Sashe 59
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana shiga, falon, ya samu, Haroon ma zaune, shida Jakadiyarsu,
tana ganinshi ta faɗaɗa fara'arta cikin kula da so mai zurfi tace.
"Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai hatimin sarauta."
Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace.
"Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma".
Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a cikinta ta kuma haifeshi,
Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso."
Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace.
"Ina kwana Ummi, ya su Jalal?".
Murmushi ta kumayi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda yaje , Jafar zai bishi,
sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi,
wani sa'in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari.
Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya shigo nan wurinka".
Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace.
"Ummi Jamil da mata?".
Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace.
"Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya korata".
Cikin sanyi yace.
"Ummi waya gayawa Abba?".
Kai ta jujjuya tare da cewa.
"Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi, Mamanku kuwa kuka tayi- tayi".
Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace.
"Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart ɗin.
Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi ko cikekken jam'i bai samuba".
Ido Haroon ya lumshe tare da cewa.
"Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara, Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan."
Murmushi Ummi tayi kana tace.
"To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?."
Hararan Sheykh yayi tare da cewa.
"To Ummi".
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace.
"Haroona yaushene bikin naku kam?".
Kanshi ya ɗan shafa kana yace.
"Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban tuzurun".
Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom.
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace.
"Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?".
Baki ya ɗan turo tare da cewa.
"Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce".
Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan,
cikin yin ƙasa da murya tace.
"Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin."
Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi.
A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma yardaddun hadimanta mutun biyu.
Breakfast mai kyau suka, haɗawa Sheykh.
Yayinda Aunty Juwairiyya ma ta shiga kitchin da kanta, ta haɗa mishi breakfast.
Jakadiyarsu kuwa da Jamil da Jalal da Affan Haroon suna falon sunata hirarsu.
A tare hadiman Mama dana Juwairiyya suka kawo, abin kari.
Suna fita ba da ɗewa, hadiman Gimbiya Aminatu kakarsu kenan.
Suka shigo suma da abun kari.
Suka jera komai kan babban dinning table dake dinning area'n dake falon.
Bayan sun fitane.
Suna cikin hira, sarƙin ƙofa, ya shigo, ya shaida musu, ga saƙo an kuma kawowa.
Jamil ne ya bada daman a shigo.
Nan ya juya ya fita,
jim kaɗan, aka turo ƙofar.
Cikin mamaki suka zuwa ƙofar ido.
Ganin M....!
*Wannan shafin nakine ke ɗaya MRS SARDAUNA, Sheykh yana godiya da soyayyarki gareshi. Domin duk masoyanshi bayanki sunka biyo*
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 14
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘
*Daga gobe ne, FREE PAGE zai ƙare, in da zan saki page 15-16 daga su kuma in kin sake ganin littafin GARKUWA a woje ba cikin groups ɗin da na buɗe nasa wanda suka biya ba, To na satane, na waɗanda basu san darajar iyayenka da girman Allah da Manzonsa suka fitar ne, to ke kuwa in kin san darajan iyayenki da girman Allah da Manzonsa, kada ki karanta na sata, akwai group ɗin ɗari uku kacal ban tsauwala ba dan nasan halin TLC da muke ciki a ƙasar nan ga mai wadata wacce take da dama taga zata iya biyan na Special Group 1k ne rak. Zaki turo ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276, kuma ƴan 300 zaku iya turowa ta ac na ɗin, in kuma baki da dama to turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number dai 09097853276. Dan Allah da Manzonsa in kin san zaki fitarmin da littafi biyoni PC ki gaya min wlh zan baki kuɗinki in fiddaki group salum-alum, ina kuma jin san saya zakiyi ki fidda na roƙeki da Allah da Manzonsa wanda bayansu babu wani kada ki saya ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina🤗*
FREE PAGE, daga gobe dai zasu ƙare ki biya kuɗin ki in kinada niyan saya.
Ganin Mom ce, yasa fuskokinsu ya baiyana abinda ke cikin zuƙatansu.
