Sashe 80
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gefen gabas ya fuskanta, inda labulaye sukayiwa wurin ƙawanya.
A hankali yasa hannunshin ya yaye labulen.
Wani ƙofa ya buɗe a .
Sai ga wani ɗan siririn corridor.
Shiga yayi, kana ya saki ƙofar ta koma ta mannu da ƙofar sai dai bata rufuba.
A hankali yake taku cikin nitsuwa,
Lips ɗin shi na ɗan motsawa alamun tasbihi yakeyi.
Tafiya mai ɗan tsawo yayi sai gashi ya kuma riski wata ƙofar.
Hannunshi yasa ya murɗa key ɗin ya buɗe, ƙofar.
Sai ga kuma wata ƙofa irin ta ƙarafuna kana dai iya hango woje.
Buɗe wannan ƙofarma yayi.
A hankali ya kutsa kai.
Wani irin sassanyan ajiyan zuciya mai tsawo yaja ya sauƙe a hankali.
Idonshi ya lumshe sabida wani irin sanyi mai masifar daɗi daya ratsa mishi jiki da zuciya.
Wani irin ɗan madaidaicin Garden Park ne mai masifar kyau.da sanyi da tsaruwa.
Daga nan bakin ƙofar daya fito ɗin.
Tayis ne fari tas a malale iya ganinka, sai gefen damanshi da bishiyoyin ayaba masu masifar duhu da sanyi dake jere reras.
Gefen hagunshi kuma bishiyoyi mangoro ne irin yan duƙus-duƙus ɗin nan ke jere,
Reras.
A hankali yake taku yana tafe yana tasbihi.
Yana jin kukan tsuntsaye mai daɗin ji yana ratsashi.
Tafiya kaɗan yayi sai gashi ya baiyana a wani irin wurin mai masifar kyau.
Wasu yan zagayen gini dakalin bulok bibbiyu akayi a ƙalla sunfi hamsin.
A ciki ko wanne zagayen akwai bishiyar dabino. Na gabanta inabi na gaban inabi tuppa, kana sai Yazawa, sai kuma na tsada, daga tsada sai na kanya, sai goruba da na giginya.
Cikin ko wanne zageyen kuma ƙasanshi koriyar ciyawa ce mai sanyi.
Can tsakiyar filin kuma wata iriyar ƙoramace mai masifar sanyi,
Ruwanshi na kwance fari ƙal-ƙal bakin wurin kuma jeren bishiyoyi goibane wanda sukayiwa kwaramar inuwa.
Gaban ƙoramar kuma wasu irin kujerun silver ne masu masifar kyau da sansi a jere a ƙalla sun kai goma zuwa ashirin.
Can gefenshi kaɗan kuma wani shingene aka zagaye da waya.
Shuke-shuken gargajiya akeyi a wurin.
Nan kusa da ƙoramar kuma shingen farar waya akayi a cikin ta wanda akayi ƴan ɗakuna-ɗakuna a cikin.
Tsuntsaye ne a ciki iya ganinka ko wanne da muhalli shin.
Kama daga Tattabaru farare ƙal-ƙal.
Sai kuma tsuntsu carki jajaye masu kyan launi ga kuma kanari da suke blue.
Sai kuma zabbi da suke yawo a ƙasa tako ina.
Can bakin ruwan kuma agwagin ruwa ne sunfi ɗari ƙwa-ƙwa.
Sai kuma zabbin daji.
dangin tsuntsaye dai babu irin wanda babu.
Ido ya zubawa tsuntsaye tamkar mai son yin magana dasu.
A hankali ya sunkuyar da kanshi jin tattausan gashin Ɗawisun Masarautar Joɗa da ya kai shekaru masu tarin yawa.
A hankali ya rusuna tare dasa tafin hannunshi ya shafa dai-dai ƙunɗun Ɗawisun inda wurin yake mai kalar blue mai kyau sabida Sheykh blue ne kalar da yafi so.
A hankali ta fara taku, ta juya mishi baya kana ta ɗaga bindinta sama samɓal har yana iya taɓo geminshi.
Wani irin takun ƙasaita tayi kana ta buɗa fikafikinta ta bazasu, ta fara tafiya a hankali.
Wannan itace suntsuwar da muddin mutun ba jinin Masarautar Joɗa bace, in ka shigo mata gaba gaɗi ba tare da an gabatar mata kai ba, zatayi ta yagune mutun tana caccakarshi.
