← Book details Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 70 OF 142

Sashe 70

Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Shi kuwa Sarki Jalaluddin, ido ya zubawa wayar jin jikan nashi ya katse kiran, murmushi yayi, irin nasu na manya, kana da sauri ya kira, Umaymah.
A can Babba birnin Katsina, kuwa Gimbiya Khadijah Umaymah kenan , wacce take matar ɗan Sarkin Tsinako, Kekkyawar mata mai cikar haiba nitsuwa, tana kishinɗe, bisa wata tattausar doguwar kujera, yayinda Hadimanta biyu ke mata tausa.
Jin wayarta na suwane, yasa ta buɗe idanunta dake lumshe, tunda sukayi waya d, ɗan ta Haroon ke gaya mata inda sukaje da ƴaƴan ƴar uwarta mafi soyuwa a rayuwarsu ne, taketa murmushi.
Ganin sunan mahaifinta ne yasa tayi saurin amsa kiran.
Bayan sun gaisane, Sarki Jalaluddin ya ɗanyi murmushi cikin nitsuwa yace.
"Khadijah, kira ɗan ki, ki bashi umarnin bin umarnin mu, domin yana nuna mana ai bamu muka haifeshi ba, bazamu tirsasashi ba".
Cikin tarin girmamawa tace.
"Ranka ya daɗe, me kukeso in bashi umarni a kai nasan bazaiyi min musuba".
Cikin jin daɗi yace.
"Kice dashi ya amince da gasar da za'ayi".
Cikin sauri tace.
"To An gama yanzu kuwa, in sha Allah zaku sameshi mai biyayya a gareku".
Daga nan sukayi sallama,
Kana ta kirashi, sau biyu tana kiranshi baya ɗagawa, sabida kanshi ya ɗau zafi yana ganin za'a tirsasashi ya cutar da kanshi.
Ga wani irin azabebben tsinkewa da zuciyarshi keyi,
Ji yake tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito, tayi ta tsalle a doron ƙasa.
Gashi duk tsoffin Masarautarsun sun zagayeshi.
Kowa da abinda ke ce mishi.
Ga uban kiɗen-kiɗen dake hawa mishi kai.