Cikin ƙasaita, Mom ke tafiya, hadimanta biyu na biye da ita da manyan kuloli na al'farma.
Jakadiyarsu ce tayi murmushi mai kama da yaƙe, tare da rusunar da kai, cikin girmamawa tace.
"Barka da shigowa, Gimbiyar ahlin masarautar Joɗa.
Cikin isa da ƙasaita ta gyaɗa mata kai bayan ta zauna, gefen Jamil dake ruggume da waya kamar, abin masifa,
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Jalal daya haɗe fuska,
Juwairiyya yace ta ɗan gyara zamanta tare da cewa.
"Barka da safiya Mom".
Murmushi mai wuyar fassarawa tayi, tare da taɓe baki, a gyatsine tace.
"Barka dai". Sai ta kuma juya ta kalli inda Jakadiyarsu ke zaune, cikin isa tace.
"GARKUWAN YA FITANE?".
A daƙile Jalal yace.
"Yana ciki kuma hutawa yakeyi".
Ko inda yake bata kallaba tace.
"Jakadiya ina buƙatar ganinshi, yanzu".
Cikin biyeyyarta tace.
"Ranki ya daɗe, in zaton bacci yakeyi".
A taƙaice tace.
"A tadoshi".
Haroon dai ido ya zuba musu yana ganin ikon Allah, kowa ji da kai da ƙasaita.
Juwairiyya ce ta ɗan kalli Haroon ɗin cikin sanyi tace.
"Ukhti, shiga ka sanar mishi".
To kawai yace, kana ya miƙe ya shiga bedroom ɗin, da Sheykh ya shiga mituna ashirin baya,
kasake yayi a bakin kofar ganin babu kowa a cikin bedroom ɗin.
A hankali ya tako ya shiga ciki, bakin ƙofar bathroom ya ɗan matso, kunnenshi ya kasa wai a lissafinshi ko zaiji mitsin ruwa.
Shiru babu kowa a ɗakin da kuma bathroom ɗin.
Ko ina yayi tsit sai wani fitinenne sanyi daya cika ɗakin, wanda sai sautin
A/C dake busawa shuuuuu a hankali.
Waige-waige yayi ganin babushi babu, motsinshi ne, ya sashi ɗan ɗaga murya yace.
"Jabeer! Jabeer!! Jabeer!!!".
Jin shirune yasashi sa hannunshin ya ɗan ƙonƙosa ƙofar bathroom, still shiru.
Hakane yasa ya ɗan tura ƙofar, wayam baya ciki.
Ganin hakane ya sashi juyawa,
shima ɗin cikin takun ƙasaitar ya fito gefen Jalal ya zauna tare da kallon Juwairiyya,kana yace.
"Baya cikifa".
Wani irin kallo Mom tayi mishi, wanda yake nuna abinda ke bakinta, cikin ɗan sakin fuska yace.
"Allah kuwa Mom baya ciki".
Kanta ta gyaɗa tare da yunƙura ta tashi tsaye.
Kana a hankali tace.
"Uhummm". Sai kuma ta juya ta kama hanyar fita, hadimanta na biye da ita a baya.
Har yaje bakin ƙofa ta juyo tare da cewa,
Ga breakfast ɗin Garkuwa".
Haroon ne yayi godiya kana ta juya ta fita.
Cikin mmki Haroon ya kalli Jamil tare da cewa.
"Jamil baya cikifa".
Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Kun dai haɗa baki, kunƙi ya fito, ya gaisa da Mamanshi".
Jalal ne ya ƙara tsuke fuskarsa tare da cewa.
"Mamarshi ko makirarshi".
Jakadiyarsu ta ɗan gyara zama tare da cewa.
"Uhummm, sanin halin mutum sai Allah".
Sai kuma ta kalli Haroon tace.
"Haroona kace mishi yazo yayi karin kumallo, kace mishi daga sashin Gimbiya Aminatu ce, ga kuma na Juwairiyya".
Cikin jaddawa yace.
