Sashe 60
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Suna cike a falon a ƙalla sun kai su bakwai dukansu. Manyan mutanene masu tarin wadatar duniya, jinin sarauta na yawo a jikinsu.
Suna zaune kamar yadda kullum suke zama, suna ɗan hira a tsakaninsu.
Habibullah ne, zaune a can tsakiyarsu a matsayinsa na shine babban ɗa ga Lamiɗo, hannunsa riƙe da.
Carɓi, sai gefen damansa, Alhaji Sani, sai kuma Barrister Kamal, kana sai. Dr Aliyu, kana sai, Badamasi, Nasiru, basiru.
Dr Aliyu ne, ke gefen daman Habibullah, bisa alamu duk mgna yakeyi mishi a kan lfyarsa.
Bappa Nasiru, wanda shine, yake bin Habibullah a girma sai dai uwarsu ba ɗaya ba, gyara zama yayi tare da jan dogon tsakin da yasa duk suka meda idonsu kanshi.
Cikin kula Habibullah yace.
"Lfy dai Nasiru?."
Wani irin kallo mara daɗin gani ya watsa mishi tare da cewa.
"Yes lfy lau, sai dai mu nan duk muna da aiki, ba zauna gari banza, irinka bane, kowa yanada hidimar yi gashi har yanzu,
Lamiɗo bai fitoba".
Murmushi yayi ba tare da yaji ciwon abinda ya gaya mishibs, a hankali yace.
"To Nasiru, ai duk saurinka kayi haƙuri dai ya fito, kaga lfyarsa yaga taka, tunda shi bai gajiya da bincikar lfyarmuba, ai muku wa bazamu gazaba.
Domin abune mai wucewa".
Wani irin kallo mai cike da tsana da tsoggoma ya mishi tare da kauda kanshi.
Basiru ne yayi dariya alamar jin daɗin kallon da ɗan uwanshi yayiwa Babban yayansu da suke ƴan uba.
shi kuwa Habibullah Abbansu Sheykh, kauda kai yayi kar bai ganiba.
Kusan a tare suka miƙe gaba ɗayansu,
tare da haɗa baki wurin cewa.
"Barka da fitowa, Mai alfarma Lamiɗon Joɗa."
Murmushi yayi tare da kallon ƴaƴan nashi ɗaya bayan ɗaya, a hankali ya ƙarasa fitowa, hannunshi sarƙafe da hannun Jabeer.
Wanda baiyanarsa yasa, gaba ɗaya suka zazzaro ido. Cikin tarin mamaki, al'ajabi, firgici, kaɗuwa, gamida tsayawar idanunsu kan ɗan babban yayan nasu, cikin wani irin daskarewa, suka juyo suka fuskaci, junansu wannan ya kalli Wannan wannan ya kalli wancan.
Murya a daburce, Nasiru ya nuna Jabeer dake tsaye, cikin wani masifeffen al'kyabbar mai masifar kyau da zadan gaske, cikin ƙafewan yawun baki yace.
"Ka gafarceni Lamiɗo, me idonuna ke gani, daga ina ka fito da Jabeer? Me kayi dashi? Meye ma'anar hakan? Mu duk ƴaƴan ka bamu kai ka shiga damu ba sai shi?".
Cikin tsare fuska irin ta manyan sarakai dattawan,
ya zubawa, Nasiru idanu, wanda dole tasa ya hadiye rahowar maganar tasa.
Habibullah kuwa, wani irin rawa da karkarwa jikinsa ya fara.
Wani masifeffen tsoro da fargabane ya rufeshi akan ɗan nashi, koda dai baya jinsu a ranshi kamar sauran ƴaƴanshi, hakan bai hanashi tsoro da fargabar abinda zai cutar dasuba. Barrister Kamal kuwa.
Wata irinyar madifeffiyar zuface ta keto mishi daga saman kanshi har tsakiyar tafin sawunshi.
Lokaci ɗaya yaji wani irin abu ya saki ƙahon zuciyarshi,
Maƙoƙoronshi ya bushe ƙamas,
duhun daya rufe mishi idone yasashi komawa zaune.
Dr Aliyu kuwa, wani irin murmushi yakeyi yana kallon ɗan babban wansun.
Shi kuwa Lamiɗo hannun Jabeer ya kuma ja, wanda yake motsa laɓɓansa a hankali yana tasbihi kamar yadda ya saba.
Zama yayi kujerarsa ta musamman, kana Jabeer kuwa ya zauna gabanshi.
Cikin tattaro yawun baki Barrister Kamal yace.
"Barka da safiya. Sarkin Joɗo.
Sai ya kuma danne tarin baƙin cikinsa yayi mishi rumfa da fuskarsa ta zahiri kana ya kalli Jabeer da ya ɗan sunkuyar da kanshi tare da gaidashi.
Cikin dakiya yace.
"Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Joɗa.
Yaushe a gari".
Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa.
"Daren jiya".
Nasiru ne ya katsesu da cewa.
"Lamiɗo, ɗakin sarautar sarakunan Joɗa kuma ya zama kowa zai iya shigane?".
Bai kulashi ba, har saida suka gaisa gaba ɗayansu, kana, ya fuskancesu, duka cikin hikima da, kaifin basira yace.
"Rigar sarautarsu ta GARKUWAN FULANI, na bashi.
Sabida akwai tafiyar gaggawa da zamuyi zuwa, Rugar Bani, da ƙaɓilun wurin suka far musu da kisa."
Kai suka gyaɗa alamun gamsuwa, kana duk, ya sallamesu.
Duk suka fita kowa da abinda ke cikin ransa, da zuciyarsa.
Bayan fitansu ne ya kalli Jabeer cikin, tarin kula yace.
"Kaje ka shirya kazo mu tafi".
Kanshi ya kuma rusunarwa cikin ladab yace.
"Allah saine, mu bari sai bayan sallan, jumma'a ina munyi jam'i anan, mu tafi gudun kada muje bamu dawoba kafin lokacin sallan."
Gyara zamanshi yayi tare da gyaɗa kai kana yace.
"Haƙƙun kayi, gsky to mu bari sai an sauƙo mutafi, in yaso muyi sallan la'asar a can."
Da Wannan shawarar suka bari sai bayan sallan, azahar ɗin su tafi.
Sun daɗe suna tattaunawa kafin, ya sallameshi ya tafi, shi kuma ya nufi fada.
A falonshi kuwa, yana shigowa duk suka zuba mishi ido, da mamaki cikin zaƙuwa Jamil yace.
"Hamma Jabeer wai ta ina kabi ka fitane? Duk bamuga fitankaba".
Kanshi ya mirgina, alamun gajiya, kana a fakaice ya kallesu baki ɗayansu, tare da cewa.
"Sama".
Murmushi sukayi baki ɗayansu, sabida fahimtar amsar daya basu, na nuni basuga sanda ya fita bane.
Suna zaune kamar yadda kullum suke zama, suna ɗan hira a tsakaninsu.
Habibullah ne, zaune a can tsakiyarsu a matsayinsa na shine babban ɗa ga Lamiɗo, hannunsa riƙe da.
Carɓi, sai gefen damansa, Alhaji Sani, sai kuma Barrister Kamal, kana sai. Dr Aliyu, kana sai, Badamasi, Nasiru, basiru.
Dr Aliyu ne, ke gefen daman Habibullah, bisa alamu duk mgna yakeyi mishi a kan lfyarsa.
Bappa Nasiru, wanda shine, yake bin Habibullah a girma sai dai uwarsu ba ɗaya ba, gyara zama yayi tare da jan dogon tsakin da yasa duk suka meda idonsu kanshi.
Cikin kula Habibullah yace.
"Lfy dai Nasiru?."
Wani irin kallo mara daɗin gani ya watsa mishi tare da cewa.
"Yes lfy lau, sai dai mu nan duk muna da aiki, ba zauna gari banza, irinka bane, kowa yanada hidimar yi gashi har yanzu,
Lamiɗo bai fitoba".
Murmushi yayi ba tare da yaji ciwon abinda ya gaya mishibs, a hankali yace.
"To Nasiru, ai duk saurinka kayi haƙuri dai ya fito, kaga lfyarsa yaga taka, tunda shi bai gajiya da bincikar lfyarmuba, ai muku wa bazamu gazaba.
Domin abune mai wucewa".
Wani irin kallo mai cike da tsana da tsoggoma ya mishi tare da kauda kanshi.
Basiru ne yayi dariya alamar jin daɗin kallon da ɗan uwanshi yayiwa Babban yayansu da suke ƴan uba.
shi kuwa Habibullah Abbansu Sheykh, kauda kai yayi kar bai ganiba.
Kusan a tare suka miƙe gaba ɗayansu,
tare da haɗa baki wurin cewa.
"Barka da fitowa, Mai alfarma Lamiɗon Joɗa."
Murmushi yayi tare da kallon ƴaƴan nashi ɗaya bayan ɗaya, a hankali ya ƙarasa fitowa, hannunshi sarƙafe da hannun Jabeer.
Wanda baiyanarsa yasa, gaba ɗaya suka zazzaro ido. Cikin tarin mamaki, al'ajabi, firgici, kaɗuwa, gamida tsayawar idanunsu kan ɗan babban yayan nasu, cikin wani irin daskarewa, suka juyo suka fuskaci, junansu wannan ya kalli Wannan wannan ya kalli wancan.
Murya a daburce, Nasiru ya nuna Jabeer dake tsaye, cikin wani masifeffen al'kyabbar mai masifar kyau da zadan gaske, cikin ƙafewan yawun baki yace.
"Ka gafarceni Lamiɗo, me idonuna ke gani, daga ina ka fito da Jabeer? Me kayi dashi? Meye ma'anar hakan? Mu duk ƴaƴan ka bamu kai ka shiga damu ba sai shi?".
Cikin tsare fuska irin ta manyan sarakai dattawan,
ya zubawa, Nasiru idanu, wanda dole tasa ya hadiye rahowar maganar tasa.
Habibullah kuwa, wani irin rawa da karkarwa jikinsa ya fara.
Wani masifeffen tsoro da fargabane ya rufeshi akan ɗan nashi, koda dai baya jinsu a ranshi kamar sauran ƴaƴanshi, hakan bai hanashi tsoro da fargabar abinda zai cutar dasuba. Barrister Kamal kuwa.
Wata irinyar madifeffiyar zuface ta keto mishi daga saman kanshi har tsakiyar tafin sawunshi.
Lokaci ɗaya yaji wani irin abu ya saki ƙahon zuciyarshi,
Maƙoƙoronshi ya bushe ƙamas,
duhun daya rufe mishi idone yasashi komawa zaune.
Dr Aliyu kuwa, wani irin murmushi yakeyi yana kallon ɗan babban wansun.
Shi kuwa Lamiɗo hannun Jabeer ya kuma ja, wanda yake motsa laɓɓansa a hankali yana tasbihi kamar yadda ya saba.
Zama yayi kujerarsa ta musamman, kana Jabeer kuwa ya zauna gabanshi.
Cikin tattaro yawun baki Barrister Kamal yace.
"Barka da safiya. Sarkin Joɗo.
Sai ya kuma danne tarin baƙin cikinsa yayi mishi rumfa da fuskarsa ta zahiri kana ya kalli Jabeer da ya ɗan sunkuyar da kanshi tare da gaidashi.
Cikin dakiya yace.
"Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Joɗa.
Yaushe a gari".
Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa.
"Daren jiya".
Nasiru ne ya katsesu da cewa.
"Lamiɗo, ɗakin sarautar sarakunan Joɗa kuma ya zama kowa zai iya shigane?".
Bai kulashi ba, har saida suka gaisa gaba ɗayansu, kana, ya fuskancesu, duka cikin hikima da, kaifin basira yace.
"Rigar sarautarsu ta GARKUWAN FULANI, na bashi.
Sabida akwai tafiyar gaggawa da zamuyi zuwa, Rugar Bani, da ƙaɓilun wurin suka far musu da kisa."
Kai suka gyaɗa alamun gamsuwa, kana duk, ya sallamesu.
Duk suka fita kowa da abinda ke cikin ransa, da zuciyarsa.
Bayan fitansu ne ya kalli Jabeer cikin, tarin kula yace.
"Kaje ka shirya kazo mu tafi".
Kanshi ya kuma rusunarwa cikin ladab yace.
"Allah saine, mu bari sai bayan sallan, jumma'a ina munyi jam'i anan, mu tafi gudun kada muje bamu dawoba kafin lokacin sallan."
Gyara zamanshi yayi tare da gyaɗa kai kana yace.
"Haƙƙun kayi, gsky to mu bari sai an sauƙo mutafi, in yaso muyi sallan la'asar a can."
Da Wannan shawarar suka bari sai bayan sallan, azahar ɗin su tafi.
Sun daɗe suna tattaunawa kafin, ya sallameshi ya tafi, shi kuma ya nufi fada.
A falonshi kuwa, yana shigowa duk suka zuba mishi ido, da mamaki cikin zaƙuwa Jamil yace.
"Hamma Jabeer wai ta ina kabi ka fitane? Duk bamuga fitankaba".
Kanshi ya mirgina, alamun gajiya, kana a fakaice ya kallesu baki ɗayansu, tare da cewa.
"Sama".
Murmushi sukayi baki ɗayansu, sabida fahimtar amsar daya basu, na nuni basuga sanda ya fita bane.