Ita kuwa Umaymah ganin bai amsa kiran bane, yasa ta kira Haroon yana ɗagawa tace.
"Ina Jazlaan bashi wayar".
Da sauri yace.
"To Umaymah uwar Garkuwa gashi nan ido ya raina fata".
Cikin barkwancinta da yaron nata tace.
"Kaci gidanku Haroon Ni ɗana ba ragobane".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To mu gani a ƙasa mana Umaymah".
Yana faɗin haka ya miƙa Jabeer wayar wanda yake cewa Lamiɗo.
"Bafa zan yiba, tsohon nan gwara ka miƙe kaje ayi da kai tunda kaine sarkin Masarautar Joɗa, Ni nan babu abinda na sani bayan nonon uwata sai al'ƙur'ani da hadisai, sai likitancin da kuka sani na karanta a dole badon raina yasoba, tun ina yaro kullum Ni a cikin sani dole kuke da tsabar rainin hankali, kaje a jibgeka, Ni kuwa nayi al'ƙawarin zan jinyaceka, Lamiɗo Joɗa."
Ya ƙarishe mgnar yana amsar wayar da Haroon ke miƙo mishi cikin faɗa yace.
"Mitsss wai meye kaketa tura min wannan argar wayar taka ne?".
Cikin mamaki Haroon yace.
"Kan uba Jabeer wayar tawace ma arga, wayar da kuɗi ta sun kai rabin million To inma argace Umaymah ce bisa layi".
Ba tare da ya kara wayar a kunneba yace.
"Hello Umaymah".
Cikin tausayi Jalal yace.
"Hamma Jabeer baka kai wayar kunneba".
Lips ɗinsa ya taune tare da cewa.
"Au, zama su sani yin abu da yawa".
Haroon kuwa mamaki yakeyi domin karo na forko kenan da yaji Jabeer yace Hello a madadin Assalamu alaikum, da shine abinda yakeyi.
Ita kuwa Umaymah tana jin ya kara wayar a kunne shi ya kira sunanta cikin rauni.
Murya a kausashe tace.
"Jabeer".
Da mamaki ya amsa dan sama da shekaru goma sha biyu kenan da Jazlaan take kiranshi, cikin sanyi yace.
"Na'am Umaymah". Cikin bada umarni tace.
"Jabeer ka tashi maza yanzu ka shiga fagen gasar nan ayishi da kai, bana son musu umarnine ba shawara ba".
Cikin sauri ya zaro siraran kyawawan idanunshi,
Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo ya miƙe tsaye cikin tashin hankali da kiɗima da firgici da baƙin cikin dakatar da gasar Shaɗi da akayi a masarautarsu ya sani da anayi da Jabeer bazai ƙalubanceshi ba, cikin sanyi yace.
"Zanje za'ayi dani, zan tabbatar da darajar masarautatarmu bata rusheba."
Da ido yabi Dottijon kakan nashi wanda a ƙalla ya kai shekaru 91 a duniya.
Cikin kauda kai yace.
"To Umaymah yadda kikace haka za'ayi amman bari in kira Sheykh Abdulkareem in sanar mishi in ya amince dai zanyi".
Da sauri tace.
"A a ban yafe ka kirashi ba, wato don kasan in ka kirashi zai kira Sitti da Mai alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen ya dakatar da duk abinda za'ayin, tunda na san cemishi zakayi ba addini bane, al'adace, to ban yardaba maza tashi".
Ganin Ya Hashim na miƙa masa wayarshi ne yasashi cewa Umaymah.
To cikin sanyi.
Yana amsa wayar da Ya Hashim ya miƙa mishi yaki Muryar, mahaifinshi cikin sanyi da kuma alamun yana kukane yace.
"Jabeer ashe har kayi girman da Lamiɗo zai umarceka da yin abu kaƙi yi mishi mubaya'a,
Ashe har na haifi ɗan da zai ja da mahaifina."
Cikin sanyi da rauni yake jujjuya kai murya na rawa yake cewa.
"A'a Abba, kayi haƙuri kada kayi kuka a kaina."
Bai kulashiba yaci gaba da cewa.
"Jabeer Ashe zuciyarka har tayi tauri da kangarewar da kanaji kana gani za'a daki mahaifina a gaban idonka, bazaka zame mishi GARKUWA ba, Jabeer wannan shine tukuicin tsantsar son da mahaifina keyi muka, wanda har ya jazamin ƙiyayya a wurin yan uwana sunaga ya fifitaku kan sauran jikokinsa Especially ma kai Jabeer komu daya haifa baya nuna mana son da yake nuna maka, shine zaka bari a dakeshi mutun mai shekaru 91 da ɗaya a duniya kai me shekaru 30 bazaka iya zame mishi GARKUWA ba?".
Cikin rauni da ƙunar zuciya, ya miƙe tsaye hannunshi yasa ya kamo na Lamiɗo cikin tarin ƙuna da zafin rai da takaici yace.
"Na Amince, zanyi gasar na yarda, ka koma ka zauna".
Wani irin farin ciki ne ya ziyarci, zuƙatansu gaba ɗaya, sai dai kowa da irin manufar farin cikinsa.

Jin haka yasa fadawan janye labulen da sukayi musu.
Shi kuwa Lamiɗo hannunshi yasa ya kamo hannun Jabeer, cikin tsantsar farin ciki da al'fahari da ƙasaita ya fara taku, suna ratsawa cikin taron.
Kana fadawansu na biye dasu a baya.
Ɗanzagi yana.
"Takawarka lfy Sarki mai daraja Lamiɗo ɗan Lamiɗo jikan Joɗa. Gyara kimtsi".
A haka har suka isa cikin asalin dandamalin da aka jiƙashi jilak da ruwa, sabida hana ƙura wanzuwa.