"Allah kuwa Ummi baya cikifa".
Da mamaki a fuskokinsu suka ɗan kalleshi, Jamil ne yace.
"Bai fita bafa".
Juwairiyya ce, ta amshi zancen da cewa.
"To kuma dai bai biyo nanba, tunda ya shiga bai fitoba".
Shi dai Haroon Ido ya zuba musu, ganin kamar basu yarda Jabeer baya cikiba.
Kuwa hakanne, saida Jamil yaje ya duba babu shi a ciki babu alamarsa.
Cikin tarin mamaki ya sanar musu, baya nan ɗinfa.
Jalal ne ya ɗan kauda tunaninsu da cewa.
"To kunata surutu, ta ina zakuga sanda ya fita, kai Jamil hankalinka duk na kan waya ina zaka ganshi."
Cikin kula Jakadiyarsu tace.
"Kaga fitarsane?".
Baki ya ɗan taɓe tare da cewa.
"Ni ban ganiba, na dai san shi ba kuɗi bane bare ya ɓata, ku jira zaku ganshi".
Da haka sukayi amanna dan a zatonsu yaga fitarshi kawai bauɗewarshi ne yasa bazai sanar musuba.
A can cikin fadar Masarautar Joɗa kuwa, falon sashin mai martaba Lamiɗo, cike yake da ƴaƴanshi maza, ziryan, wanda kullum iwar hakan suke haɗuwa domin gaidashi kana su gaisa da juna, ya tambayi lfyar ko wanne ɗanshi da ahlinshin.
To yau ta kasance jumma'atu babbar rana, wanda kuma, duk safiyar jumma'a.
Cikin wani ɗakin gadon sarautarsu, yakan shiga shida kanshi, yake tsabtace wannan ɗakin duk ran jumma'ar duniya, a tarihi da tsarin masarautarsun babu wanda zai shiga ɗakin sai wanda yake, matsayin Sarki.
Babu wani wanda ya taɓa shiga wannan ɗakin, sai wanda yake sarki.
tana ganinshi ta faɗaɗa fara'arta cikin kula da so mai zurfi tace.
"Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai hatimin sarauta."
Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace.
"Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma".
Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a cikinta ta kuma haifeshi,
Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso."
Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace.
"Ina kwana Ummi, ya su Jalal?".
Murmushi ta kumayi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda yaje , Jafar zai bishi,
sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi,
wani sa'in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari.
Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya shigo nan wurinka".
Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace.
"Ummi Jamil da mata?".
Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace.
"Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya korata".
Cikin sanyi yace.
"Ummi waya gayawa Abba?".
Kai ta jujjuya tare da cewa.
"Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi, Mamanku kuwa kuka tayi- tayi".
Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace.
"Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart ɗin.
Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi ko cikekken jam'i bai samuba".
Ido Haroon ya lumshe tare da cewa.
"Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara, Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan."
Murmushi Ummi tayi kana tace.
"To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?."
Hararan Sheykh yayi tare da cewa.
"To Ummi".
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace.
"Haroona yaushene bikin naku kam?".
Kanshi ya ɗan shafa kana yace.
"Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban tuzurun".
Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom.
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace.
"Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?".
Baki ya ɗan turo tare da cewa.
"Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce".
Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan,
cikin yin ƙasa da murya tace.
"Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin."
Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi.
A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma yardaddun hadimanta mutun biyu.
Breakfast mai kyau suka, haɗawa Sheykh.
Yayinda Aunty Juwairiyya ma ta shiga kitchin da kanta, ta haɗa mishi breakfast.
Jakadiyarsu kuwa da Jamil da Jalal da Affan Haroon suna falon sunata hirarsu.
A tare hadiman Mama dana Juwairiyya suka kawo, abin kari.
Suna fita ba da ɗewa, hadiman Gimbiya Aminatu kakarsu kenan.
Suka shigo suma da abun kari.
Suka jera komai kan babban dinning table dake dinning area'n dake falon.
