Sashe 75
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A hankali ta zauna, shiru tayi tana sauƙe shessheƙan kuka.
Cikin ƙuna da baƙin cikin rashin sa wancan ɗan birni mai fata kamar ta jariri kukanne ya sakar mishi fargaba,
cikin sanyi yace.
"Mata!".
Bata kalleshi ba kuma bata dena shessheƙan ba.
Kiranta ya kuma yi a karo na uku.
"Mata!".
Cikin disashewar muryar tace.
"Na'am".
Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau a hankali yace.
"Mata bakya so nane!?".
A bazata tambayarshi tazo mata,
ta ina kuma ta yaya zatace mishi bata sonshi, bayan tasan abin da yayi mata shekarun baya, dama fansar shi ta soshine kuma ta aureshi, da wanne bakin zatace mishi bata sonshi.
wasu zafafan hawaye masu ɗumi ta zubda.
Haƙiƙa ya Ba'ana mugune amman a iya saninta a kanta ya zama mugun, tunda sai wanda ya nuna baya sonta dashine yakewa mugunta,
Babbar matsalarshi mushirkine kuma baya salla.
Cikin rawan murya da kuka tace.
"A a Ya Ba'ana Ni bance bana sonka ba".
Da sauri yace.
"Uhhmmm to meyasa bakya ganin laifin Salmanu akan duk abinda yake min, ko dai shi kikeso ne Mata!?".
Da sauri ta jujjuya mishi kai sabida sanin ko jinkirin bashi amsa tayi zai iya yiwa Salmanu illa.
Cikin rawan murya tace.
"Bana son ka cutar da shine sabida, shi ya janye batun soyayyarsa gareni. Ka kuma sani karatu yake koya min amatsayinshi na wanda ya samu karantarwa a wata jami'a,
Yana sona da al'khairi kai kuma kana ƙinshi, ko dai ka manta ka ce min zaka so duk wanda yake sona da al'khairi yake kuma taimaka min".
Jiki a mace ya gyaɗa mata kai,
sai kuma ya rumtse idanunshi da yakejin suna cikowa da hawaye yace.
"Lokuta da dama sai inga kamar bakya farin cikin ganina, a madadin farin ciki sai inga tsorona cikin ƙwayar idonki."
Juyowa tayi gareshi da kyau cikin kuka tace.
"Ba kai ke bani tsoroba, abinda kakeyi ne yake sani tsoronka, ya Ba'ana ka bar wannan asirce-asircen babu kyau shirka ne, wanda yake ɗaya daga cikin manyan zunuban da Ubangiji ya haramtawa mumini yin tsafi haramun ne".
Kanshi ya jingina da jikin gini yana kallonta tamkar yau ya fara ganinta,
A hankali ya fara mgna cikin muryar da bata taɓa jin rauninta a muryarsa ba yace.
"Mata ina sonki, wallahi Allah kenan rantsuwar musulmai, ina sonki, son da ni kaina bansan adadinshi ba,
Duk abinda nakeyi a kanki nefa, Shatu ki min uzuri, na roƙeki kiyi min ɗa'ar riƙe tukuicin abinda nai miki a baya,
Ki soni koda rabin yadda nake sonki ne.
Kiji tausayina Shatu ina jin tsoron kada ƙaddara ta rabamu,".
Kekkyawar fuskarshi ta zubawa ido, tana gani. Irin kyan da Allah yayi mishi sai dai sam babu kyan hali ya zama kyan ɗan maciji.
Cikin sanyi tace.
"Ya Ba'ana tsoro kuma?".
Kai ya gyaɗa mata cikin sanyi yace.
"Eh sabida muddin aka rabamu, zan zamewa fulani babban ƙalubale a rayuwarsa, kuma duk wanda yayi sanadin rabuwata da ke, wallahi zaiga toskun rayuwar duniya, zaiyi dana sani, zan zama mugun zahiri. Na san ke Kum bakya son hakan.
Yau kuma fargaba na, yafi na baya yawaita da wannan jikan sarki ya iya daurewa azabar bulalina baiyi ƙollaba."