Amman muddin dai kai jinin Masarautar Joɗa ne, kana shiga zata zo gabanka.
Tayi maka hakan.
Sai dai kuma bayan yin hakan in mutun nada wata zazzafar nasaba a masarautar misali shine sarki maici to in tayi wannan baza fikafikinta takanyi ta zagaya sarki sau bakwai kafin ta tsaya a gabanshi sai sarkin ya umarceta data tafi kafin zata tafi.
To babban abinda ya ƙara jazawa Jabeer matsala a rayuwarsa shine,
Duk sanda yazo gaban tsuntsuwar Ɗawisun nan sai tayi mishi wannan abin da zagaya sau bakwai abinda a tarihin masarautar sarki kawai yakeyiwa abin.
Matsalar abin a gaban Barrister Kamal da kuma Baba Bashiru da Abba sai Lamiɗo ne ta fara yimishi wannan abun.
Tofa ta bakin Baba Basiru ne mgnar ta zaga kunnen mazauna masarautar Joɗa.
Babban tashin hankalin masu son gadar wannan kujerar, shine yadda side ɗin Jabeer ke kusanci da Garden ɗin da take ciki.
Tashin hankalinsu ya ƙara tsananta ne tun randa Suka ga Lamiɗo yasa an buɗawa Jabeer hanyar shiga wurin ta cikin falonshi ba sai ya zagaya yabi hanyar da kowa ke bi ba,
Ya zama shida Lamiɗo sune masu hanya kowa daga falonshi zai shiga wurin.
A hankali Jabeer yayi murmushi tare da kallon yadda tsuntsuwar ta gama zagayashi kana tazo ta tsaya gabanshi tare da baza fikafikinta.
Cikin harcen Larabci yace mata.
"Fatana dai ba bauta min kikeyi ba! Domin babu wani abin bautawa da gsky sai Allah, wanda shine ya halicce ni ya halicceki.
Ni kuma ba kowa bane face halittarsa, sai dai na kasance cikin halittarsa mai girma da karrama fiye da komai, dan shi da kanshi yace.
Walaƙad karramna bani Adam."
Wani irin juya kai tsuntsuwar tayi kana ta meda fiffigefa ta rufe, kafin ta juya ta nufi wani kekyawan wurin da aka ware mata, inda take tare da yayanta da mijinta.
Juyawa yayi can gefe ya hango wasu yan kyawawan tsuntsaye farare
A bakin ruwan.
Ga tattabarun sun zagaye wurin da sauran tsuntsayen.
A hankali ya zauna a wata kujera mai kamar gado.
Kishinƙiɗa yayi kana ya lumshe idonshi yana maijin yadda sassanyan iskar wurin ke ratsashi.
Karatun al'ƙur'ani ya fara cikin sassanyan murya mai daɗin sauraro.
Umaymah kuwa tunda ta fito, sai ta nufi sashin Hajia Mama, hira sukayi sosai cikin shaƙuwa irin ta yan uwa.
Suna zaune a nan Abba ya shigo.
Tana ganinshi tai murmushi,
shima murmushin yayi tare da cewa.
"Maman yara".
Cikin sakin fuska tace.
"Na'am Yaya".
Murmushi mai cike da zafi da ƙuna wanda ya baiyana har kan fuskarshi yayi kana ya zauna gefenta.
Gaisawa sukayi cikin danne ababen dake cin ransu.
Hajia Mama kuwa, tuni sai hawaye take zubdawa.
A hankali Umaymah ta miƙa mata handkin dake hannunta alamun ta share hawayenta.
Bayan ta share hawayenta ne,
Abba ya miƙa tare da cewa.
"Kin gaisa da Mom Imran kuwa? Da Salma".
Fuska a ɗan haɗe tace.
"A a".
Miƙewa yayi tare da cewa.
"To muje ku gaisa."
Binshi tayi a baya suka nufi inda yace ɗin.
A falo suka samu Mom Imaran tana ganin.
Sun shigo tare da Hajia Mama tayi wani irin haɗe fuska, cikin nuna ko in kula tacewa Umaymah.
"Yaushe kikazo?".
A daƙile tace.
"Jiya".
Kanta ta ɗan kauda tare da cewa.
"Ya hanya".
Alhamdulillah tace a taƙaice.
Cikin kufula Hajia Mama tace.
"Mu tafi".
Miƙewa Umaymah tayi kana Abba ma ya miƙa sashin Amaryarshi Salma ya nufa da ita.
