Sashe 20
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Suna fita suka sameshi zaune bisa dakalin ƙofar gidan nasu.
Da sauri Junainah ta isa gareshi tare da cewa.
"Oyoyo yaya Salmanu".
Ajiye kwanon tayi a gefenshi.
Da sauri yasa hannunshin suka tafa da hannunta data miƙa mishi, cikin sakin fuska da nitsuwa yace.
"I miss you ƙanwali".
Dariya mai ɗan sauti tayi tare da cewa.
"Miss you too my dear".
Dariya mai sauti sukayi a tare cikin jin daɗi wanda aka kira da Salmanu ya lakace hancin Junainah tare da cewa.
"Alhamdulillah alama ta nuna ƙanwaliya tana zuwa makaranta babu wasa".
Cikin jin daɗi tace.
"Sosai ma ya Salmanu yanzu ajiyana huɗu fa, yanzuma dan hutu mukeyi, kuma gashi ko a gidama Ina karatu".
Jinjina mata yayi da hannunshi kana, ya jawo kwanan data ajiye tare da cewa.
"Ƙanwaliya me kika kawo mim ne?".
Cikin murmushi tace.
"Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na Addana".
Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida.
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren,
Cikin sanyi yace.
"Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kin rama kena".
Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace.
"Ga wuri kizo ki zauna mana".
A hankali tace,
"A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana".
"Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?".
Salmanu ya faɗa a hankali.
Da sauri tace.
"Eh".
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
"Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?".
A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi.
Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace.
"Gaya min me kike tsoro?".
Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai".
Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace.
"Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba".
Da sauri tace.
"Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi".
Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace.
"Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon".
Cikin yanayin nitsuwarta tace.
"A a kaci kawai Ya Salmanu".
Da sauri yace.
"No kada kimin musu".
Shiru tayi jin yaci gaba da cewa.
"Muddin dai ina raye in sha Allah.
wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki".
Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu.
A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna ɗan hirarsu
Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai.
Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa.
"Ummey".
"Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru,
Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace.
"Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?".
Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace.
"Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?".
Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa.
"To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi".
Kai ta juya tare da cewa.
"Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko".
Murmushi Ummey tayi kana tace.
"Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki".
da haka suka konta bacci.
Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai,
Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta.
Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu.
Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma.
To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu.
Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba.
Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki shiyasa tun yana ƙaraminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi. Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani ɗin.
A can ƙasa mai tsarki kuwa,
Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana uku da zuwa suka tafi, Madina,
Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki Jalaluddin, shi kuma yaje har Ɓadamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi ɗaurin auren.
To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka.
Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal.
Kullum yakan kira Juwairiyya.
Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce.
Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh Abdulkareem domin yana tare da manyan baƙi.
Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti.
Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan jin daɗin rayuwar duniya,
Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah suna gefenta, cikin shiga ta al'farma,
Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim ɗin sukeyiwa tausa.
Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da danƙawa-ɗanƙwal dajaja sai sauran abincinsu na larabawa.
Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna ɗan taɓa hira.
Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya ɗan juya ya kalli wayar ba tare daya juya kanshiba,
Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar,
da sauri ya ɗauko wayar ya miƙa mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran.
Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace.
"Barka da dare Hajia Mama".
A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare da cewa.
"Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane".
Idonshi ya ɗan ɗago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace.
"Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal".
Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata muzurai".
Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace.
"Hajia Mama kiyi musu faɗa kice su barifa sun girma".
Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa.
"Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma".
Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa.
"Ina Sitti na?". A taƙaice yace.
"Gata nan kusa dani".
Cikin yanayin jin daɗi tace.
"Bata waya". To yace kana ya miƙa Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa.
"(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ƙara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace, kana suka gaisa cikin tsananin jin daɗi.
Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake kishinƙiɗe ya lumshe ido a hankali tace.
"Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka ɗaki ɗaki, da bai gankaba yaƙi fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu.
Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo mishi,
Haka Jazrah da Jannart,
Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace.
"Lamiɗo ya gaya min ɗazu da mukayi waya".
Shiru sukayi baki ɗayansu, a hankali Haroon ya miƙe kwance tare da faɗawa nazari mai zurfi.
Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar musu hankali kafin, sukayi sallama da juna.
Da sauri Junainah ta isa gareshi tare da cewa.