Wani irin ajiyan zuciya taja tare da cewa.
"Babu komai ya Ba'ana Ni dai ina tayi mana addu'an ALLAH yayi mana zaɓi mafi al'khairi a rayuwata, ya kuma shige min gaba a dukkan motsina".
Ido ya zuba mata babu ko ƙebtawa, cikin sanyi yace.
"Nine mafa al'khairinki Mata".
Da sauri tace.
"Baka saniba".
A zafafe yace.
"Na sani mana".
Cikin tsoro tace.
"Kai masanin gaibu ne kenan?".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Ehh kusan haka tunda nayi duba a kanki".
A hankali tace.
"Wa'iyazubillah. Duba ba gsky bane, zai iya maka ƙarya".
Hannu ya ɗaga mata da sauri kana ya nuna mata hanyar shiga gida.
A hankali ta tashi tsaye cikin sanyi tace.
"Allah ya baka haƙuri ya shiryeka".
Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin yin kuka.
Da sauri ya juyo cikin sanyi yace.
"Kada kiyi kukan mata, nayi haƙuri.
yanzu na fasa jiran Sai kin gama karatu ayi mana aure.
Duk randa wancan malamin ya dawo ya rama gasar Shaɗinsa. Za'a ɗaura auren mu a ranar, domin
Koda duk bulalin duniyar nan zai zabgeni dasu wlh bazaici nasara a kainaba domin idona ba idon da zai zubda hawaye a kanki bane bilali ɗaya nake tsoro kuma babu wanda yasan inda suke.
In kuwa aka samu wani akasin dama bazai samuba, to zan bar ƙasar nan zan koma ƙasar Cameroon can babban birnin Yahunde, inbi cikin Rugar wasu fulanin.
Sai dai ko bana nan duk wanda ya aureki ya auri ajalinsa."
Bata iya tanka mishiba, a haka ya juya ya tafi.
Kana ita kuma ta koma cikin gida.
A cikin masarautar Joɗa kuwa.
Sai da akayi sallan isha kafin.
Su Haroon suka dawo gida.
Suna tafe,
Abba da Lamiɗo da Galadima, da Dr Aliyu da kuma Sarkin Shaɗi.
Suna biye dasu a baya.
Kai tsaye wucewa sukayi har bedroom ɗin Jabeer har yanzu bacci yakeyi.
Sai dai tunda lokacin salla yayi yaketa jin baccin ba daɗi sai dai kuma Allah bai bashi ikon farkawa ba.
Dubashi sukayi tare da ƙara shafa mishi wasu magunguna kana suka fita suka tafi.
Hakama Gimbiya Aminatu tazo itama har ɗaki sai dai samunshi yana bacci yasa ta tafi.
Bayan fitanta ba daɗe Barrister Kamal da ɗan sa Sulaiman sukazo.
Suma har ciki suka shiga suka dubashi.
Kana suka tafi.
A ranan a daren gaba ɗaya mutanen masarautar kowa yaji lbrin abinda ya faru.
A falon su Jafar duk sukaci abinci.
Ganin dare ya tsalane yasa Juwairiyya jan hannun Jafar suka tafi.
Jalal, Jamil, Ya Hashim kuma sukayi musu saida safe kowa ya tafi side ɗin shi.
Jakadiyarsu kuwa itama ta nufi sashinta,
Ya zama dagashi sai Haroon.
Sha biyu da rabi dai-dai na dare.
Haroon zaune kan wata doguwar kujera irin ta sarakuna dake cikin ɗakin.
Waya yakeyi da Jannart,
yana konce ne dagashi sai boxes.
Waya sukeyi irin ta mosoyan da shaƙuwarsu tayi yawa,
Wani irin miƙa yayi wanda gaba ɗaya gabban jikinshi suka amsa.
Cikin tarin kasala da masifeffen shauƙi yace.
"Wash Allah na".
Cikin kashe murya da ta ingizo Bukatarsa tace.
"Ohhh sorry Ya Haroon meya faru gaya min me yasameka".