Suna shiga tana jin muryarshi ta fito, da sauri ta nufe shi da nufin zata ruggumeshi da sauri yace.
"Ga Umaymah tazo".
A take taja birki ta tsaya cikin gyatsine tace.
"Ya kike kinzo lfy, ki gaida mutan gida".
Cikin wani irin kallo Umaymah tace.
"Uhummmm kema ki gaida mutan gidanku".
Tana faɗin haka ta juya ta tafi abinta.
Hajia Mama na biye da ita.
Ita kuwa Salma tana ganin fitansu ta ruggume mijinta.
Koda suka koma Side ɗin Hajia Mama bata daɗe a nanba ta nufi sashin Gimbiya Aminatu.
To bata fito nan ɗinba sai shabiyu saura.
Koda ta dawo Haroon da Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya kawai ta samu a falon.
Sai kuma Jalal da Hibba da suke dinning area suna zaune bisa kujerun Dinning table ɗin.
Sun sa plet a tsakiyarsu da kofunan tea a hannunsu, alamun sai yanzu sukeyin breakfast.
Cikin kula Aunty Juwairiyya tacewa Ƙanwar mahaifinta ɗin.
"Umaymah muje kuci abinci rana tayi fa".
Murmushi tayi tare da son danne ɓacin ranta tace.
"Alhamdulillah Juwairiyya Ni kuma da nakeda Hajia Mama ga Gimbiya Aminatu, ai naci nayi nak."
Cikin sauri Jakadiyarsu ta e.
"Ga kuma Matar Barrister Kamal ma ta aiko miki abin kari.
Gimbiya Saudatu ma ta aiko miki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"A ajiye minshi sai anjima, kinga Juwairiyya kada ki shiga kitchen yau kizo mu wuni hira abinmu, abinci tako ina zaizo".
Cikin sanyi Juwairiyya tace.
"Uhummm Umaymah ke har zaki iya cin abinci waɗanan mutane ai Gimbiya Saudatu ba abin wuya bane tasa mana guba muci duk mu mutu.
Sai dai muci na gidan Barrister".
Kai Jakadiyarsu ta jinjina alamun eh.
Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace.
"Haroon!."
Da sauri ya amsa tare da tahowa inda take.
Gefenta ya zauna tare da cewa.
"Umaymah gani".
Ba tare da ta kalleshiba tace.
"Ina Jazlaan?".
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Y shiga Garden".
Kai ta ɗan jinjina mishi tare da zubawa Jalal ido.
Ita Hibba sai murmushi takeyi shi kuma fuskarshi kamar boss.
A hankali ta miƙa ta nufi falon Jabeer ɗin.
Da sauri ta kalli Haroon tare da cewa.
"Ina zakaje".
Baki ya ɗan tura tare da cewa.
"Umaymah inda zakije mana".
Cikin tsokana tace
"Sirri zanyi da ɗan".
Tana faɗin haka ta juya ta nufi can. Shima Haroon yana biye da ita a baya.
A hankali take taku har ta isa inda yake.
Gefenshi ta zauna tare da zuba mishi ido.
Cikin kula tace.
"Jazlaan".
Cikim nitsuwa ya buɗe idonshi tare da kallon inda tarin tsuntsayen nan suke,
Lokaci ɗaya idanunshi suka kaɗa sukayi jazir.
lips ɗinshi ya fara motsawa da nufin yin mgna amman ya gagara,
sai wani irin kuka mai ƙarfi da yake son ƙawance mishi daga can ƙasan zuciyarsa.
Hakan yasa lips ɗinshi karkarwa tamkar mai jin sanyi.
Umaymah kuwa. Tuni hawaye sun wonke mata fuskarta tana mai kallon tsuntsayen.
Ganin Haroon yasa tayi mishi alamun ya kawo mata ruwa.
Ba musu ya juya ba tare da yayi mgn ba jim kaɗan ya dawo da goran ruwa da glass cup. Ruwan ya tsiyaya a kofin ya miƙa Umaymah.
Cikin sanyin murya tace.
"Ga ruwan sanyi kasha, nasan zakaji sanyin ƙunan da kakeji a ranka".
Ta ƙare shi mgnar tana miƙa mishi cup ɗin.
Amsa yayi yayinda gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi alamun tsananin tarin baƙin ciki duniya.
Da kyar ya iya shan rabin kofin.
Nan ta gyara zamanta tare da kamo hannunshi ta fara tausar zuciyarshi kan abinda tasan shine babban matsalarshi.
