Sashe 81
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A garin Bani kuwa zuwa yanzu hankali ƙabilar ɓachama yayi matsifar tashi, tsoro mai tsanani ya rufesu.
Tsoron da yasa da yawansu suka rinƙa guduwa suna koma cikin babban birnin Ɓadamaya,
Wasu kuma su tafi wasu jihohin.
Sabida sun gama tsinkewa da goron gaiyata da fulani keta raɓawa babu dare babu rana birni da ƙauye duk inda suka san fulani na nan sai da suka aika musu goro
Wannan ne yasa mafiya yawan kafuran aran na kare.
Inda hakan ya fusata Habban Ɓacama.
Har ta kaishi ga cewa, duk ba ɓacamen da yasan tsoron fulanine ya sashi guduwa to kada ya kuskura ya sake dawo mishi garinshi garin Shikan.
To wannan abun shiyasa wasu suka fasa guduwa, wasu da basuyi nisaba suka dawo.
To kuma kwatsam sai gashi yau an aiko an karɓin sandar sarautar Shikan dake hannunshi
Wannan abun yasa da yawa mutanen cikin Shikan Maza da mata hausa fulani da Ɓacamawa da sauran ƙabilu suka kuma rinƙa fecewa sabida, suna ganin yanzu dai shi kanshi Sarki Shikan bashi da madafa bashi da ƙarfi tunda an karɓe sandar sarautar shi.
To hakane yasa, ya rinka bin ƙauyuka Especially mutanen Bonon da kewaye ya rinƙa zugasu da ingiza su cewa, nanfa garinsu ne ya zasuyi su gudu kan Fulani.
Kuma ma suda sukeda dodon tsafinsu Bonon ai shi kadai ya ishi fulanin.
Da haka yasa duk ƙabilun Ɓacamawa na ƙauyukan basu guduba.
Sunata shirin faɗa yayinda cikin garin Shikan kuma yayi shal ko ina shiru babu mutane.
Cikin garin Bani kuwa, iya tsoronsu da suka gani a cikin kafuran ya sasu jin daɗi tunda gashi har suna guduwa subar garin da suke musu gadara da gori a kanshi da cika bakin sai sun kori Fulani a garuruwansu.
To tabbas sunada nasara akan fansar da zasu ɗauka, zasu ramane dan nemawa kansu enci.
Sun san iya sau ɗaya in sun nunawa arnatakun nan zasu iya gwabzawa dasu zasu barsu su sarara.
Haka yasa suke jin ƙarfin guiwar yin abun.
Ba'ana kuwa yanata ƙara shirya kanshi, sabida ramuwar gasar da za'ayi.
Ya Salmanu kuwa yanzu ya fara jajir cewa, yana fakewa da jarumtar Jabeer yana gasawa Ba'ana maganganu.
Sosai ya ƙara shigewa Shatu a mako ɗayan nan.
Kuma tana jin daɗin hakan.
Ta sake sosai.
Zuwa yanzu kuma jikin Ummey yayi sauƙi garawau sai dai har yau bata taɓa yin mgna ba ta zama tamkar kurma.
Da dare bayan sallan isha'i,
tana zsune ita da ya Salmanu suna hira cikin nitsuwa tace.
"Ya Salmanu gobene zamuje asibiti mu dubo su Junaidu da sauran marasa lfy dake cikin Genaral Hospital Ɓadawaya, dan naji ƙishin-kishin ɗin wai har yanzu babu likitan daya dubasu."
Cikin gamsuwa da hakan yace.
"Eh hakan yana da kyau, kuje in sha Allah muma jibi asabar zamuyi gamgami muje, danma goben jumma'a ne da munje tare".
Sai kuma ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Da yaushe zakuje?".
Cikin sanyi tace.
"Da safe zamuje, in anyi sallan azahar zan dawo, amman Rafi'a zata wuce makaranta".
yace.
"To ke sai yaushe zaki koma?".
"Sai Ummey ta ɗan ƙara samun sauƙi. Ni da na so mu kaita asibiti kan batun rashin mgnar tata.
Gyara zaman shi yayi tare da cewa.
"Wannan ba matsala bace, wlh firgici da tsoro ne yasata hakan".
Haka dai sukaci gaba da hirarsu.
Washe gari ranar jumma'a, misalin karfe sha biyu dai-dai suka fito zasu tafi asibitin.
A bakin lambun garinsu sukayi kiciɓis da Ba'ana nan ya tsaidata dole suka zauna.
A can cikin masarautar Joɗa kuwa,
Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, da Jabeer ne tafe a hankali suka shiga cikin Garden ɗin nan.
Ta gefen Lamiɗo, suna shiga suka nufi inda katon curin dake wurin shekara da shekaru.
Shi dai Jabeer binsu yakeyi baiyi magana ba,
Koda suka isa wurin zama sukayi dabas a ƙasa.
Dole shima ya zauna, cikin sanyi Lamiɗo yace.
"Assalamu alaikum Jaimi".
