi loma ɗaya sai ta kusan 4 minute bata kuma sawa a bakiba.
Sai dai ta shanye tea ɗin ganin hakane yasa Ummi ta ƙara haɗa mata wani shayin.
Shima ta shanye abinta fes, taliyar kuma baifi cokali biyar ba tayi.
Su Jalal kuwa suna shiga suka wuce Dinning area suma sukayi breakfast ɗin kana suka fita, sabida hidimomin salla. Domin yau za'ayi hawan daba, Jalal kuma mayene mai zaman kanshi a kan sarrafa, doki, ɗan daga Affan sai shi.
Bayan Sheykh a iya sarrafa doki kab Masarautar Joɗa .
Amman shi Sheykh ya daɗe da cewa shi ya girma da yin wannan sakarcin.
Su Ummi kuwa, kitchen Suka kuma shiga.
Sanin yau tabbas akwai baƙi masu ɗimbin yawa da masarautar Joɗa zata amshi baƙoncinsu.
Domun ƙananan sarakunan wasu garuruwanma duk zasu zo da tawagar su.
Haka yasa suka shiryawa taron haiƙan ƙadaran ko wani Side dake gidan za'ayi abinci a ciccika manyan kuloli a kai fadar Lamiɗo, wani a kai sashin bayi.
Kana kuma ko wani Side da baƙin su.
Haka yasa su Ummi da Saratu da Larai zagewa.
Sukayi abinci kala-kala kana suka ciccika kulolin aka kai fada akai wurin bayi.
Sannan sukayi nasu kuma suka sassaka a Foodflaks masu ɗan karen kyau suka jera a Dinning table,
tare da plate, spoons, and forks. Kana sun cika Fridge kuma da drinks kala-kala.
Sun kuma yi Pepper Checken mai zafi na zabbi.
Sai kusan ƙarfe ɗaya suka gama komai,
Su Saratu suka kimtsa komai kana suka tafi.
Su kuma duk suka shiga ɗaki da nufin yin wonka.
Tuni zuwa lokacin Masarautar Joɗa ta fara ɗinkewa da baƙi tako wani sashin.
Sheykh Jabeer kuwa, tunda ya tashi.
Ya nufi cikin Garden ɗin nan da ababen tarihin masarautar Joɗa yake.
Zazzagayawa yakeyi yana dubawa, dan tabbatar da babu wani abun da zai cutar da wani ko wata.
Sabida yasan yau manyan baƙi zasu shigo ciki.
A nuna musu ababen tarihi da dai sauransu.
Gefen da curin da macijiyar nan yake ya nufa.
Ya dudduba ƙofofin ba hayaƙi ba komai.
Sai dai in mutun ya kasa kunne zaiji sautin numfashin macijiyar ka da ƴan ƙanana kuka irin na ƙananan macizai.
A hankali ya ƙara matsowa bakin curin. Cikin nitsuwa yayi gyaran murya.
sai kuma yaji sautin kukansu da kuma numfashin uwar ya ƙaru sosai.
A hankali yace.
"Assalamu alaikum, ya ke wannan halittar Ubangijin sammai da ƙasai".
Gyara tsayuwarshi yayi jin numfashin na ƙara matsowa.
A hankali yace.
"Ba cewa nayi ki fitoba, nazo in roƙeki ne kamar yadda Manzon Allah ya sanar mana, dukkan halitta tanaji.
Kuma ina kaga wani abun cutarwa a gidanka ka haɗashi da Allah da Manzonsa kace ya fita.
Manzon Allah ya bamu tabbacin.
Muddin ba mai cutarwa bane zai fita.
In yaƙi fita kuwa ka kasheshi".
Ɗan zagaitawa yayi jin kukansu ya kuma tsananta, cikin sanyi yace.
"Ni bazan roƙeku kan ku fita ku bar muhallin zamanku da ban san tsawon shekara nawa kuke rayuwa a wurinba.
Kuma bansan dalilin zamanku a wurinba.
Shiyasa bazance ku bar Masarautar Joɗa ba.
Kuma bazan kasheku ba,
Sai dai roƙana garemu.
Munada baƙi a Masarautar Joɗa kuma yau zasu shigo, dan Allah da Manzonsa, kada ku fito ku baiyana kanku ga baƙinmu kada ku razana mana baƙi kada ku cutar mana da mutanenmu.
Kuyi zamanku a muhallin ku".
Shiru sukayi tsit alamun sun jishi kuma sun gamsu".
Fahimtar hakane yasashi cewa.
"Na barku lfy".
Yana faɗin haka ya juya, Lamiɗo da Galadima ya gani tsaye a bayanshi.
Murmushi sukayi tare da matsowa inda suke.
Galadima ne yace.
"Kada ka damu da fitarshi da zamanshi da yaranshi
Domin kai ke ganinshi a nan, amman duk in da wani mugu ya shigo masarautar Joɗa da nufin yiwa Lamiɗo wani abun zai ganta da yaranta a gabanshi.
Murmushi yayi tare da amsar goran zam-zam ɗin yace.
"Baku shanye tsohon ba Ummi ni gashi na samo sabo".