Cikin sakaliyar murya yace.
"Haroon yunwa yakeji".
Sam bata fahimci inda batunshi ya dosaba haka yasa cikin haɗa fuska tace,
"Ya Haroon ka dawo gida, shi Hamma Jabeer ba matace dashi ba, bare ya kula da cikinku, na kuma san in kuna Side ɗinsa ba wani zuwa wurin Aunty Juwairiyya zakuyiba, kuma itama fama takeyi da mijinta.
Ni gsky ka dawo Tsinako nasan Umaymah zata kular min da kai da kyau, ko kuma kazo Masarautarmu Leddi julɓe, nida Sitti mu kula da kai".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Masarauta Joɗo fa masarautace mai daraja, da karrama baƙo baki san asalin tarihin inda masarautar tasamu suna Joɗa bako.
Baby kada ki damu kular da muke samu ko sarki mai mata huɗu da kwarkawara biyar baya samu.
Tako wani sashi na gidan abinci hadimai ke kawowa Side ɗin Sheykh a ƙalla wani lokacin kusan abinci kala goma muke riska, kinsan fulani ba marowata bane.
Kawai matsalar wannan yunwar rashinki ne, a kusa yasa nake jina ina tashi sama kamar doki".
Cikin kunya da kauda zancen tace.
"Ya jikin Hamma Jabeer shugaban tuzuran ƙasar mu?".
A hankali ya juyo kanshi ya kalli bisa makeken gadon da Jabeer ke kai.
Da sauri ya katse kiran bayan yace mata.
"Ina zuwa".
Kan gadon ya nufa, jabeer ɗin yana ƙoƙarin tashi zaune.
Hannunshi daya miƙa zai taimaka mishi, ya buge cikin haɗe fuska yace.
"Yanzu ƙarfe nawa?".
Wayarshi dake hannunshi ya duba cikin zuba mishi ido yace.
"Ƙarfe ɗaya dai-dai".
Cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi kuka yace.
"Shine ka barni ina bacci kamar kafurin da bashi da addini.
Anyi sallan bamgrib baka tasheniba, anyi Isha'i baka tasheniba, daga wannan masifeffen bacci mara daɗi mai cike da mafarkai marasa daɗin da nasan rashin yin salla a lokacin sane ya jazamin su.
Iya wunin yau duk so kuke kuyi min asarar lokuta masu muhimmanci da daraja, kun sani na makara la'asar da magriba hakama isha."
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye,
Tare daci gaba da cewa.
"Da fari ansa ni na tsaya gaban jama'a da baiyana surata,
Aka ɗora min da duka kana, akasa na makara sallan la'asar,
Yanzu kuma mangriba da isha'inma kun barni ina baccin asara na makara, sabida baka san darajar yin salla a cikin jam'i da kuma yin ta cikin lokacin ta ba ko?".
Cikin taɓe baki Haroon yace.
"Kasan ai ni ba musulmi bane, ban san komaiba".
Harara ya dannawa Haroon tare da cewa.
"Kai ka gayawa kanka, Ni bana kafurta mutum, abinda na sani dai kai tsarin yahudu da nasarane,
To bari kaji, Ni bani da laifin komai sabida bacci nakeyi, mai bacci kuma al'ƙalami ya sauƙa kansa har sai ya farka.
Kai dake ganina ina bacci lokacin salla yayi idonka biyu baka tasheniba haƙƙin a kanka ya rataya."
Ya ƙarishe mgnar yana shiga bathroom tare da cewa.
"Ka cire idonka a kaina banza mai kallo kamar mayun wancan garin mugayen".
Murmushi Haroon yayi tare da komawa ya zauna bisa kujerar.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wonka ya kumayi da ruwan ɗumi,
kana ya kimtsa cikin irin suturun da yake ta'ammali dasu, in yana gida.
kana ya ɗaura wata farar jallabiya kai.
Sannan ya fito bayan ya shafa mai ya fesa turare.
Yana fita ya fara ramuwar sallan daya wuceshi yana bacci.
