Sashe 13
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai tsaye garin Shikan suka nufa.
Tafiyar ba wata mai nisa bace daga cikin birnin Joɗa zuwa Shikan, cikin mitina kaɗan suka isa,
Ƙarfe biyara da miti biyar suka isa.
Cikin Shikan a nan tasa drever ya tsaya ta sayi Junainah sweet.
Biyar da mintuna goma dai-dai suka isa kwanar mashigar Rukarsu Rugar Bani.
Cikin tsoron kada Ba'ana yaga wani yazo ya sauketa ya masa rashin mutunci, tace.
Ya sauketa a nan ba musu ya sauketa dan ai inda sabo ya saba.
Tana fita taja jakarta, ta rataya kana ta gyara tarhan da tayiwa kanta.
Shi kuma ya juya ya tafi.
A hankali ta zubawa yankin garin nasu ido, ko ina yayi kore shar, yabanya da ni'imar damina ta wadaci ko ina, wata iriyar sassanyar iska mai daɗin ke ratsa mata jiki da zuciya.
Ajiyan zuciya ta sauƙe a hankali tare da lumshe idanunta kana ta buɗe hannayenta cikin begen gida tace.
"Rayuwar ƙauye mu akwai daɗeeee".
Ido ta buɗe tana kallon tako ina makiyayen rugarsune suketa dawowa daga kiwo,
Dabbobi saffan-saffan sunata dawowa,
garin yayi lum ga wani hadari mai ƙarfi daya keto, daga ƙasan dutsen da yayiwa Kyauyen ko ince Rugar Bani ƙawanya, a hankali take taku tana bin kan faffaɗan hanyan da makiyayan sukayishi bi ma'ana burtali kenan.
Taku take yayinda gefen hagunta wutsiyar kogin Shikan ne konce iya ganinta,
gefen dama kuwa Garden ɗinsune mai girma wanda yasa sanyin wurin yake yawaita, sauri ta ɗan farayi sabida akwai ƴar tazara kana kuma gashi magriba ta karato.
Tana cikin tafiya tana rataye da jakarta, kamar daga sama taga wulgawar inuwan mutun, cikin sauri ta zaro idonta ta kalli gefen hagu da damanta,
Ba kowa ganin hakane yasa taci gaba da tafiyarta cikin dakiya, taku uku tayi ana huɗu taji ansa hannu an amshi jakarta, da sauri ta juyo ta kalli gefen da aka amshi jakar.
Babu kowa a wurin kuma ga jakarta a rataye ita ɗaya tana binta suna tafiya a jere.
Cikin wani irin fargaba tsaro kaɗuwa da tsananin firgita ta....!
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 6
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*FREE PAGE*
*Kada dai ku manta har yanzu Free page kuke samu, wanda zamu datseshi cikin ko wanne lokacin, hamzarta ku biya darinki uku kacal ko 1k ga mai dama da niya, domin samun cikekken labarin daki-daki cikin salama. Turo kuɗin ta asusuna na Jaiz. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidan biyanki ta layina 09097853276. In ya zama larura ba halin turawa ta ac turo katin mtn na ɗari uku, ko na 1k ɗin domin ci gaban lbrin GARKUWA. Sayan na gari maida kuɗi gida. Ina mai yi muku fatan al'khairi masoyana makaranta, ina sonku domin Allah ina fatan kyautata alaƙa ta da kowa sabida nasan ko ina raye watarana zan zama tarihi a duniyar marubuta, sabida yauda gobe ta wuce watsa, in ba mutuwa akwai tsufa. Kana dole watan wata rana gwanayen zasu zama tsoffin hannu kana yan koyo na yanzu su zama gwanayen, domin da babu yan koyo tabbas da gwanayen sun ƙare, inada fata da burin ganin al'ƙaluman Adabi sun inƙanta baki ɗayansu ba nawa kaɗaiba, tsarkake rubutu ki/ka domin kece madubin wata marubuciya da zata iya tasowa nan gaba.Ina mai muku fatan al'khairi🙏🏻🤝🏻🥰😘makaranta da marubuta*
Cikin firgita da tsoron tace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil, lailaha'illalahu Muhammadurasulillahi sallahu'alaihi wasallam Auzubikalimatillahi ta'ammati min sharrin ma khalaƙa Allahum...".