Hibba ce ta ɗan kalleshi tare da cewa.
"Hamma Jabeer, su Sitti ma sun dawo ne?".
Kai ya gyaɗa mata alamar eh.
Kana ya miƙe tare da cewa.
"Ummi bari inje in ɗan huta".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ai dole kam saida hutu dan gajiya da rashin bacci kam ka kwasosu dole kayi ramuwar bacci".
Ta ƙarishe mgnar tana kollonshi tuni ya shiga corridor'n shiga cikin falonshi.
Dama kuma tuni ita da kanta ta kai mishi abinci a Dinning table ɗinshi.
Nan sukaci gaba da hira.
Hibba na cewa.
"Umaymah na ta dawo na kusa komawa".
Cikin taɓe fuska Jalal ya kalleta a fakaice.
Jamil kuwa dariya yayi tare da cewa.
"Za dai ki gudu yarinya faɗi gskyarki".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Ba wani tsoro ai na gaya mata ta kontar da hankalinta."
Jafar kuwa karatunshi yakeyi.
A hankali saɓanin baya da in zai karatun da ɗan ƙarfi yakeyi.
Sosai suka ɗan yi hira kana suka watse kowa ya tafi makoncinsa.
Shi kuwa Sheykh yana shiga.
Ya rinƙa sauƙe numfashin gajiya tare da rage kayan jikinshi.
Wonka ya shiga yayi kana yasa wasu riga da wondo masu taushi yazo ya konta.
Ba tare da yasha ko ruwaba, sabida tarin gajiya da bacci.
Gaba ɗaya wunin yau a zaune yayi yishi ko a ɗan tsaye.
Gashi rabonsa da bacci tun jiya da safe da ya ɗanyi kaɗan kafin ya tafi harami sallan walaha.
Yana konciya kuwa yayi addu'o'in ya shafa jikinsa.
Kana ya fuskanci allon majigi dake liƙe a bongon ɗakin wanda yake ɗauke da full ƙura'an. Karatu ya farayi daga ƙasa zuwa sama wato nasi.
Ɗaga nan bacci yayi awon gaba dashi ko inna'alzzan bai jeba.
Ummi da Hibba kuwa suna isa falon Shatu cikin kula Ummi tace.
"Kije ku kwana kinji ko Hibba babu abinda zai sameki,
Bazata miki komaiba, bata da lfy bai dace mu barta ita ɗaya ba".
Cikin sanyi Hibba tace.
"Gsky Ummi bazan iyaba wlh ina tsoro".
Cikin hikima Ummi tace.
"To muje ki hau gado ku kwanta ni kuma sai in kwanta a ƙasa kam carpet ɗin.
Gyada tayi cikin gamsuwa da hakan.
Haka sukayi Ummi ta kwanta a ƙasa ita kuma Hibba ta konta gefenta a ɗan tsorace.
Ita kam Shatu batama san sunayi ba, domin bacci mai nauyi takeyi.
Haka dai Ummi tai shiru saida ta tabbatar Hibba tayi bacci kana ta koma ɗakinta.
Washe gari da safe bayan Ummi, Saratu, da Hibba sun gama karyawa ne.
Shatu da tunda tai sallan asuba ta koma ta konta kan sallayar sai yanzu ta fito.
Tayi wonkanta fes ta ƙenƙesa ado da kolliyar ta ba irin mai ramɓatsau ɗin nan ba.
Komai dai-dai tayi abunta.
Riga da siket ne na Mateyal mai taushin gaske, White Coffee mai kyau.
sai ɗan ƙaramin gyale ta yafa a kanta, cikin nitsuwa ta fito.
A falo ta zauna tare da juyowa ta kalli Ummi dake shirya abinci a Dinning table.
"Ina kwana Ummi".
Tace cikin muryarta Normal.
Cikin kulawa Ummi ta juyo tare da cewa.
"Lafiya lau Shatu. Kin taso kenan".
Murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"Ummi meyasa baki tadani ba, kika shiga kitchen da kanki".
Kai ta jinjina tare da ɗaukan cup mai ɗan girma,
Tea mai kauri ta haɗa a ciki kana,
ta taho inda take miƙa mata cup ɗin tayi tare da cewa.
"Gashi amshi kisha, aiki kam ai saida lfy".
Amsa tayi tana murmushi a hankali tace.
"Lfyata lau ai Ummi kawai dai baccin ne ban san meyasa nake ta yinshi ba".
Kai kawai Ummi ta gyaɗa mata,
Kana ta juyo tace.
"Hibba kawo mana namu abincin nan muci.
Najiyo Muryar Jamil suna zuwa, kuwa wata ƙil dasu Imran zasu zo".
To tace kana ta ɗauko musu nasu Foodflaks ɗin da plate and spoons da ta kawo musu.
Jolof ɗin taliyace da kifin banɗa dasu Kabeji da karas da green beans da dai sauran kayan haɗin.
Sai kuma, ferfesun kayan ciki.
A plate ɗaya Hibba tasa musu, da ita kana ta sawa Ummi.
Kana tasa musu fork, tare da cewa.