Haroon kuwa falo ya fita abincin da yasan zai iya ci ya kawo mishin
Cikin ƙuna da baƙin cikin rashin sa wancan ɗan birni mai fata kamar ta jariri kukanne ya sakar mishi fargaba,
cikin sanyi yace.
"Mata!".
Bata kalleshi ba kuma bata dena shessheƙan ba.
Kiranta ya kuma yi a karo na uku.
"Mata!".
Cikin disashewar muryar tace.
"Na'am".
Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau a hankali yace.
"Mata bakya so nane!?".
A bazata tambayarshi tazo mata,
ta ina kuma ta yaya zatace mishi bata sonshi, bayan tasan abin da yayi mata shekarun baya, dama fansar shi ta soshine kuma ta aureshi, da wanne bakin zatace mishi bata sonshi.
wasu zafafan hawaye masu ɗumi ta zubda.
Haƙiƙa ya Ba'ana mugune amman a iya saninta a kanta ya zama mugun, tunda sai wanda ya nuna baya sonta dashine yakewa mugunta,
Babbar matsalarshi mushirkine kuma baya salla.
Cikin rawan murya da kuka tace.
"A a Ya Ba'ana Ni bance bana sonka ba".
Da sauri yace.
"Uhhmmm to meyasa bakya ganin laifin Salmanu akan duk abinda yake min, ko dai shi kikeso ne Mata!?".
Da sauri ta jujjuya mishi kai sabida sanin ko jinkirin bashi amsa tayi zai iya yiwa Salmanu illa.
Cikin rawan murya tace.
"Bana son ka cutar da shine sabida, shi ya janye batun soyayyarsa gareni. Ka kuma sani karatu yake koya min amatsayinshi na wanda ya samu karantarwa a wata jami'a,
Yana sona da al'khairi kai kuma kana ƙinshi, ko dai ka manta ka ce min zaka so duk wanda yake sona da al'khairi yake kuma taimaka min".
Jiki a mace ya gyaɗa mata kai,
sai kuma ya rumtse idanunshi da yakejin suna cikowa da hawaye yace.
"Lokuta da dama sai inga kamar bakya farin cikin ganina, a madadin farin ciki sai inga tsorona cikin ƙwayar idonki."
Juyowa tayi gareshi da kyau cikin kuka tace.
"Ba kai ke bani tsoroba, abinda kakeyi ne yake sani tsoronka, ya Ba'ana ka bar wannan asirce-asircen babu kyau shirka ne, wanda yake ɗaya daga cikin manyan zunuban da Ubangiji ya haramtawa mumini yin tsafi haramun ne".
Kanshi ya jingina da jikin gini yana kallonta tamkar yau ya fara ganinta,
A hankali ya fara mgna cikin muryar da bata taɓa jin rauninta a muryarsa ba yace.
"Mata ina sonki, wallahi Allah kenan rantsuwar musulmai, ina sonki, son da ni kaina bansan adadinshi ba,
Duk abinda nakeyi a kanki nefa, Shatu ki min uzuri, na roƙeki kiyi min ɗa'ar riƙe tukuicin abinda nai miki a baya,
Ki soni koda rabin yadda nake sonki ne.
Kiji tausayina Shatu ina jin tsoron kada ƙaddara ta rabamu,".
Kekkyawar fuskarshi ta zubawa ido, tana gani. Irin kyan da Allah yayi mishi sai dai sam babu kyan hali ya zama kyan ɗan maciji.
Cikin sanyi tace.
"Ya Ba'ana tsoro kuma?".
Kai ya gyaɗa mata cikin sanyi yace.
"Eh sabida muddin aka rabamu, zan zamewa fulani babban ƙalubale a rayuwarsa, kuma duk wanda yayi sanadin rabuwata da ke, wallahi zaiga toskun rayuwar duniya, zaiyi dana sani, zan zama mugun zahiri. Na san ke Kum bakya son hakan.
Yau kuma fargaba na, yafi na baya yawaita da wannan jikan sarki ya iya daurewa azabar bulalina baiyi ƙollaba."