A hankali yasa hannunshin ya yaye labulen.
Wani ƙofa ya buɗe a .
Sai ga wani ɗan siririn corridor.
Shiga yayi, kana ya saki ƙofar ta koma ta mannu da ƙofar sai dai bata rufuba.
A hankali yake taku cikin nitsuwa,
Lips ɗin shi na ɗan motsawa alamun tasbihi yakeyi.
Tafiya mai ɗan tsawo yayi sai gashi ya kuma riski wata ƙofar.
Hannunshi yasa ya murɗa key ɗin ya buɗe, ƙofar.
Sai ga kuma wata ƙofa irin ta ƙarafuna kana dai iya hango woje.
Buɗe wannan ƙofarma yayi.
A hankali ya kutsa kai.
Wani irin sassanyan ajiyan zuciya mai tsawo yaja ya sauƙe a hankali.
Idonshi ya lumshe sabida wani irin sanyi mai masifar daɗi daya ratsa mishi jiki da zuciya.
Wani irin ɗan madaidaicin Garden Park ne mai masifar kyau.da sanyi da tsaruwa.
Daga nan bakin ƙofar daya fito ɗin.
Tayis ne fari tas a malale iya ganinka, sai gefen damanshi da bishiyoyin ayaba masu masifar duhu da sanyi dake jere reras.
Gefen hagunshi kuma bishiyoyi mangoro ne irin yan duƙus-duƙus ɗin nan ke jere,
Reras.
A hankali yake taku yana tafe yana tasbihi.
Yana jin kukan tsuntsaye mai daɗin ji yana ratsashi.
Tafiya kaɗan yayi sai gashi ya baiyana a wani irin wurin mai masifar kyau.
Wasu yan zagayen gini dakalin bulok bibbiyu akayi a ƙalla sunfi hamsin.
A ciki ko wanne zagayen akwai bishiyar dabino. Na gabanta inabi na gaban inabi tuppa, kana sai Yazawa, sai kuma na tsada, daga tsada sai na kanya, sai goruba da na giginya.
Cikin ko wanne zageyen kuma ƙasanshi koriyar ciyawa ce mai sanyi.
Can tsakiyar filin kuma wata iriyar ƙoramace mai masifar sanyi,
Ruwanshi na kwance fari ƙal-ƙal bakin wurin kuma jeren bishiyoyi goibane wanda sukayiwa kwaramar inuwa.
Gaban ƙoramar kuma wasu irin kujerun silver ne masu masifar kyau da sansi a jere a ƙalla sun kai goma zuwa ashirin.
Can gefenshi kaɗan kuma wani shingene aka zagaye da waya.
Shuke-shuken gargajiya akeyi a wurin.
Nan kusa da ƙoramar kuma shingen farar waya akayi a cikin ta wanda akayi ƴan ɗakuna-ɗakuna a cikin.
Tsuntsaye ne a ciki iya ganinka ko wanne da muhalli shin.
Kama daga Tattabaru farare ƙal-ƙal.
Sai kuma tsuntsu carki jajaye masu kyan launi ga kuma kanari da suke blue.
Sai kuma zabbi da suke yawo a ƙasa tako ina.
Can bakin ruwan kuma agwagin ruwa ne sunfi ɗari ƙwa-ƙwa.
Sai kuma zabbin daji.
dangin tsuntsaye dai babu irin wanda babu.
Ido ya zubawa tsuntsaye tamkar mai son yin magana dasu.
A hankali ya sunkuyar da kanshi jin tattausan gashin Ɗawisun Masarautar Joɗa da ya kai shekaru masu tarin yawa.
A hankali ya rusuna tare dasa tafin hannunshi ya shafa dai-dai ƙunɗun Ɗawisun inda wurin yake mai kalar blue mai kyau sabida Sheykh blue ne kalar da yafi so.
A hankali ta fara taku, ta juya mishi baya kana ta ɗaga bindinta sama samɓal har yana iya taɓo geminshi.
Wani irin takun ƙasaita tayi kana ta buɗa fikafikinta ta bazasu, ta fara tafiya a hankali.
Wannan itace suntsuwar da muddin mutun ba jinin Masarautar Joɗa bace, in ka shigo mata gaba gaɗi ba tare da an gabatar mata kai ba, zatayi ta yagune mutun tana caccakarshi.
Amman muddin dai kai jinin Masarautar Joɗa ne, kana shiga zata zo gabanka.