"Bismillah Aunty Shatu sauƙo muci ko".
To tace kana ta sauƙo,
suka fara cin abincin.
Amman ina tayi loma ɗaya sai ta kusan 4 minute bata kuma sawa a bakiba.
Sai dai ta shanye tea ɗin ganin hakane yasa Ummi ta ƙara haɗa mata wani shayin.
Shima ta shanye abinta fes, taliyar kuma baifi cokali biyar ba tayi.
Su Jalal kuwa suna shiga suka wuce Dinning area suma sukayi breakfast ɗin kana suka fita, sabida hidimomin salla. Domin yau za'ayi hawan daba, Jalal kuma mayene mai zaman kanshi a kan sarrafa, doki, ɗan daga Affan sai shi.
Bayan Sheykh a iya sarrafa doki kab Masarautar Joɗa .
Amman shi Sheykh ya daɗe da cewa shi ya girma da yin wannan sakarcin.
Su Ummi kuwa, kitchen Suka kuma shiga.
Sanin yau tabbas akwai baƙi masu ɗimbin yawa da masarautar Joɗa zata amshi baƙoncinsu.
Domun ƙananan sarakunan wasu garuruwanma duk zasu zo da tawagar su.
Haka yasa suka shiryawa taron haiƙan ƙadaran ko wani Side dake gidan za'ayi abinci a ciccika manyan kuloli a kai fadar Lamiɗo, wani a kai sashin bayi.
Kana kuma ko wani Side da baƙin su.
Haka yasa su Ummi da Saratu da Larai zagewa.
Sukayi abinci kala-kala kana suka ciccika kulolin aka kai fada akai wurin bayi.
Sannan sukayi nasu kuma suka sassaka a Foodflaks masu ɗan karen kyau suka jera a Dinning table,
tare da plate, spoons, and forks. Kana sun cika Fridge kuma da drinks kala-kala.
Sun kuma yi Pepper Checken mai zafi na zabbi.
Sai kusan ƙarfe ɗaya suka gama komai,
Su Saratu suka kimtsa komai kana suka tafi.
Su kuma duk suka shiga ɗaki da nufin yin wonka.
Tuni zuwa lokacin Masarautar Joɗa ta fara ɗinkewa da baƙi tako wani sashin.
Sheykh Jabeer kuwa, tunda ya tashi.
Ya nufi cikin Garden ɗin nan da ababen tarihin masarautar Joɗa yake.
Zazzagayawa yakeyi yana dubawa, dan tabbatar da babu wani abun da zai cutar da wani ko wata.
Sabida yasan yau manyan baƙi zasu shigo ciki.
A nuna musu ababen tarihi da dai sauransu.
Gefen da curin da macijiyar nan yake ya nufa.
Ya dudduba ƙofofin ba hayaƙi ba komai.
Sai dai in mutun ya kasa kunne zaiji sautin numfashin macijiyar ka da ƴan ƙanana kuka irin na ƙananan macizai.
A hankali ya ƙara matsowa bakin curin. Cikin nitsuwa yayi gyaran murya.
sai kuma yaji sautin kukansu da kuma numfashin uwar ya ƙaru sosai.
A hankali yace.
"Assalamu alaikum, ya ke wannan halittar Ubangijin sammai da ƙasai".
Gyara tsayuwarshi yayi jin numfashin na ƙara matsowa.
A hankali yace.
"Ba cewa nayi ki fitoba, nazo in roƙeki ne kamar yadda Manzon Allah ya sanar mana, dukkan halitta tanaji.
Kuma ina kaga wani abun cutarwa a gidanka ka haɗashi da Allah da Manzonsa kace ya fita.
Manzon Allah ya bamu tabbacin.
Muddin ba mai cutarwa bane zai fita.
In yaƙi fita kuwa ka kasheshi".
Ɗan zagaitawa yayi jin kukansu ya kuma tsananta, cikin sanyi yace.
"Ni bazan roƙeku kan ku fita ku bar muhallin zamanku da ban san tsawon shekara nawa kuke rayuwa a wurinba.
Kuma bansan dalilin zamanku a wurinba.
Shiyasa bazance ku bar Masarautar Joɗa ba.
Kuma bazan kasheku ba,
Sai dai roƙana garemu.
Munada baƙi a Masarautar Joɗa kuma yau zasu shigo, dan Allah da Manzonsa, kada ku fito ku baiyana kanku ga baƙinmu kada ku razana mana baƙi kada ku cutar mana da mutanenmu.
Kuyi zamanku a muhallin ku".
Shiru sukayi tsit alamun sun jishi kuma sun gamsu".
Fahimtar hakane yasashi cewa.
"Na barku lfy".
Yana faɗin haka ya juya, Lamiɗo da Galadima ya gani tsaye a bayanshi.
Murmushi sukayi tare da matsowa inda suke.
Galadima ne yace.
"Kada ka damu da fitarshi da zamanshi da yaranshi
Domin kai ke ganinshi a nan, amman duk in da wani mugu ya shigo masarautar Joɗa da nufin yiwa Lamiɗo wani abun zai ganta da yaranta a gabanshi.