Wani irin ajiyan zuciya taja tare da cewa.
"Babu komai ya Ba'ana Ni dai ina tayi mana addu'an ALLAH yayi mana zaɓi mafi al'khairi a rayuwata, ya kuma shige min gaba a dukkan motsina".
Ido ya zuba mata babu ko ƙebtawa, cikin sanyi yace.
"Nine mafa al'khairinki Mata".
Da sauri tace.
"Baka saniba".
A zafafe yace.
"Na sani mana".
Cikin tsoro tace.
"Kai masanin gaibu ne kenan?".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Ehh kusan haka tunda nayi duba a kanki".
A hankali tace.
"Wa'iyazubillah. Duba ba gsky bane, zai iya maka ƙarya".
Hannu ya ɗaga mata da sauri kana ya nuna mata hanyar shiga gida.
A hankali ta tashi tsaye cikin sanyi tace.
"Allah ya baka haƙuri ya shiryeka".
Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin yin kuka.
Da sauri ya juyo cikin sanyi yace.
"Kada kiyi kukan mata, nayi haƙuri.
yanzu na fasa jiran Sai kin gama karatu ayi mana aure.
Duk randa wancan malamin ya dawo ya rama gasar Shaɗinsa. Za'a ɗaura auren mu a ranar, domin
Koda duk bulalin duniyar nan zai zabgeni dasu wlh bazaici nasara a kainaba domin idona ba idon da zai zubda hawaye a kanki bane bilali ɗaya nake tsoro kuma babu wanda yasan inda suke.
In kuwa aka samu wani akasin dama bazai samuba, to zan bar ƙasar nan zan koma ƙasar Cameroon can babban birnin Yahunde, inbi cikin Rugar wasu fulanin.
Sai dai ko bana nan duk wanda ya aureki ya auri ajalinsa."
Bata iya tanka mishiba, a haka ya juya ya tafi.
Kana ita kuma ta koma cikin gida.
A cikin masarautar Joɗa kuwa.
Sai da akayi sallan isha kafin.
Su Haroon suka dawo gida.
Suna tafe,
Abba da Lamiɗo da Galadima, da Dr Aliyu da kuma Sarkin Shaɗi.
Suna biye dasu a baya.
Kai tsaye wucewa sukayi har bedroom ɗin Jabeer har yanzu bacci yakeyi.
Sai dai tunda lokacin salla yayi yaketa jin baccin ba daɗi sai dai kuma Allah bai bashi ikon farkawa ba.
Dubashi sukayi tare da ƙara shafa mishi wasu magunguna kana suka fita suka tafi.
Hakama Gimbiya Aminatu tazo itama har ɗaki sai dai samunshi yana bacci yasa ta tafi.
Bayan fitanta ba daɗe Barrister Kamal da ɗan sa Sulaiman sukazo.
Suma har ciki suka shiga suka dubashi.
Kana suka tafi.
A ranan a daren gaba ɗaya mutanen masarautar kowa yaji lbrin abinda ya faru.
A falon su Jafar duk sukaci abinci.
Ganin dare ya tsalane yasa Juwairiyya jan hannun Jafar suka tafi.
Jalal, Jamil, Ya Hashim kuma sukayi musu saida safe kowa ya tafi side ɗin shi.
Jakadiyarsu kuwa itama ta nufi sashinta,
Ya zama dagashi sai Haroon.
Sha biyu da rabi dai-dai na dare.
Haroon zaune kan wata doguwar kujera irin ta sarakuna dake cikin ɗakin.
Waya yakeyi da Jannart,
yana konce ne dagashi sai boxes.
Waya sukeyi irin ta mosoyan da shaƙuwarsu tayi yawa,
Wani irin miƙa yayi wanda gaba ɗaya gabban jikinshi suka amsa.
Cikin tarin kasala da masifeffen shauƙi yace.
"Wash Allah na".
Cikin kashe murya da ta ingizo Bukatarsa tace.
"Ohhh sorry Ya Haroon meya faru gaya min me yasameka".
Cikin sakaliyar murya yace.
"Haroon yunwa yakeji".
Sam bata fahimci inda batunshi ya dosaba haka yasa cikin haɗa fuska tace,
"Ya Haroon ka dawo gida, shi Hamma Jabeer ba matace dashi ba, bare ya kula da cikinku, na kuma san in kuna Side ɗinsa ba wani zuwa wurin Aunty Juwairiyya zakuyiba, kuma itama fama takeyi da mijinta.
Ni gsky ka dawo Tsinako nasan Umaymah zata kular min da kai da kyau, ko kuma kazo Masarautarmu Leddi julɓe, nida Sitti mu kula da kai".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Masarauta Joɗo fa masarautace mai daraja, da karrama baƙo baki san asalin tarihin inda masarautar tasamu suna Joɗa bako.
Baby kada ki damu kular da muke samu ko sarki mai mata huɗu da kwarkawara biyar baya samu.
Tako wani sashi na gidan abinci hadimai ke kawowa Side ɗin Sheykh a ƙalla wani lokacin kusan abinci kala goma muke riska, kinsan fulani ba marowata bane.
Kawai matsalar wannan yunwar rashinki ne, a kusa yasa nake jina ina tashi sama kamar doki".
Cikin kunya da kauda zancen tace.
"Ya jikin Hamma Jabeer shugaban tuzuran ƙasar mu?".
A hankali ya juyo kanshi ya kalli bisa makeken gadon da Jabeer ke kai.
Da sauri ya katse kiran bayan yace mata.
"Ina zuwa".
Kan gadon ya nufa, jabeer ɗin yana ƙoƙarin tashi zaune.
Hannunshi daya miƙa zai taimaka mishi, ya buge cikin haɗe fuska yace.
"Yanzu ƙarfe nawa?".
Wayarshi dake hannunshi ya duba cikin zuba mishi ido yace.
"Ƙarfe ɗaya dai-dai".
Cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi kuka yace.
"Shine ka barni ina bacci kamar kafurin da bashi da addini.
Anyi sallan bamgrib baka tasheniba, anyi Isha'i baka tasheniba, daga wannan masifeffen bacci mara daɗi mai cike da mafarkai marasa daɗin da nasan rashin yin salla a lokacin sane ya jazamin su.
Iya wunin yau duk so kuke kuyi min asarar lokuta masu muhimmanci da daraja, kun sani na makara la'asar da magriba hakama isha."
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye,
Tare daci gaba da cewa.
"Da fari ansa ni na tsaya gaban jama'a da baiyana surata,
Aka ɗora min da duka kana, akasa na makara sallan la'asar,
Yanzu kuma mangriba da isha'inma kun barni ina baccin asara na makara, sabida baka san darajar yin salla a cikin jam'i da kuma yin ta cikin lokacin ta ba ko?".
Cikin taɓe baki Haroon yace.
"Kasan ai ni ba musulmi bane, ban san komaiba".
Harara ya dannawa Haroon tare da cewa.
"Kai ka gayawa kanka, Ni bana kafurta mutum, abinda na sani dai kai tsarin yahudu da nasarane,
To bari kaji, Ni bani da laifin komai sabida bacci nakeyi, mai bacci kuma al'ƙalami ya sauƙa kansa har sai ya farka.
Kai dake ganina ina bacci lokacin salla yayi idonka biyu baka tasheniba haƙƙin a kanka ya rataya."
Ya ƙarishe mgnar yana shiga bathroom tare da cewa.
"Ka cire idonka a kaina banza mai kallo kamar mayun wancan garin mugayen".
Murmushi Haroon yayi tare da komawa ya zauna bisa kujerar.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wonka ya kumayi da ruwan ɗumi,
kana ya kimtsa cikin irin suturun da yake ta'ammali dasu, in yana gida.
kana ya ɗaura wata farar jallabiya kai.
Sannan ya fito bayan ya shafa mai ya fesa turare.
Yana fita ya fara ramuwar sallan daya wuceshi yana bacci.
Haroon kuwa falo ya fita abincin da yasan zai iya ci ya kawo mishin