Da sauri ta koma da baya ba tare da karisa addu'ar ƙarshen data faro ɗinba. Ganin Ba'ana ne tsaye a gabanta cikin wata iriyar dariya yace.
"Ke ki nitsu masoyinki ne ke gadinki, gsky *Mata* dole in rage miki wannan tsoron, domin matar Ba'ana bazata kasance matsoraciya ba, dole in ƙara tsumaki in dafaki da kyau, ta yadda idanunki zasu buɗe da kyau".
Cikin karkarwar da bai bar jikintaba tace.
"Bana so. Ni ka barnin da tsorona, nifa macece ba namiji irinka ba, kaine ke shiga daji da tsaunuka kake buƙatar wani abu ya kare ka".
Da sauri Ba'ana farin kekyawan babarbare ya matso gareta cikin shigar fulanin da ya zame mushi sutura yace.
"Mata ke bakya buƙatar kariyar ne?."
Da sauri ta gyaɗa mishi kai tare da cewa.
"Ni na yarda cewa addu'a'u saiful muminin ne, kuma shi na riƙe, so bana buƙatar waɗannan asirce asircen".
Murmushi yayi tare da murza ƙafarshi ta hagu sai gashi ya zama kamar inuwa ba mutun ya ɓacewa ganinta ɓat.
Da sauri ta rufe idanunta tare da cewa.
"Bana so ina tsoro ka dena caccanza kamanni a gabana".
Da sauri tayi baya ganinshi gab da ita,
Dariyar ƙeta yayi tare da cewa.
"Baga irinta nanba, idonki baya iya ganin komai, dole zan ƙara haɗaki irin haɗin da zaki ke banbance mai layar ɓata data zana da jingina bongo da dama duk mutun mai juyewa i zuwa wata halittar".
Ya karishe mgnar yana nuna mata hanya alamun su tafi.
A hankali suka jera suna tafiya a tare.
Allah ya sani Ba'ana yana masifar son Shatu tun tana ƴar ƙaramar yarinya, yana sonto irin sonda ko ƙudane in ya sauƙa kanta in dai namiji ne to zai kasheshi, ganinta kusa dashi kawai yana sashi jin daɗi, duk muguntarsa baya yi mata, duk duniya babu wanda Ba'ana ya yarda da shi bare yasan sirrin makarin sihirurrukan dake jikinshi. Ba'ana mutunne da yake tamkar al'janu sabida yawan ta'ammali da sihiri kai harma da tsafi, Ba'ana riƙeƙƙen tantirin ɓarawone wanda ya buwayi Fulani al'ummar Afirka gaba ɗayanta, da sace-sacen dabbobinshi, muddin ya ƙella ido yaga garken shanunka yayi mishi, to tazarar kilo mita talatin da biyar yake tsayuwa da garken, yayi FITO ɗaya tak, wallahi duk sihirin kafiyar garkenka zai kunce kuma duk inda yayi shanayenka zasu bishi a baya da kuma wannan tazarar, da zaran kasa Hukuma cikin zancen kuma yana burza layar ɓatanshi dashi da dabbobin duk zasu ɓace.
Duk garken da yaga yayi mishi to sai ya kwashesu tsan da wannan ya tara dukiyar dabbobin da shi kanshi baisan adadinshiba babu ƙasar da bashi da makiyayanshi kamar su.
Chadi, Nijer, Cameroon, Ghana, Gabon, Maroco, Senigal, da dai sauran kasashen makusantanmu kuma masu dabbobi, hikimar da yakeyi, muddin ya saci shanayen ƙasar Niger to sai ya cillasu ƙasar Senegal, in kuma makiyayanshi na ƙasar Sanigal sukayi sata to sai ya turo shanayen ƙasar Gabon, haka dai yake banbance mazauninsu.
Sai dai garin zamansa ɗaya ne Rugar Bani, inda nan aka haifeshi mahaifinshi Bukar wanda babarbaren Norba ne saye da sayar da kanwane ya ajiyeshi cikin rugar FULANI shiyasa ya zama dilan saida kanwa, sabida dole duk bafulatani makiyayi yana ta'ammali da kanwa dan ana zubawa dabobbi susha a ruwa ko asa musu a dusa ko harawa yana musu mgni.
Ba'ana ya shiga cikin Fulani ya saje dasu.
Yayinda hakan ya bashi damar da duk duniya ake ɗaukarshi matsayin bafulatani, koda yake hakan baya rasa nasaba, da kallon da mutanen duniya sukewa duk mutumin da akaga shanu, tumaki a gabanshi tofa ko wacce gabilace shi, ya zama bafulatani, wanda kuma sam ba haka abin yakeba.
Mahaifiyar Ba'ana ɗaya daga cikin ƙabilar ɓachama ce,
wacce Bukar ya aura tana a matsayinta na anniya, koda kuwa suka haihu ɗan su. Bukar ya rinjaye ta Ba'ana ya kasance musulmi, sai daifa a baɗini baƙar zuciyarsa da aiyikansa na kafuraine, sata kuwa a wurin babarsa ya gada.
Ba'ana kekyawan mutun ne ajin forko wanda ya gaji wannan kyan ne a kakarshi mahaifiyar babanshi wacce take shuwa Arabce, koda maƙiyinshi yasan tabbas Ba'ana kekyawane.
A duniya kab Shatu ce tasan sirrinshi ciki da woje,
sai daifa bata san yana sataba, amman duk wani abu na asiri da yadda za'a karya asirin da kuma yadda yake juyewa duk ta sani.
To hakanne yasa sam bata fatan ya zama miji a gareta bare uban ƴaƴanta, sai dai babu yadda ta iya. Domin ya mata babbar rana a rayuwarta ya mata taimakon da yasa aka ɗaukar mishi al'ƙawarin aurenta.
Gashi kuma duk wanda yace yana sonta karshenshi mutuwa, kuma yana gaya mata cewa duk wanda yace zai rabashi da ita zai kasheshi Wannan yasa kullum addu'ar shirya take mishi da fatan Allah ya rabata dashi lfy innshi ba mai shiryuwa bane.
Tafiya sukeyi cikin nitsuwa a hankali, murmushi yaketayi cikin so da ƙaunarta yace.
"Mata ya akayi na ganki da ƙaramar jaka?".
Kai ta ɗan gyaɗa mishi tana kallon kekyawar fuskarshi, cikin murmushi yace.
"Kece kika ajiyeni a kasar Kautal a Rugar Bani, kina ƙare karatunki zamuyi aurenmu in ɗaukeki mubar ƙasar, kawai dolece tasa na hakura da batun aurenmu kiyi karatu, dan naga kina son karatun kuma nasan zaki karantar mana da yaranmu, kuma ina son ki zama babbar lawyer mai zaman kanta, sai ki zama lawyer na koda watan-wata rana, rana zata ɓacin min".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kamar yaune zan kare karatun, Ya Ba'ana".
Kanshi ya rausayar tare da gyara riƙon igiyar jakar da yayi, kana yace.
"Allah ya nuna min wannan lokacin, in sha Allah sadakin aurenki Garken shanu ɗari zan bada".
Cikin mmki ta zaro ido tare da cewa.
"Kai Ya Ba'ana garke ɗari bama shanu ɗariba, ya bana ina zaka samu wannan shanun kaida garken naku ko shanu hamsin bai cikaba".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Allah zai kawosu kafin lokacin auren namu".
A hankali tace.
"Allah ya kawosu".
Amin Amin yace tare da ɗan juyowa ya kalleta, murmushi yayi mata, kana ya miƙo mata jakar tata cikin so yace.
"Mun iso bakin Gari ki shiga.
Ni zan koma baya dama rakoki nazo nayi kar shaiɗanun bakin kogi su cutarmin dake".
Kai ta ɗan jinjina tare da cewa.
"Ya Ba'ana lokacin sallah ya kusa fa ai gwara ka shigo sai kayi salla ka koma".
Bakinshi ya ɗan tabe tare da cewa.
"No bar sallan nan sai bayan mako biyu ina ƙara dafa jikinane kuma in nayi al'walan duk aikin zai karye".
Dafa kanta tayi da sauri tare da cewa.
"Wa'iyazubillah Wayyo Allah na Ya Ba'ana ka gane mana wannan abin da kakeyi shirka ne,".
Kanshi ya jujjuya tare da cewa.
"Shiga cikin gari zanzo musha hira da daren".
To kawai tace mishi ta juya ta nufi cikin garin.
Tafiyar ba wata mai nisa bace daga cikin birnin Joɗa zuwa Shikan, cikin mitina kaɗan suka isa,
Ƙarfe biyara da miti biyar suka isa.
Cikin Shikan a nan tasa drever ya tsaya ta sayi Junainah sweet.
Biyar da mintuna goma dai-dai suka isa kwanar mashigar Rukarsu Rugar Bani.
Cikin tsoron kada Ba'ana yaga wani yazo ya sauketa ya masa rashin mutunci, tace.
Ya sauketa a nan ba musu ya sauketa dan ai inda sabo ya saba.
Tana fita taja jakarta, ta rataya kana ta gyara tarhan da tayiwa kanta.
Shi kuma ya juya ya tafi.
A hankali ta zubawa yankin garin nasu ido, ko ina yayi kore shar, yabanya da ni'imar damina ta wadaci ko ina, wata iriyar sassanyar iska mai daɗin ke ratsa mata jiki da zuciya.
Ajiyan zuciya ta sauƙe a hankali tare da lumshe idanunta kana ta buɗe hannayenta cikin begen gida tace.
"Rayuwar ƙauye mu akwai daɗeeee".
Ido ta buɗe tana kallon tako ina makiyayen rugarsune suketa dawowa daga kiwo,
Dabbobi saffan-saffan sunata dawowa,
garin yayi lum ga wani hadari mai ƙarfi daya keto, daga ƙasan dutsen da yayiwa Kyauyen ko ince Rugar Bani ƙawanya, a hankali take taku tana bin kan faffaɗan hanyan da makiyayan sukayishi bi ma'ana burtali kenan.
Taku take yayinda gefen hagunta wutsiyar kogin Shikan ne konce iya ganinta,
gefen dama kuwa Garden ɗinsune mai girma wanda yasa sanyin wurin yake yawaita, sauri ta ɗan farayi sabida akwai ƴar tazara kana kuma gashi magriba ta karato.
Tana cikin tafiya tana rataye da jakarta, kamar daga sama taga wulgawar inuwan mutun, cikin sauri ta zaro idonta ta kalli gefen hagu da damanta,
Ba kowa ganin hakane yasa taci gaba da tafiyarta cikin dakiya, taku uku tayi ana huɗu taji ansa hannu an amshi jakarta, da sauri ta juyo ta kalli gefen da aka amshi jakar.
Babu kowa a wurin kuma ga jakarta a rataye ita ɗaya tana binta suna tafiya a jere.
Cikin wani irin fargaba tsaro kaɗuwa da tsananin firgita ta....!
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 6
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*FREE PAGE*
*Kada dai ku manta har yanzu Free page kuke samu, wanda zamu datseshi cikin ko wanne lokacin, hamzarta ku biya darinki uku kacal ko 1k ga mai dama da niya, domin samun cikekken labarin daki-daki cikin salama. Turo kuɗin ta asusuna na Jaiz. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidan biyanki ta layina 09097853276. In ya zama larura ba halin turawa ta ac turo katin mtn na ɗari uku, ko na 1k ɗin domin ci gaban lbrin GARKUWA. Sayan na gari maida kuɗi gida. Ina mai yi muku fatan al'khairi masoyana makaranta, ina sonku domin Allah ina fatan kyautata alaƙa ta da kowa sabida nasan ko ina raye watarana zan zama tarihi a duniyar marubuta, sabida yauda gobe ta wuce watsa, in ba mutuwa akwai tsufa. Kana dole watan wata rana gwanayen zasu zama tsoffin hannu kana yan koyo na yanzu su zama gwanayen, domin da babu yan koyo tabbas da gwanayen sun ƙare, inada fata da burin ganin al'ƙaluman Adabi sun inƙanta baki ɗayansu ba nawa kaɗaiba, tsarkake rubutu ki/ka domin kece madubin wata marubuciya da zata iya tasowa nan gaba.Ina mai muku fatan al'khairi🙏🏻🤝🏻🥰😘makaranta da marubuta*
Cikin firgita da tsoron tace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil, lailaha'illalahu Muhammadurasulillahi sallahu'alaihi wasallam Auzubikalimatillahi ta'ammati min sharrin ma khalaƙa Allahum...".
