Sashe 126
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka kuwa akayi su Sara suka fara rabawa.
Ita kuwa Ummi ita da kanta da Hibba suka kai na sashin Gimbiya Aminatu.
Kana suka dawo da kuloli har uku na abincin sallan da Gimbiya Aminatu ta basu.
Kana ɗaya daga cikin tace na Sheykh ne a ajiye mishi.
Koda suka dawo samu sukayi su Saratu sun gama rabawa kab.
Kamar yadda Ummi ta tsara.
Har sun tattare ko ina sun gyara sun share sun goge sun tafi.
Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya kan dinning table ɗinsu cike yake da Foodflaks iri da kala abinci kala-kala.
Wani irin kallo Shatu tayiwa kulolin kana tayi murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa ta juya ta nufi tsakiyar falon.
A gaggauce sukayi wonka kowa yayi shirin idi.
Ƙarfe tara saura kwata duk suka fito falo.
Tuni lokacin kuma liman har ya fara huɗuba.
Su Jalal, Jamil Ya Jafar suna tsaye cikin shiga ta al'farma.
Karon forko dataga manyan kaya a jikin Jalal.
Sai kamanninshi da Hamma Jabeer ɗin nasu ya fito sak-sak kamar an tsaga kara hatta rashin yawan dariyarsu iri ɗaya ne.
Sai dai shi Sheykh ko yaushe zakaga lips ɗinshi na motsawa yana tasbihi saɓanin Jalal da zaka ganshi baki a tsuke.
Hibba ce ta fito cikin tarin farin ciki da son Jalal yayi murmushi tare da cewa.
"Masha Allah ya Jalal kayi kyau kafisu duka".
Ya Jafar dake karatu kamar ko yaushene ya kalli Shatu da Hibba da sukayi shigar atampa iri ɗaya da manyan hijabai har ƙasa ga sallaya da carbi a hannunsu sunyi matuƙar kyau, murmushi yayi musu kana ya juya yayi gaba.
Jamil ne yace.
"Aunty Shatu sai mun dawo, in munci abinci sai mu sharewa.
Oga, Dr, Garkuwa, Malam, akarmakallahu, Sheykh, mijin Sayyada, ɗin ɗakinshi".
Dariya sukayi dukansu yadda ya jero masa sunayen nashi.
Ummi dake cikin shiga ta al'farma ta miƙa tare da cewa mu tafi.
Suna fita suka rufe ƙofar.
Suka tafi masallacin. Masarautar Joɗa ɗan yin sallan idi.
Suna fita su mata sukayi gefen mata su kuwa maza sukayi gefen maza.
Bayan an idar da sallane kuma sai suka zagaya suka shigo ta asalin ƙofar sukayi yadda sunna ta koyar.
Suna dawowa kuwa a falo suka zube nan sukaci suka sha sukayi
haniƙan.
A dai-dai lokacin kuma su Sheykh dama sauran al'ummar Annabi duk an sauƙo sallan idi.
Suna ɗawafin ban kwana.
Sosai Sheykh ke baza ido ko zai sake ganin wancan mutumin amman ina hakan bai samuba.
Koda suka fito daga ɗawafin ban kwana.
Kai tsaye gidan Sheykh Abdulkareem suka wuce.
Nan yayi musu addu'o'in komawa lfy.
Kusan duk baƙin gidan a ranar suka bar gidan.
Da su Aunty Hafsat ma ranar suka juya Masco hakama Ibrahim.
Koda suka iso Airport kowa da inda ya nufa.
A nan Ibrahim ya ruggume Sheykh tare da ɗan dukan bayanshi yace.
"In Sha Allah Auren Haroon dani za'ayi".
Shima Sheykh ruggumeshi yayi gam-gam tare da cewa.
"Allah yasa, ina kewar rashinka a ƙasar mu".
Aunty Rahma ne tace.
"Kai jirgifa ba jiranku zaiba oga Sheykh".
Sakin juna sukayi kana kowa ya nufi inda jirgin ƙasarsa yake.
Bayan duk matafiya sun shiga, jirgin ƙasar Nigeria wanda zai sauƙa jihar Ɓadamaya.
A hankali ya zauna.
Ya Hashim na gefenshi.
Kasan cewar yana kusa da window ne, ya ɗan juya yana kallon mutanen daketa hada-hadar nufar inda jiragan ƙasar su jihohinsu suke.