Bayan sun fitane.
Suna cikin hira, sarƙin ƙofa, ya shigo, ya shaida musu, ga saƙo an kuma kawowa.
Jamil ne ya bada daman a shigo.
Nan ya juya ya fita,
jim kaɗan, aka turo ƙofar.
Cikin mamaki suka zuwa ƙofar ido.
Ganin M....!
*Wannan shafin nakine ke ɗaya MRS SARDAUNA, Sheykh yana godiya da soyayyarki gareshi. Domin duk masoyanshi bayanki sunka biyo*
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 14
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🐄🌈🦚🤴🏻💘
*Daga gobe ne, FREE PAGE zai ƙare, in da zan saki page 15-16 daga su kuma in kin sake ganin littafin GARKUWA a woje ba cikin groups ɗin da na buɗe nasa wanda suka biya ba, To na satane, na waɗanda basu san darajar iyayenka da girman Allah da Manzonsa suka fitar ne, to ke kuwa in kin san darajan iyayenki da girman Allah da Manzonsa, kada ki karanta na sata, akwai group ɗin ɗari uku kacal ban tsauwala ba dan nasan halin TLC da muke ciki a ƙasar nan ga mai wadata wacce take da dama taga zata iya biyan na Special Group 1k ne rak. Zaki turo ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276, kuma ƴan 300 zaku iya turowa ta ac na ɗin, in kuma baki da dama to turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number dai 09097853276. Dan Allah da Manzonsa in kin san zaki fitarmin da littafi biyoni PC ki gaya min wlh zan baki kuɗinki in fiddaki group salum-alum, ina kuma jin san saya zakiyi ki fidda na roƙeki da Allah da Manzonsa wanda bayansu babu wani kada ki saya ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina🤗*
FREE PAGE, daga gobe dai zasu ƙare ki biya kuɗin ki in kinada niyan saya.
Ganin Mom ce, yasa fuskokinsu ya baiyana abinda ke cikin zuƙatansu.
Cikin ƙasaita, Mom ke tafiya, hadimanta biyu na biye da ita da manyan kuloli na al'farma.
Jakadiyarsu ce tayi murmushi mai kama da yaƙe, tare da rusunar da kai, cikin girmamawa tace.
"Barka da shigowa, Gimbiyar ahlin masarautar Joɗa.
Cikin isa da ƙasaita ta gyaɗa mata kai bayan ta zauna, gefen Jamil dake ruggume da waya kamar, abin masifa,
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Jalal daya haɗe fuska,
Juwairiyya yace ta ɗan gyara zamanta tare da cewa.
"Barka da safiya Mom".
Murmushi mai wuyar fassarawa tayi, tare da taɓe baki, a gyatsine tace.
"Barka dai". Sai ta kuma juya ta kalli inda Jakadiyarsu ke zaune, cikin isa tace.
"GARKUWAN YA FITANE?".
A daƙile Jalal yace.
"Yana ciki kuma hutawa yakeyi".
Ko inda yake bata kallaba tace.
"Jakadiya ina buƙatar ganinshi, yanzu".
Cikin biyeyyarta tace.
"Ranki ya daɗe, in zaton bacci yakeyi".
A taƙaice tace.
"A tadoshi".
Haroon dai ido ya zuba musu yana ganin ikon Allah, kowa ji da kai da ƙasaita.
Juwairiyya ce ta ɗan kalli Haroon ɗin cikin sanyi tace.
"Ukhti, shiga ka sanar mishi".
To kawai yace, kana ya miƙe ya shiga bedroom ɗin, da Sheykh ya shiga mituna ashirin baya,
kasake yayi a bakin kofar ganin babu kowa a cikin bedroom ɗin.
A hankali ya tako ya shiga ciki, bakin ƙofar bathroom ya ɗan matso, kunnenshi ya kasa wai a lissafinshi ko zaiji mitsin ruwa.
Shiru babu kowa a ɗakin da kuma bathroom ɗin.