Tayi maka hakan.
Sai dai kuma bayan yin hakan in mutun nada wata zazzafar nasaba a masarautar misali shine sarki maici to in tayi wannan baza fikafikinta takanyi ta zagaya sarki sau bakwai kafin ta tsaya a gabanshi sai sarkin ya umarceta data tafi kafin zata tafi.
To babban abinda ya ƙara jazawa Jabeer matsala a rayuwarsa shine,
Duk sanda yazo gaban tsuntsuwar Ɗawisun nan sai tayi mishi wannan abin da zagaya sau bakwai abinda a tarihin masarautar sarki kawai yakeyiwa abin.
Matsalar abin a gaban Barrister Kamal da kuma Baba Bashiru da Abba sai Lamiɗo ne ta fara yimishi wannan abun.
Tofa ta bakin Baba Basiru ne mgnar ta zaga kunnen mazauna masarautar Joɗa.
Babban tashin hankalin masu son gadar wannan kujerar, shine yadda side ɗin Jabeer ke kusanci da Garden ɗin da take ciki.
Tashin hankalinsu ya ƙara tsananta ne tun randa Suka ga Lamiɗo yasa an buɗawa Jabeer hanyar shiga wurin ta cikin falonshi ba sai ya zagaya yabi hanyar da kowa ke bi ba,
Ya zama shida Lamiɗo sune masu hanya kowa daga falonshi zai shiga wurin.
A hankali Jabeer yayi murmushi tare da kallon yadda tsuntsuwar ta gama zagayashi kana tazo ta tsaya gabanshi tare da baza fikafikinta.
Cikin harcen Larabci yace mata.
"Fatana dai ba bauta min kikeyi ba! Domin babu wani abin bautawa da gsky sai Allah, wanda shine ya halicce ni ya halicceki.
Ni kuma ba kowa bane face halittarsa, sai dai na kasance cikin halittarsa mai girma da karrama fiye da komai, dan shi da kanshi yace.
Walaƙad karramna bani Adam."
Wani irin juya kai tsuntsuwar tayi kana ta meda fiffigefa ta rufe, kafin ta juya ta nufi wani kekyawan wurin da aka ware mata, inda take tare da yayanta da mijinta.
Juyawa yayi can gefe ya hango wasu yan kyawawan tsuntsaye farare
A bakin ruwan.
Ga tattabarun sun zagaye wurin da sauran tsuntsayen.
A hankali ya zauna a wata kujera mai kamar gado.
Kishinƙiɗa yayi kana ya lumshe idonshi yana maijin yadda sassanyan iskar wurin ke ratsashi.
Karatun al'ƙur'ani ya fara cikin sassanyan murya mai daɗin sauraro.
Umaymah kuwa tunda ta fito, sai ta nufi sashin Hajia Mama, hira sukayi sosai cikin shaƙuwa irin ta yan uwa.
Suna zaune a nan Abba ya shigo.
Tana ganinshi tai murmushi,
shima murmushin yayi tare da cewa.
"Maman yara".
Cikin sakin fuska tace.
"Na'am Yaya".
Murmushi mai cike da zafi da ƙuna wanda ya baiyana har kan fuskarshi yayi kana ya zauna gefenta.
Gaisawa sukayi cikin danne ababen dake cin ransu.
Hajia Mama kuwa, tuni sai hawaye take zubdawa.
A hankali Umaymah ta miƙa mata handkin dake hannunta alamun ta share hawayenta.
Bayan ta share hawayenta ne,
Abba ya miƙa tare da cewa.
"Kin gaisa da Mom Imran kuwa? Da Salma".
Fuska a ɗan haɗe tace.
"A a".
Miƙewa yayi tare da cewa.
"To muje ku gaisa."
Binshi tayi a baya suka nufi inda yace ɗin.
A falo suka samu Mom Imaran tana ganin.
Sun shigo tare da Hajia Mama tayi wani irin haɗe fuska, cikin nuna ko in kula tacewa Umaymah.
"Yaushe kikazo?".
A daƙile tace.
"Jiya".
Kanta ta ɗan kauda tare da cewa.
"Ya hanya".
Alhamdulillah tace a taƙaice.
Cikin kufula Hajia Mama tace.
"Mu tafi".
Miƙewa Umaymah tayi kana Abba ma ya miƙa sashin Amaryarshi Salma ya nufa da ita.