Gaba ɗaya taron mutanen wurin maza da mata manya da yara, Jabeer suka zubawa ido, sabida duk wanda ya ganshi yaga sahihin Balarabe, mai kamala da nitsuwa, uwa uba kima da haiba, ƙwarjini shi ya cika dukkan idanun magautanshi dake wannan yanki,
yayinda masoyanshi ke taraddadin abinda zai faru.
A tsakiyar filin suka tsaya, hannunsu dake raƙe dana juna Lamiɗo ya ɗaga tare da fuskantarta gabas, kana ya juya yamma, ya kuma juyawa kudu da Arewa, sannan suka dawo tsakiyar filin,
Cikin ƙasaita, yace.
"Ga GARKUWAN FULANI, kuma daga Wannan nasarar da zaiyi a gasar nan,
Zai tabbatar GARKUWAR Masarautar Joɗa, GARKUWA kuma mai ikon zama inda yaso a cikin fada".
Dariya Bukar yayi kana ya ɗaga hannun Ba'ana da yaketa wani abu da ƙirjinshi kamar damisa,
Cikin isa da yaƙini da al'fahari yace.
"Mu kuma ga namu Garkuwan, da muke da tabbacin bai taɓa gasa ya faɗiba".
Sake hannunshi Lamiɗo yayi kana ya juya ya koma ya zauna, cikin rumfar da akayi musu masauƙin.
Al'ƙalin gasar ne yazo tsakiyar taro, kamar ko yaushe, hannun Ba'ana ya kamo, ya ɗaga sama, hakan yasa, gaba ɗaya makiɗa da mabusa suka ƙara sautin kiɗe-kiɗen su, wanda Jabeer ke jinsa har tsakiyar kansa, Allah ya sani, baya son hayani koda dai-dai da ƙwayar zarra ne, ga wani masifeffen fargaba da tsinkewar da zuciyarshi keyi, yanaji tamkar yasa hannunshi ya toshe kunnuwanshi.
Ɗan wani gajeren tsaki yaja sabida Allah ma ya sani baya son kallo, to kuma yanajin yadda idanun mutane ke yawo a jikinshi.

Shi kuwa al'ƙalin gasar, yana sake hannun Ba'ana yazo ya kamo hannun Jabeer,
Da sauri ya juyo ya kalleshi sabida kamo hannunshi da yayi sai yaji tamkar hannun jariri ya kamo dam laushi da taushin fatar, hannun sanyi ƙalau,
girgiza kanshi yayi cikin tausayawa, sabisa, ya za'ayi ace mai wannan taushin hannun fatarsa ta iya jurar azababbun bulali masu masifar zafi.
Ɗaga hannun Jabeer yayi sama.
Yana mai nunawa taron mutanen shi a matsayin dashi za'a gwabza.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, duk abinda akeyi idonshi na cikin ɗan siririn farin galashi mai garai-garai dake liƙe a fuskarshi,
Hannunshi kuma riƙe da carɓinshi, kana bakinshi ambaton sunan Allah.

Cikin tarin mamaki ya kalli,
Al'ƙalin gasar tare dasa hannunshi ya riƙe bakin al'kyabbar jikinshi cikin haɗe fuska yace.
"Me hakan!?". Cikin saurin rusunar da kai Al'ƙalin gasar yace.
"Za'a cire kayan jikin naka ne!".
Cikin tarin mamaki ya zazzaro ido waje, a baiyane yace.
"Akan me kenan, suturar da Allah yayi min a matsayin mulmi, in killace kaina, shine zaku yayemin a cikin dubban dubatan mutane?".
Cikin dakiya Al'ƙalin ya ɗan kalleshi domin kwarjinin Jabeer ya cika masa fuska cikin sanyi yace.
"Allah rene, ƙa'idar gasar ce, ba'ayi da kaya a jikin mutun sai ɗan kamfai, kawai ake bari a jikin mutun".
Cikin kufula da harzuƙa yace.
"To bada niba, Ni nan Muhammad Jabeer wallahi banyi lalacewar da zan tsaya tsirara a gaban jama'a ba".
Yana faɗin haka ya juya a fusashe, zai fita cikin taron.
Ganin hakane yasa Galadima, yayi saurin tasowa, kana Ɗan buram na biye dashi a baya, tareshi sukayi tare da kamo hannunshi.
Chapter 70 · 0% Book details