"Oyoyo yaya Salmanu".
Ajiye kwanon tayi a gefenshi.
Da sauri yasa hannunshin suka tafa da hannunta data miƙa mishi, cikin sakin fuska da nitsuwa yace.
"I miss you ƙanwali".
Dariya mai ɗan sauti tayi tare da cewa.
"Miss you too my dear".
Dariya mai sauti sukayi a tare cikin jin daɗi wanda aka kira da Salmanu ya lakace hancin Junainah tare da cewa.
"Alhamdulillah alama ta nuna ƙanwaliya tana zuwa makaranta babu wasa".
Cikin jin daɗi tace.
"Sosai ma ya Salmanu yanzu ajiyana huɗu fa, yanzuma dan hutu mukeyi, kuma gashi ko a gidama Ina karatu".
Jinjina mata yayi da hannunshi kana, ya jawo kwanan data ajiye tare da cewa.
"Ƙanwaliya me kika kawo mim ne?".
Cikin murmushi tace.
"Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na Addana".
Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida.
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren,
Cikin sanyi yace.
"Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kin rama kena".
Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace.
"Ga wuri kizo ki zauna mana".
A hankali tace,
"A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana".
"Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?".
Salmanu ya faɗa a hankali.
Da sauri tace.
"Eh".
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
"Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?".
A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi.
Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace.
"Gaya min me kike tsoro?".
Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana son abinda zai cutar da kai".
Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace.
"Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin baki cancanci zama matar mushurkiba".
Da sauri tace.
"Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare mgnar ta koma kunnenshi".
Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace.
"Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon".
Cikin yanayin nitsuwarta tace.
"A a kaci kawai Ya Salmanu".
Da sauri yace.
"No kada kimin musu".
Shiru tayi jin yaci gaba da cewa.
"Muddin dai ina raye in sha Allah.
wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki".
Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu.
A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da budurwarshi suna ɗan hirarsu
Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin komai.
Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa.
"Ummey".
"Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba mata,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru,
Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace.
"Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?".
Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace.
"Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?".
Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa.
"To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi".
Kai ta juya tare da cewa.
"Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko".
Murmushi Ummey tayi kana tace.
"Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki".
da haka suka konta bacci.
Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu, dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai,
Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta.
Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake, gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu.
Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma.
To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da al'barkasu a jikinsu.
Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba.
Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki shiyasa tun yana ƙaraminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi. Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani ɗin.
A can ƙasa mai tsarki kuwa,
Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana uku da zuwa suka tafi, Madina,
Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki Jalaluddin, shi kuma yaje har Ɓadamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi ɗaurin auren.
To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka.
Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal.
Kullum yakan kira Juwairiyya.
Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce.
Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh Abdulkareem domin yana tare da manyan baƙi.
Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti.
Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan jin daɗin rayuwar duniya,
Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah suna gefenta, cikin shiga ta al'farma,
Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim ɗin sukeyiwa tausa.
Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da danƙawa-ɗanƙwal dajaja sai sauran abincinsu na larabawa.
Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna ɗan taɓa hira.
Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya ɗan juya ya kalli wayar ba tare daya juya kanshiba,
Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar,
da sauri ya ɗauko wayar ya miƙa mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran.
Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace.
"Barka da dare Hajia Mama".
A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare da cewa.
"Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane".
Idonshi ya ɗan ɗago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace.
"Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal".
Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata muzurai".
Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace.
"Hajia Mama kiyi musu faɗa kice su barifa sun girma".
Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa.
"Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma".
Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa.
"Ina Sitti na?". A taƙaice yace.
"Gata nan kusa dani".
Cikin yanayin jin daɗi tace.
"Bata waya". To yace kana ya miƙa Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa.
"(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ƙara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace, kana suka gaisa cikin tsananin jin daɗi.
Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake kishinƙiɗe ya lumshe ido a hankali tace.
"Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka ɗaki ɗaki, da bai gankaba yaƙi fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu.
Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo mishi,
Haka Jazrah da Jannart,
Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace.
"Lamiɗo ya gaya min ɗazu da mukayi waya".
Shiru sukayi baki ɗayansu, a hankali Haroon ya miƙe kwance tare da faɗawa nazari mai zurfi.
Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar musu hankali kafin, sukayi sallama da juna.