Suna shiga tana jin muryarshi ta fito, da sauri ta nufe shi da nufin zata ruggumeshi da sauri yace.
"Ga Umaymah tazo".
A take taja birki ta tsaya cikin gyatsine tace.
"Ya kike kinzo lfy, ki gaida mutan gida".
Cikin wani irin kallo Umaymah tace.
"Uhummmm kema ki gaida mutan gidanku".
Tana faɗin haka ta juya ta tafi abinta.
Hajia Mama na biye da ita.
Ita kuwa Salma tana ganin fitansu ta ruggume mijinta.
Koda suka koma Side ɗin Hajia Mama bata daɗe a nanba ta nufi sashin Gimbiya Aminatu.
To bata fito nan ɗinba sai shabiyu saura.
Koda ta dawo Haroon da Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya kawai ta samu a falon.
Sai kuma Jalal da Hibba da suke dinning area suna zaune bisa kujerun Dinning table ɗin.
Sun sa plet a tsakiyarsu da kofunan tea a hannunsu, alamun sai yanzu sukeyin breakfast.
Cikin kula Aunty Juwairiyya tacewa Ƙanwar mahaifinta ɗin.
"Umaymah muje kuci abinci rana tayi fa".
Murmushi tayi tare da son danne ɓacin ranta tace.
"Alhamdulillah Juwairiyya Ni kuma da nakeda Hajia Mama ga Gimbiya Aminatu, ai naci nayi nak."
Cikin sauri Jakadiyarsu ta e.
"Ga kuma Matar Barrister Kamal ma ta aiko miki abin kari.
Gimbiya Saudatu ma ta aiko miki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"A ajiye minshi sai anjima, kinga Juwairiyya kada ki shiga kitchen yau kizo mu wuni hira abinmu, abinci tako ina zaizo".
Cikin sanyi Juwairiyya tace.
"Uhummm Umaymah ke har zaki iya cin abinci waɗanan mutane ai Gimbiya Saudatu ba abin wuya bane tasa mana guba muci duk mu mutu.
Sai dai muci na gidan Barrister".
Kai Jakadiyarsu ta jinjina alamun eh.
Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace.
"Haroon!."
Da sauri ya amsa tare da tahowa inda take.
Gefenta ya zauna tare da cewa.
"Umaymah gani".
Ba tare da ta kalleshiba tace.
"Ina Jazlaan?".
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Y shiga Garden".
Kai ta ɗan jinjina mishi tare da zubawa Jalal ido.
Ita Hibba sai murmushi takeyi shi kuma fuskarshi kamar boss.
A hankali ta miƙa ta nufi falon Jabeer ɗin.
Da sauri ta kalli Haroon tare da cewa.
"Ina zakaje".
Baki ya ɗan tura tare da cewa.
"Umaymah inda zakije mana".
Cikin tsokana tace
"Sirri zanyi da ɗan".
Tana faɗin haka ta juya ta nufi can. Shima Haroon yana biye da ita a baya.
A hankali take taku har ta isa inda yake.
Gefenshi ta zauna tare da zuba mishi ido.
Cikin kula tace.
"Jazlaan".
Cikim nitsuwa ya buɗe idonshi tare da kallon inda tarin tsuntsayen nan suke,
Lokaci ɗaya idanunshi suka kaɗa sukayi jazir.
lips ɗinshi ya fara motsawa da nufin yin mgna amman ya gagara,
sai wani irin kuka mai ƙarfi da yake son ƙawance mishi daga can ƙasan zuciyarsa.
Hakan yasa lips ɗinshi karkarwa tamkar mai jin sanyi.
Umaymah kuwa. Tuni hawaye sun wonke mata fuskarta tana mai kallon tsuntsayen.
Ganin Haroon yasa tayi mishi alamun ya kawo mata ruwa.
Ba musu ya juya ba tare da yayi mgn ba jim kaɗan ya dawo da goran ruwa da glass cup. Ruwan ya tsiyaya a kofin ya miƙa Umaymah.
Cikin sanyin murya tace.
"Ga ruwan sanyi kasha, nasan zakaji sanyin ƙunan da kakeji a ranka".
Ta ƙare shi mgnar tana miƙa mishi cup ɗin.
Amsa yayi yayinda gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi alamun tsananin tarin baƙin ciki duniya.
Da kyar ya iya shan rabin kofin.
Nan ta gyara zamanta tare da kamo hannunshi ta fara tausar zuciyarshi kan abinda tasan shine babban matsalarshi.