Can cikin wasu ayarin mutane maza da mata ya hango wannan fuskar da ya gani.
Sun nufi can ciki suna tafiya yankin da jiragen ƙasar Cameroon suke.
Cikin tarin mamaki ya bishi da kallo tabbas badon jirginsu ya fara ƙugin tashiba da ya fita yaje ya tabbatar da fuskar dattijon da yake hangowa.
A haka dai suka ɓacewa ganinshi.
Kana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasarmu ta haihuwa.
Ana gida Nigeria kuwa cikin Jihar Ɓadamaya a Masarautar Joɗa.
Zaune suke a falon.
Shatu na waya da Junaidu nan yake ce mata,
Sun samu sauƙi dukansu.
Ance za'a sallamesu bayan salla.
Kuma harda ɗinkunan kayan salla akayi musu.
Bayan sun gama waya da shine ta kira Rafi'a.
Nan suka gaisa har ta bawa Ummi su gaisa.
Bayan ta bawa Ummi wayarne.
Jamil ya ɗan kalli agogon hannunshi a hankali ya miƙe tare da kallon Shatu yace.
"Muje mu gyara Side din boss kar ya dawo ya samu da datti".
Kai ta gyaɗa mishi kana ta amshi wayarta da Ummi ke miƙa mata.
tare da ce mata.
"Eh dan Allah Shatu tashi maza-maza kuje share wurin da kyau".
A hankali ta miƙe tare da cewa.
"To."
Hibba ce ta bisu a baya.
Jamil na gaba ita Shatu'n tana tsakiya.
Hibba na bayanta.
A haka suka shigo falon. Da komai na ciki yake fes-fes babu wani daddi ko ƙura ko hargitsewa, sabida an share falon safiyar yau, sai ƙamshi da sanyi ke tashi.
A hankali Jamil ya ɗan sa hannunshi tsakanin ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu sheƙin Daimond dake matsayin labulen Dinning area ɗin shi.
Ita dai Shatu ido ta zuba mushi,
ganin ya zaro key ɗin a cikinsu.
Ƙofar bedroom ɗin ya nufa tare da cewa.
"Muje."
To sukace kana suka biyo bayanshi.
Tana nazarin wurin da suke ajiye key ɗin.
Key ɗin ya saka cikin raminshi tare da murzawa.
Da sauri Shatu ta rumtse idanunta.
A hankali take jin zuciyarta na harbawa da sauri-sauri.
Shi kuwa Jamil tura ƙofar yayi bayan ya murɗa key ɗin ya buɗe.
Wani irin masifeffen harbawa da azaban ƙarfi zuciyar Shatu tayi.
Kutsa kai cikin Jamil yayi.
Tare dasa hannunshi jikin ginin a hankali ya kunna wutan ɗakin hasken ya gauraye ko ina,
jikin window ya wuce ya yaye labulen tare da buɗeglass ɗin.
Iskam cikin Garden ɗin dake bayan window wanda ɗawisu yake ciki.
Ya buso ɗakin.
Juyowa yayi ya kalli Shatu da ke tsaye bakin ƙofar.
"Ku shigo, in nuna miki yadda zakiyi mishi".
A hankali Hibba ta ratsa gefenta tare da cewa.
"Aunty Shatu mushiga".
Ido ta buɗe a hankali tare da bin bayan Hibba da kallo.
Kana ta ɗaga ƙafarta da kyar ta.
Taka cikin ɗakin, wani irin azabebben sarawa kanta yayi tamkar ana buga mata guduma a tsakiyar kan.
Cikin rawan ƙafa ta ɗaga ƙafafuwan ta,
Tayi taku huɗu zuwa biyar.
Ta kusa isa tsakiyar ɗakin.
Kenan.
Wani irin jujjuyawa taga kanta nayi.
Wasu irin ababe masu ban tsoro ta fara gani suna gilmawa cikin ƙwayar idanunta, shiyasa taketa jujjuya kanta.
Ta kalli gabas ta kalli yamma ta kalli kudu ta kalli arewa.
Hibba ce ta juyo tana kallonta jin Jamil nata mgna bata bashi amsaba.
Cikin sauri ta matso kusa da ita ganin yadda taketa jujjuya kai, ga idanunta da suka juye suka zama kamar harari garke, kana sai Rollin ball eyes ɗin ta take da sauri-sauri.
Cikin Mamaki Hibba tace.
"Aunty Shatu! Aunty Shatu!!".
Shiru ba amsa hakane yasa.
Jamil juyo kanshi ya kalli inda suke, da sauri ya juyo gaba ɗaya jikinshi ganin.
Wani irin karkarwa da jikin Shatu keyi.
Hibba kuwa da ƙarfi cikin tsoro tace.
"Aunty Shatu lfy kuwa?".
Ita kuwa Shatu, zuwa yanzu bata jinsu bata kuma fahimtar me suke faɗa hankalinta ya juye.
Cikin wani irin layi da rawan jiki tamkar mazari ta nufi tsakiyar ɗakin.
A nan ta tsaya gis gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Cikin tsananin tsoro da firgita.
"Hibba ta juya a guje tana cewa.
"Wayyo Ummi! Ummi!! Ummi!!! Kizo zakiga yadda Aunty Shatu keyi."
Ummi dake falo ita da Aunty Juwairiyya,
Kamar daga sama suke jiyo muryar Hibba tana rabka musu kira cikin firgici da razani.
Haka yasa Ummi da Aunty Juwairiyya miƙewa da sauri suka nufi corridor'n da suke jiyo muryar Hibba na fitowa.
Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar falon.
Cikin sauri Ummi ta ture Hibba ta wuce da gudu ta nufi cikin ɗakin.
Sabida jiyo muryar Jamil na cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahuwani'imal wakil. Ummi! Ummi!! Kizoooo".
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka shigo.
"Dai-dai lokacin kuma rawan da jikin Shatu keyi ya tsananta.
Wani irin kuka tasa tare da tafiya ƙasa luuu zata faɗi
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka tarota.
Bisa jikin Ummi ta faɗi hakan yasa itama Ummi tayi ƙasa ta zauna.
Babu abinda suke maimaitawa sai innalillahi wa innailaihi rajiun.
A kiɗime cikin tsananin gigita Jamil yace.
"Subahanallahi Ummi ta sumafa".
Jiki na rawa Aunty Juwairiyya ta juya da gudu babban falon ta fito tare da ɗauko goran ruwan sanyi.
Kana ta juyo a da sassarfa ta nufi can.
Hibba kuwa a gigice take gayawa Jalal da Ya Jafar abinda ke faru.
Da sauri ya Jafar ya tashi ya nufi can.
Jalal kuwa ya zauna dan ya lura Hibba tayi masifar tsorita.
A ɗakin nashi kuwa,
Shiru ta lafe jikin Ummi kamar babu rai koda.
Ummi ta yayyafa mata ruwan sanyi a fuskarta, a banza saida ta kuma watsa mata a karo na uku ne.
Kafin taja wani dogon numfashi cikin sanyi da tsoro Ummi tace.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ta sunkuyo kanta tana ɗan kiranta.
"Shatu! Shatu!! Shatu!!!".
Ba amsawa kuma bata buɗe ido ba,
A hankali ya Jafar ya zauna gefensu, karatun da yakeyi yaci gaba dayi.
Cikin sanyi ta buɗe idanunta.
Sai kuma ta yunƙura a hankali ta tashi zaune.
Da sauri Ummi ta zaro ido ganin yadda idanunta suka juye a murɗe.
Ita kuwa Shatu miƙewa tsaye tayi, cikin rawan sanyi da karkarwa, ta fara zagaya ɗakin a hankali taje baki Bathroom nanma buɗe ƙofar tayi ta shiga.
Jim kaɗan ta fito.
Idanun suna yadda suke sai dai.
Yanzu hawayene keta shatata babu ƙaƙƙautawa.
A hankali tazo bakin gadon.
Sai kuma kawai sukaga ta faɗa kan gadon a sune!
Wannan shine tashin hankali da ba'a samishi rana.
Da gudu suka kumayi kanta, cikin firgici da tsananin tsoro Ummi ta ƙara yayyafa mata ruwan.
Amman shiru, haka suka tsaya cirko-cirko, shi kuwa Ya Jafar sai gashi yana karatu yana kuka kamar dai yadda yakeyi kafin a auro Shatu a masarautar Joɗa in Sheykh baya nan.
Gaba ɗaya sun birkice sunma rasa me zasuyi.
Ita kuwa Ummi ita da kanta da Hibba suka kai na sashin Gimbiya Aminatu.
Kana suka dawo da kuloli har uku na abincin sallan da Gimbiya Aminatu ta basu.
Kana ɗaya daga cikin tace na Sheykh ne a ajiye mishi.
Koda suka dawo samu sukayi su Saratu sun gama rabawa kab.
Kamar yadda Ummi ta tsara.
Har sun tattare ko ina sun gyara sun share sun goge sun tafi.
Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya kan dinning table ɗinsu cike yake da Foodflaks iri da kala abinci kala-kala.
Wani irin kallo Shatu tayiwa kulolin kana tayi murmushin da ita kaɗai tasan ma'anarsa ta juya ta nufi tsakiyar falon.
A gaggauce sukayi wonka kowa yayi shirin idi.
Ƙarfe tara saura kwata duk suka fito falo.
Tuni lokacin kuma liman har ya fara huɗuba.
Su Jalal, Jamil Ya Jafar suna tsaye cikin shiga ta al'farma.
Karon forko dataga manyan kaya a jikin Jalal.
Sai kamanninshi da Hamma Jabeer ɗin nasu ya fito sak-sak kamar an tsaga kara hatta rashin yawan dariyarsu iri ɗaya ne.
Sai dai shi Sheykh ko yaushe zakaga lips ɗinshi na motsawa yana tasbihi saɓanin Jalal da zaka ganshi baki a tsuke.
Hibba ce ta fito cikin tarin farin ciki da son Jalal yayi murmushi tare da cewa.
"Masha Allah ya Jalal kayi kyau kafisu duka".
Ya Jafar dake karatu kamar ko yaushene ya kalli Shatu da Hibba da sukayi shigar atampa iri ɗaya da manyan hijabai har ƙasa ga sallaya da carbi a hannunsu sunyi matuƙar kyau, murmushi yayi musu kana ya juya yayi gaba.
Jamil ne yace.
"Aunty Shatu sai mun dawo, in munci abinci sai mu sharewa.
Oga, Dr, Garkuwa, Malam, akarmakallahu, Sheykh, mijin Sayyada, ɗin ɗakinshi".
Dariya sukayi dukansu yadda ya jero masa sunayen nashi.
Ummi dake cikin shiga ta al'farma ta miƙa tare da cewa mu tafi.
Suna fita suka rufe ƙofar.
Suka tafi masallacin. Masarautar Joɗa ɗan yin sallan idi.
Suna fita su mata sukayi gefen mata su kuwa maza sukayi gefen maza.
Bayan an idar da sallane kuma sai suka zagaya suka shigo ta asalin ƙofar sukayi yadda sunna ta koyar.
Suna dawowa kuwa a falo suka zube nan sukaci suka sha sukayi
haniƙan.
A dai-dai lokacin kuma su Sheykh dama sauran al'ummar Annabi duk an sauƙo sallan idi.
Suna ɗawafin ban kwana.
Sosai Sheykh ke baza ido ko zai sake ganin wancan mutumin amman ina hakan bai samuba.
Koda suka fito daga ɗawafin ban kwana.
Kai tsaye gidan Sheykh Abdulkareem suka wuce.
Nan yayi musu addu'o'in komawa lfy.
Kusan duk baƙin gidan a ranar suka bar gidan.
Da su Aunty Hafsat ma ranar suka juya Masco hakama Ibrahim.
Koda suka iso Airport kowa da inda ya nufa.
A nan Ibrahim ya ruggume Sheykh tare da ɗan dukan bayanshi yace.
"In Sha Allah Auren Haroon dani za'ayi".
Shima Sheykh ruggumeshi yayi gam-gam tare da cewa.
"Allah yasa, ina kewar rashinka a ƙasar mu".
Aunty Rahma ne tace.
"Kai jirgifa ba jiranku zaiba oga Sheykh".
Sakin juna sukayi kana kowa ya nufi inda jirgin ƙasarsa yake.
Bayan duk matafiya sun shiga, jirgin ƙasar Nigeria wanda zai sauƙa jihar Ɓadamaya.
A hankali ya zauna.
Ya Hashim na gefenshi.
Kasan cewar yana kusa da window ne, ya ɗan juya yana kallon mutanen daketa hada-hadar nufar inda jiragan ƙasar su jihohinsu suke.
Can cikin wasu ayarin mutane maza da mata ya hango wannan fuskar da ya gani.
Sun nufi can ciki suna tafiya yankin da jiragen ƙasar Cameroon suke.
Cikin tarin mamaki ya bishi da kallo tabbas badon jirginsu ya fara ƙugin tashiba da ya fita yaje ya tabbatar da fuskar dattijon da yake hangowa.
A haka dai suka ɓacewa ganinshi.
Kana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasarmu ta haihuwa.
Ana gida Nigeria kuwa cikin Jihar Ɓadamaya a Masarautar Joɗa.
Zaune suke a falon.
Shatu na waya da Junaidu nan yake ce mata,
Sun samu sauƙi dukansu.
Ance za'a sallamesu bayan salla.
Kuma harda ɗinkunan kayan salla akayi musu.
Bayan sun gama waya da shine ta kira Rafi'a.
Nan suka gaisa har ta bawa Ummi su gaisa.
Bayan ta bawa Ummi wayarne.
Jamil ya ɗan kalli agogon hannunshi a hankali ya miƙe tare da kallon Shatu yace.
"Muje mu gyara Side din boss kar ya dawo ya samu da datti".
Kai ta gyaɗa mishi kana ta amshi wayarta da Ummi ke miƙa mata.
tare da ce mata.
"Eh dan Allah Shatu tashi maza-maza kuje share wurin da kyau".
A hankali ta miƙe tare da cewa.
"To."
Hibba ce ta bisu a baya.
Jamil na gaba ita Shatu'n tana tsakiya.
Hibba na bayanta.
A haka suka shigo falon. Da komai na ciki yake fes-fes babu wani daddi ko ƙura ko hargitsewa, sabida an share falon safiyar yau, sai ƙamshi da sanyi ke tashi.
A hankali Jamil ya ɗan sa hannunshi tsakanin ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu sheƙin Daimond dake matsayin labulen Dinning area ɗin shi.
Ita dai Shatu ido ta zuba mushi,
ganin ya zaro key ɗin a cikinsu.
Ƙofar bedroom ɗin ya nufa tare da cewa.
"Muje."
To sukace kana suka biyo bayanshi.
Tana nazarin wurin da suke ajiye key ɗin.
Key ɗin ya saka cikin raminshi tare da murzawa.
Da sauri Shatu ta rumtse idanunta.
A hankali take jin zuciyarta na harbawa da sauri-sauri.
Shi kuwa Jamil tura ƙofar yayi bayan ya murɗa key ɗin ya buɗe.
Wani irin masifeffen harbawa da azaban ƙarfi zuciyar Shatu tayi.
Kutsa kai cikin Jamil yayi.
Tare dasa hannunshi jikin ginin a hankali ya kunna wutan ɗakin hasken ya gauraye ko ina,
jikin window ya wuce ya yaye labulen tare da buɗeglass ɗin.
Iskam cikin Garden ɗin dake bayan window wanda ɗawisu yake ciki.
Ya buso ɗakin.
Juyowa yayi ya kalli Shatu da ke tsaye bakin ƙofar.
"Ku shigo, in nuna miki yadda zakiyi mishi".
A hankali Hibba ta ratsa gefenta tare da cewa.
"Aunty Shatu mushiga".
Ido ta buɗe a hankali tare da bin bayan Hibba da kallo.
Kana ta ɗaga ƙafarta da kyar ta.
Taka cikin ɗakin, wani irin azabebben sarawa kanta yayi tamkar ana buga mata guduma a tsakiyar kan.
Cikin rawan ƙafa ta ɗaga ƙafafuwan ta,
Tayi taku huɗu zuwa biyar.
Ta kusa isa tsakiyar ɗakin.
Kenan.
Wani irin jujjuyawa taga kanta nayi.
Wasu irin ababe masu ban tsoro ta fara gani suna gilmawa cikin ƙwayar idanunta, shiyasa taketa jujjuya kanta.
Ta kalli gabas ta kalli yamma ta kalli kudu ta kalli arewa.
Hibba ce ta juyo tana kallonta jin Jamil nata mgna bata bashi amsaba.
Cikin sauri ta matso kusa da ita ganin yadda taketa jujjuya kai, ga idanunta da suka juye suka zama kamar harari garke, kana sai Rollin ball eyes ɗin ta take da sauri-sauri.
Cikin Mamaki Hibba tace.
"Aunty Shatu! Aunty Shatu!!".
Shiru ba amsa hakane yasa.
Jamil juyo kanshi ya kalli inda suke, da sauri ya juyo gaba ɗaya jikinshi ganin.
Wani irin karkarwa da jikin Shatu keyi.
Hibba kuwa da ƙarfi cikin tsoro tace.
"Aunty Shatu lfy kuwa?".
Ita kuwa Shatu, zuwa yanzu bata jinsu bata kuma fahimtar me suke faɗa hankalinta ya juye.
Cikin wani irin layi da rawan jiki tamkar mazari ta nufi tsakiyar ɗakin.
A nan ta tsaya gis gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Cikin tsananin tsoro da firgita.
"Hibba ta juya a guje tana cewa.
"Wayyo Ummi! Ummi!! Ummi!!! Kizo zakiga yadda Aunty Shatu keyi."
Ummi dake falo ita da Aunty Juwairiyya,
Kamar daga sama suke jiyo muryar Hibba tana rabka musu kira cikin firgici da razani.
Haka yasa Ummi da Aunty Juwairiyya miƙewa da sauri suka nufi corridor'n da suke jiyo muryar Hibba na fitowa.
Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar falon.
Cikin sauri Ummi ta ture Hibba ta wuce da gudu ta nufi cikin ɗakin.
Sabida jiyo muryar Jamil na cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahuwani'imal wakil. Ummi! Ummi!! Kizoooo".
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka shigo.
"Dai-dai lokacin kuma rawan da jikin Shatu keyi ya tsananta.
Wani irin kuka tasa tare da tafiya ƙasa luuu zata faɗi
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka tarota.
Bisa jikin Ummi ta faɗi hakan yasa itama Ummi tayi ƙasa ta zauna.
Babu abinda suke maimaitawa sai innalillahi wa innailaihi rajiun.
A kiɗime cikin tsananin gigita Jamil yace.
"Subahanallahi Ummi ta sumafa".
Jiki na rawa Aunty Juwairiyya ta juya da gudu babban falon ta fito tare da ɗauko goran ruwan sanyi.
Kana ta juyo a da sassarfa ta nufi can.
Hibba kuwa a gigice take gayawa Jalal da Ya Jafar abinda ke faru.
Da sauri ya Jafar ya tashi ya nufi can.
Jalal kuwa ya zauna dan ya lura Hibba tayi masifar tsorita.
A ɗakin nashi kuwa,
Shiru ta lafe jikin Ummi kamar babu rai koda.
Ummi ta yayyafa mata ruwan sanyi a fuskarta, a banza saida ta kuma watsa mata a karo na uku ne.
Kafin taja wani dogon numfashi cikin sanyi da tsoro Ummi tace.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ta sunkuyo kanta tana ɗan kiranta.
"Shatu! Shatu!! Shatu!!!".
Ba amsawa kuma bata buɗe ido ba,
A hankali ya Jafar ya zauna gefensu, karatun da yakeyi yaci gaba dayi.
Cikin sanyi ta buɗe idanunta.
Sai kuma ta yunƙura a hankali ta tashi zaune.
Da sauri Ummi ta zaro ido ganin yadda idanunta suka juye a murɗe.
Ita kuwa Shatu miƙewa tsaye tayi, cikin rawan sanyi da karkarwa, ta fara zagaya ɗakin a hankali taje baki Bathroom nanma buɗe ƙofar tayi ta shiga.
Jim kaɗan ta fito.
Idanun suna yadda suke sai dai.
Yanzu hawayene keta shatata babu ƙaƙƙautawa.
A hankali tazo bakin gadon.
Sai kuma kawai sukaga ta faɗa kan gadon a sune!
Wannan shine tashin hankali da ba'a samishi rana.
Da gudu suka kumayi kanta, cikin firgici da tsananin tsoro Ummi ta ƙara yayyafa mata ruwan.
Amman shiru, haka suka tsaya cirko-cirko, shi kuwa Ya Jafar sai gashi yana karatu yana kuka kamar dai yadda yakeyi kafin a auro Shatu a masarautar Joɗa in Sheykh baya nan.
Gaba ɗaya sun birkice sunma rasa me zasuyi.