Da sauri ta koma da baya ba tare da karisa addu'ar ƙarshen data faro ɗinba. Ganin Ba'ana ne tsaye a gabanta cikin wata iriyar dariya yace.
"Ke ki nitsu masoyinki ne ke gadinki, gsky *Mata* dole in rage miki wannan tsoron, domin matar Ba'ana bazata kasance matsoraciya ba, dole in ƙara tsumaki in dafaki da kyau, ta yadda idanunki zasu buɗe da kyau".
Cikin karkarwar da bai bar jikintaba tace.
"Bana so. Ni ka barnin da tsorona, nifa macece ba namiji irinka ba, kaine ke shiga daji da tsaunuka kake buƙatar wani abu ya kare ka".
Da sauri Ba'ana farin kekyawan babarbare ya matso gareta cikin shigar fulanin da ya zame mushi sutura yace.
"Mata ke bakya buƙatar kariyar ne?."
Da sauri ta gyaɗa mishi kai tare da cewa.
"Ni na yarda cewa addu'a'u saiful muminin ne, kuma shi na riƙe, so bana buƙatar waɗannan asirce asircen".
Murmushi yayi tare da murza ƙafarshi ta hagu sai gashi ya zama kamar inuwa ba mutun ya ɓacewa ganinta ɓat.
Da sauri ta rufe idanunta tare da cewa.
"Bana so ina tsoro ka dena caccanza kamanni a gabana".
Da sauri tayi baya ganinshi gab da ita,
Dariyar ƙeta yayi tare da cewa.
"Baga irinta nanba, idonki baya iya ganin komai, dole zan ƙara haɗaki irin haɗin da zaki ke banbance mai layar ɓata data zana da jingina bongo da dama duk mutun mai juyewa i zuwa wata halittar".
Ya karishe mgnar yana nuna mata hanya alamun su tafi.
A hankali suka jera suna tafiya a tare.
Allah ya sani Ba'ana yana masifar son Shatu tun tana ƴar ƙaramar yarinya, yana sonto irin sonda ko ƙudane in ya sauƙa kanta in dai namiji ne to zai kasheshi, ganinta kusa dashi kawai yana sashi jin daɗi, duk muguntarsa baya yi mata, duk duniya babu wanda Ba'ana ya yarda da shi bare yasan sirrin makarin sihirurrukan dake jikinshi. Ba'ana mutunne da yake tamkar al'janu sabida yawan ta'ammali da sihiri kai harma da tsafi, Ba'ana riƙeƙƙen tantirin ɓarawone wanda ya buwayi Fulani al'ummar Afirka gaba ɗayanta, da sace-sacen dabbobinshi, muddin ya ƙella ido yaga garken shanunka yayi mishi, to tazarar kilo mita talatin da biyar yake tsayuwa da garken, yayi FITO ɗaya tak, wallahi duk sihirin kafiyar garkenka zai kunce kuma duk inda yayi shanayenka zasu bishi a baya da kuma wannan tazarar, da zaran kasa Hukuma cikin zancen kuma yana burza layar ɓatanshi dashi da dabbobin duk zasu ɓace.
Duk garken da yaga yayi mishi to sai ya kwashesu tsan da wannan ya tara dukiyar dabbobin da shi kanshi baisan adadinshiba babu ƙasar da bashi da makiyayanshi kamar su.
Chadi, Nijer, Cameroon, Ghana, Gabon, Maroco, Senigal, da dai sauran kasashen makusantanmu kuma masu dabbobi, hikimar da yakeyi, muddin ya saci shanayen ƙasar Niger to sai ya cillasu ƙasar Senegal, in kuma makiyayanshi na ƙasar Sanigal sukayi sata to sai ya turo shanayen ƙasar Gabon, haka dai yake banbance mazauninsu.
Sai dai garin zamansa ɗaya ne Rugar Bani, inda nan aka haifeshi mahaifinshi Bukar wanda babarbaren Norba ne saye da sayar da kanwane ya ajiyeshi cikin rugar FULANI shiyasa ya zama dilan saida kanwa, sabida dole duk bafulatani makiyayi yana ta'ammali da kanwa dan ana zubawa dabobbi susha a ruwa ko asa musu a dusa ko harawa yana musu mgni.
Ba'ana ya shiga cikin Fulani ya saje dasu.
Yayinda hakan ya bashi damar da duk duniya ake ɗaukarshi matsayin bafulatani, koda yake hakan baya rasa nasaba, da kallon da mutanen duniya sukewa duk mutumin da akaga shanu, tumaki a gabanshi tofa ko wacce gabilace shi, ya zama bafulatani, wanda kuma sam ba haka abin yakeba.
Mahaifiyar Ba'ana ɗaya daga cikin ƙabilar ɓachama ce,
wacce Bukar ya aura tana a matsayinta na anniya, koda kuwa suka haihu ɗan su. Bukar ya rinjaye ta Ba'ana ya kasance musulmi, sai daifa a baɗini baƙar zuciyarsa da aiyikansa na kafuraine, sata kuwa a wurin babarsa ya gada.
Ba'ana kekyawan mutun ne ajin forko wanda ya gaji wannan kyan ne a kakarshi mahaifiyar babanshi wacce take shuwa Arabce, koda maƙiyinshi yasan tabbas Ba'ana kekyawane.
A duniya kab Shatu ce tasan sirrinshi ciki da woje,
sai daifa bata san yana sataba, amman duk wani abu na asiri da yadda za'a karya asirin da kuma yadda yake juyewa duk ta sani.
To hakanne yasa sam bata fatan ya zama miji a gareta bare uban ƴaƴanta, sai dai babu yadda ta iya. Domin ya mata babbar rana a rayuwarta ya mata taimakon da yasa aka ɗaukar mishi al'ƙawarin aurenta.
Gashi kuma duk wanda yace yana sonta karshenshi mutuwa, kuma yana gaya mata cewa duk wanda yace zai rabashi da ita zai kasheshi Wannan yasa kullum addu'ar shirya take mishi da fatan Allah ya rabata dashi lfy innshi ba mai shiryuwa bane.
Tafiya sukeyi cikin nitsuwa a hankali, murmushi yaketayi cikin so da ƙaunarta yace.
"Mata ya akayi na ganki da ƙaramar jaka?".
Kai ta ɗan gyaɗa mishi tana kallon kekyawar fuskarshi, cikin murmushi yace.
"Kece kika ajiyeni a kasar Kautal a Rugar Bani, kina ƙare karatunki zamuyi aurenmu in ɗaukeki mubar ƙasar, kawai dolece tasa na hakura da batun aurenmu kiyi karatu, dan naga kina son karatun kuma nasan zaki karantar mana da yaranmu, kuma ina son ki zama babbar lawyer mai zaman kanta, sai ki zama lawyer na koda watan-wata rana, rana zata ɓacin min".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kamar yaune zan kare karatun, Ya Ba'ana".
Kanshi ya rausayar tare da gyara riƙon igiyar jakar da yayi, kana yace.
"Allah ya nuna min wannan lokacin, in sha Allah sadakin aurenki Garken shanu ɗari zan bada".
Cikin mmki ta zaro ido tare da cewa.
"Kai Ya Ba'ana garke ɗari bama shanu ɗariba, ya bana ina zaka samu wannan shanun kaida garken naku ko shanu hamsin bai cikaba".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Allah zai kawosu kafin lokacin auren namu".
A hankali tace.
"Allah ya kawosu".
Amin Amin yace tare da ɗan juyowa ya kalleta, murmushi yayi mata, kana ya miƙo mata jakar tata cikin so yace.
"Mun iso bakin Gari ki shiga.
Ni zan koma baya dama rakoki nazo nayi kar shaiɗanun bakin kogi su cutarmin dake".
Kai ta ɗan jinjina tare da cewa.
"Ya Ba'ana lokacin sallah ya kusa fa ai gwara ka shigo sai kayi salla ka koma".
Bakinshi ya ɗan tabe tare da cewa.
"No bar sallan nan sai bayan mako biyu ina ƙara dafa jikinane kuma in nayi al'walan duk aikin zai karye".
Dafa kanta tayi da sauri tare da cewa.
"Wa'iyazubillah Wayyo Allah na Ya Ba'ana ka gane mana wannan abin da kakeyi shirka ne,".
Kanshi ya jujjuya tare da cewa.
"Shiga cikin gari zanzo musha hira da daren".
To kawai tace mishi ta juya ta nufi cikin garin.