Ko ina yayi tsit sai wani fitinenne sanyi daya cika ɗakin, wanda sai sautin
A/C dake busawa shuuuuu a hankali.
Waige-waige yayi ganin babushi babu, motsinshi ne, ya sashi ɗan ɗaga murya yace.
"Jabeer! Jabeer!! Jabeer!!!".
Jin shirune yasashi sa hannunshin ya ɗan ƙonƙosa ƙofar bathroom, still shiru.
Hakane yasa ya ɗan tura ƙofar, wayam baya ciki.
Ganin hakane ya sashi juyawa,
shima ɗin cikin takun ƙasaitar ya fito gefen Jalal ya zauna tare da kallon Juwairiyya,kana yace.
"Baya cikifa".
Wani irin kallo Mom tayi mishi, wanda yake nuna abinda ke bakinta, cikin ɗan sakin fuska yace.
"Allah kuwa Mom baya ciki".
Kanta ta gyaɗa tare da yunƙura ta tashi tsaye.
Kana a hankali tace.
"Uhummm". Sai kuma ta juya ta kama hanyar fita, hadimanta na biye da ita a baya.
Har yaje bakin ƙofa ta juyo tare da cewa,
Ga breakfast ɗin Garkuwa".
Haroon ne yayi godiya kana ta juya ta fita.
Cikin mmki Haroon ya kalli Jamil tare da cewa.
"Jamil baya cikifa".
Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Kun dai haɗa baki, kunƙi ya fito, ya gaisa da Mamanshi".
Jalal ne ya ƙara tsuke fuskarsa tare da cewa.
"Mamarshi ko makirarshi".
Jakadiyarsu ta ɗan gyara zama tare da cewa.
"Uhummm, sanin halin mutum sai Allah".
Sai kuma ta kalli Haroon tace.
"Haroona kace mishi yazo yayi karin kumallo, kace mishi daga sashin Gimbiya Aminatu ce, ga kuma na Juwairiyya".
Cikin jaddawa yace.
"Allah kuwa Ummi baya cikifa".
Da mamaki a fuskokinsu suka ɗan kalleshi, Jamil ne yace.
"Bai fita bafa".
Juwairiyya ce, ta amshi zancen da cewa.
"To kuma dai bai biyo nanba, tunda ya shiga bai fitoba".
Shi dai Haroon Ido ya zuba musu, ganin kamar basu yarda Jabeer baya cikiba.
Kuwa hakanne, saida Jamil yaje ya duba babu shi a ciki babu alamarsa.
Cikin tarin mamaki ya sanar musu, baya nan ɗinfa.
Jalal ne ya ɗan kauda tunaninsu da cewa.
"To kunata surutu, ta ina zakuga sanda ya fita, kai Jamil hankalinka duk na kan waya ina zaka ganshi."
Cikin kula Jakadiyarsu tace.
"Kaga fitarsane?".
Baki ya ɗan taɓe tare da cewa.
"Ni ban ganiba, na dai san shi ba kuɗi bane bare ya ɓata, ku jira zaku ganshi".
Da haka sukayi amanna dan a zatonsu yaga fitarshi kawai bauɗewarshi ne yasa bazai sanar musuba.
A can cikin fadar Masarautar Joɗa kuwa, falon sashin mai martaba Lamiɗo, cike yake da ƴaƴanshi maza, ziryan, wanda kullum iwar hakan suke haɗuwa domin gaidashi kana su gaisa da juna, ya tambayi lfyar ko wanne ɗanshi da ahlinshin.
To yau ta kasance jumma'atu babbar rana, wanda kuma, duk safiyar jumma'a.
Cikin wani ɗakin gadon sarautarsu, yakan shiga shida kanshi, yake tsabtace wannan ɗakin duk ran jumma'ar duniya, a tarihi da tsarin masarautarsun babu wanda zai shiga ɗakin sai wanda yake, matsayin Sarki.
Babu wani wanda ya taɓa shiga wannan ɗakin, sai wanda yake sarki.