Da mamaki Jabeer ya kalleshi,
Hiraminshi ya gyara tare da cewa.
"To yau kuma".
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya rufe mishi bakinshi.
Hannunshi yasa ya janye hannun Galadima tare da cewa.
"Yo ai ba sai ka rufe min bakiba, in kace nayi shiruma zanyi, sai dai ina naga abin saɓon Allah ko tsireni za'ayi sai na faɗa".
Dafe kai Galadima yayi tare da tsuke fuskarsa.
Ganin haka ya taɓe baki tare da ɗaga kafaɗunshi ya ɗan buɗasu alamar, ban damuba.
Sarkin Shaɗi kuwa bai kallesu bama.
Wani irin zabura Jabeer yayi cikin tsananin firgici da kaɗuwa lokacin da yaga wani irin h ....!
By
*GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako wacce ƙofa na jikin curin.
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi.
Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga ƙofofin ramin shirgegen curin.
Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune.
Ido ya zuba musu tare da cewa.
"Me hakan?".
Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da cewa.
"Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?".
Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce.
Cikin hatsala Lamiɗo yace.
"Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe bakin nan".
Wani kallo yayi mishi tare da cewa.
"Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah".
Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi.
Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa,
Sai wani irin huci.
Da sauri Jabeer yace.
"Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma'a ace, inada abinda yafi wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan sha biyu."
Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba.
Sabida dama sun san za'ayi haka kam.
Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba.
Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau.
Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi girma.
Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun!."
Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu.
Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi.
Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya razana.
Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai suke firgitashiba.
tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za'ayi mishi ne.
Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta fitowa taƙi ƙarewa.
Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune.
Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine.
A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo,
Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin nan saida suka fito ras kamar an wonkesu.
Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma,
Kamar forko sai ga hayaƙin.
Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa.
"Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za'a jazamin kaji su bini su tsastsageni.
Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah".
Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu,
fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi.
Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana suma duk suka miƙa.
Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin.
Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo,
da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa.
"Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu nan.
Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?".
Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace.
"Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa".
Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita.
Lamiɗo kuwa tuni sun tafi.
Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi.
A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci.
"Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben gargaji.
Wannan wacce iriyar fitinace?".
Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi,
babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan jumma'a ne.
A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi.
Kai tsaye bathroom ya wuce.
Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire,
Cillasu yayi cikin injin wonki.
A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue.
A hankali ya shiga cikin wurin wonkan.
Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma'a anshi.
Bayan ya fitone ya nufi drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin.
Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa, yana tsane ruwan jikinshi.
Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi.
Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare ɗayar ma.
Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya.
Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman kanshi.
Cikin hamzari ya fito bedroom,
Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi. Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi.
Tsoron da yasa da yawansu suka rinƙa guduwa suna koma cikin babban birnin Ɓadamaya,
Wasu kuma su tafi wasu jihohin.
Sabida sun gama tsinkewa da goron gaiyata da fulani keta raɓawa babu dare babu rana birni da ƙauye duk inda suka san fulani na nan sai da suka aika musu goro
Wannan ne yasa mafiya yawan kafuran aran na kare.
Inda hakan ya fusata Habban Ɓacama.
Har ta kaishi ga cewa, duk ba ɓacamen da yasan tsoron fulanine ya sashi guduwa to kada ya kuskura ya sake dawo mishi garinshi garin Shikan.
To wannan abun shiyasa wasu suka fasa guduwa, wasu da basuyi nisaba suka dawo.
To kuma kwatsam sai gashi yau an aiko an karɓin sandar sarautar Shikan dake hannunshi
Wannan abun yasa da yawa mutanen cikin Shikan Maza da mata hausa fulani da Ɓacamawa da sauran ƙabilu suka kuma rinƙa fecewa sabida, suna ganin yanzu dai shi kanshi Sarki Shikan bashi da madafa bashi da ƙarfi tunda an karɓe sandar sarautar shi.
To hakane yasa, ya rinka bin ƙauyuka Especially mutanen Bonon da kewaye ya rinƙa zugasu da ingiza su cewa, nanfa garinsu ne ya zasuyi su gudu kan Fulani.
Kuma ma suda sukeda dodon tsafinsu Bonon ai shi kadai ya ishi fulanin.
Da haka yasa duk ƙabilun Ɓacamawa na ƙauyukan basu guduba.
Sunata shirin faɗa yayinda cikin garin Shikan kuma yayi shal ko ina shiru babu mutane.
Cikin garin Bani kuwa, iya tsoronsu da suka gani a cikin kafuran ya sasu jin daɗi tunda gashi har suna guduwa subar garin da suke musu gadara da gori a kanshi da cika bakin sai sun kori Fulani a garuruwansu.
To tabbas sunada nasara akan fansar da zasu ɗauka, zasu ramane dan nemawa kansu enci.
Sun san iya sau ɗaya in sun nunawa arnatakun nan zasu iya gwabzawa dasu zasu barsu su sarara.
Haka yasa suke jin ƙarfin guiwar yin abun.
Ba'ana kuwa yanata ƙara shirya kanshi, sabida ramuwar gasar da za'ayi.
Ya Salmanu kuwa yanzu ya fara jajir cewa, yana fakewa da jarumtar Jabeer yana gasawa Ba'ana maganganu.
Sosai ya ƙara shigewa Shatu a mako ɗayan nan.
Kuma tana jin daɗin hakan.
Ta sake sosai.
Zuwa yanzu kuma jikin Ummey yayi sauƙi garawau sai dai har yau bata taɓa yin mgna ba ta zama tamkar kurma.
Da dare bayan sallan isha'i,
tana zsune ita da ya Salmanu suna hira cikin nitsuwa tace.
"Ya Salmanu gobene zamuje asibiti mu dubo su Junaidu da sauran marasa lfy dake cikin Genaral Hospital Ɓadawaya, dan naji ƙishin-kishin ɗin wai har yanzu babu likitan daya dubasu."
Cikin gamsuwa da hakan yace.
"Eh hakan yana da kyau, kuje in sha Allah muma jibi asabar zamuyi gamgami muje, danma goben jumma'a ne da munje tare".
Sai kuma ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Da yaushe zakuje?".
Cikin sanyi tace.
"Da safe zamuje, in anyi sallan azahar zan dawo, amman Rafi'a zata wuce makaranta".
yace.
"To ke sai yaushe zaki koma?".
"Sai Ummey ta ɗan ƙara samun sauƙi. Ni da na so mu kaita asibiti kan batun rashin mgnar tata.
Gyara zaman shi yayi tare da cewa.
"Wannan ba matsala bace, wlh firgici da tsoro ne yasata hakan".
Haka dai sukaci gaba da hirarsu.
Washe gari ranar jumma'a, misalin karfe sha biyu dai-dai suka fito zasu tafi asibitin.
A bakin lambun garinsu sukayi kiciɓis da Ba'ana nan ya tsaidata dole suka zauna.
A can cikin masarautar Joɗa kuwa,
Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, da Jabeer ne tafe a hankali suka shiga cikin Garden ɗin nan.
Ta gefen Lamiɗo, suna shiga suka nufi inda katon curin dake wurin shekara da shekaru.
Shi dai Jabeer binsu yakeyi baiyi magana ba,
Koda suka isa wurin zama sukayi dabas a ƙasa.
Dole shima ya zauna, cikin sanyi Lamiɗo yace.
"Assalamu alaikum Jaimi".
Da mamaki Jabeer ya kalleshi,
Hiraminshi ya gyara tare da cewa.
"To yau kuma".
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya rufe mishi bakinshi.
Hannunshi yasa ya janye hannun Galadima tare da cewa.
"Yo ai ba sai ka rufe min bakiba, in kace nayi shiruma zanyi, sai dai ina naga abin saɓon Allah ko tsireni za'ayi sai na faɗa".
Dafe kai Galadima yayi tare da tsuke fuskarsa.
Ganin haka ya taɓe baki tare da ɗaga kafaɗunshi ya ɗan buɗasu alamar, ban damuba.
Sarkin Shaɗi kuwa bai kallesu bama.
Wani irin zabura Jabeer yayi cikin tsananin firgici da kaɗuwa lokacin da yaga wani irin h ....!
By
*GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako wacce ƙofa na jikin curin.
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi.
Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga ƙofofin ramin shirgegen curin.
Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune.
Ido ya zuba musu tare da cewa.
"Me hakan?".
Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da cewa.
"Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?".
Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce.
Cikin hatsala Lamiɗo yace.
"Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe bakin nan".
Wani kallo yayi mishi tare da cewa.
"Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah".
Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi.
Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa,
Sai wani irin huci.
Da sauri Jabeer yace.
"Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma'a ace, inada abinda yafi wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan sha biyu."
Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba.
Sabida dama sun san za'ayi haka kam.
Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba.
Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau.
Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi girma.
Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun!."
Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu.
Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi.
Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya razana.
Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai suke firgitashiba.
tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za'ayi mishi ne.
Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta fitowa taƙi ƙarewa.
Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune.
Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine.
A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo,
Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin nan saida suka fito ras kamar an wonkesu.
Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma,
Kamar forko sai ga hayaƙin.
Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa.
"Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za'a jazamin kaji su bini su tsastsageni.
Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah".
Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu,
fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi.
Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana suma duk suka miƙa.
Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin.
Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo,
da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa.
"Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu nan.
Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?".
Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace.
"Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa".
Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita.
Lamiɗo kuwa tuni sun tafi.
Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi.
A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci.
"Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben gargaji.
Wannan wacce iriyar fitinace?".
Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi,
babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan jumma'a ne.
A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi.
Kai tsaye bathroom ya wuce.
Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire,
Cillasu yayi cikin injin wonki.
A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue.
A hankali ya shiga cikin wurin wonkan.
Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma'a anshi.
Bayan ya fitone ya nufi drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin.
Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa, yana tsane ruwan jikinshi.
Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi.
Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare ɗayar ma.
Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya.
Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman kanshi.
Cikin hamzari ya fito bedroom,
Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi. Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi.