Sashe 118
Garkuwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
A hankali ya miƙe tsaye bayan ya sha ruwan zam-zam mai ɗan sanyi kan ƴaƴan itatuwan da yaci.
System ɗinshi ya ajiye kan Dinning table ɗin, tare da wayarshi.
Gefenta ya ɗan ratsa ya fara taka steps ɗin tare da kallonta a fakaice.
Yana gab da sauƙane ya ɗan motsa lips ɗinshi tare da cewa.
"Kaɗan kenan in dai baki dena samin ido a jikina ba,
Faɗuwa harda kareireyewa zakiyi in baki kiyayi yimin kallon ƙurillaba, na lura ku mutanen wancan dajin bakuda abinda kukafi so sama da kallon killataccen wuri na jikin mutun.
Muddin baki dena satan kallon jikina ba, sai waɗannan mayatattun idanun naki sun tsiyaye kin huta ki zama makauniya babu ɗan jagora.
Kiyi dai a hankali ko kya samu ki mutu da idonki,".
Ya ƙarishe mgnar yana tafi kamar bashi yayi mgnar ba.
Ita kuwa Shatu hannun tasa ta sharce hawayenta tare da rakashi da hararan kai mugune.
A falon ya samu su Ummi sunata dariya.
Cikin sauri ya kalli su Jamil yace.
"Kai wannan dariyar na menene, ku taso mu tafi masallaci".
Cikin dariya Jamil yace.
"Allah ko Hamma Jabeer ina zaton Hibba bata taɓa azumi ba sai bana.
Ga yadda ta dawo wuni ɗaya, wai a haka kuma har ta fara lissafin wai yauwa yau mun kai ɗaya mun rage".
Ɗan gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Muhibbata tashi kije kiyi salla sai ki ɗan konta ki huta kafin a kira isha'i ko".
Cikin sanyi tace.
"To Hamma MJ".
Jalal kuwa cikin yin ƙasa da murya yace.
"Gobe ma zakiyi ne ko zaki huta".
Cikin kwaɓe fuska tace.
"Zanyi Umaymah tace, bana ko ɗaya in nasha sai na biya".
Murmushi ya ɗan yi tare da cewa.
"Ashe dai kin girma".
Da sauri ta sunkuyar da kanta, shi kuwa yabi bayansu Jamil.
Duk sukayi gaba, Sheykh kuwa na bayansu.
har yaje tsakiyar falon sai kuma ya ɗan tsaya jin Ummi na ce mishi.
"Shetu fa".
Cikin saurin tafiya masallacin yace.
"Tana can ta faɗi wai ko ta karye ne naji tana cewa ban dai san mataba".
Yana kaiwa nan ya fita, ita kuwa Ummi da sauri ta miƙe cikin zaro ido tace.
"Karaya kuma? Innalillahi yaushe".
Tayi maganar tana nufar falonshi,
A bakin ƙofar shigowa sukayi kiciɓis da ita, da sauri ta tareta tare da tallabota, jin yadda jikinta ke rawane ta jawota suka fito falon cikin tausayawa tace.
"Sannu Shatu".
Cikin tausaya Hibba taketa jera mata sannu.
Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa.
"Baki sha ruwan ba ma ko?".
Kanta ta gyaɗa mata alamar eh.
Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo mata.
Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla.
Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su.
Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin shirin Fatawa.
Sai tara dai-dai ya dawo, gida.
A kitchen ya jiyosu.
Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi.
Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi.
Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu.
Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon.
zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah,
tana ɗagawa tace.
"Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?".
Gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28".
Dariya ta ɗanyi tare da cewa.
"Kaɗan ma daga aikin Hibba".
Sai kuma tace.
"Ina ɗiyata kuma, ya azumin?."
Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace.
"Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa.
"Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa".
Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace.
"Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa".
"To ya Amarya?".
"Ban sani ba".
Cikin dariya Haroon yace.
"Allah baka haƙuri".
Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah.
Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa.
A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne.
Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi.
To tace kana ta juya ta tafi.
Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba ɗayatare da cewa.
"Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito.
Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman.
Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su.
Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga.
Yauma kamar daren jiya haka sukayi.
Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin.
A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-kaɗan.
Yau wunin azumi na biyar kenan.
Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani.
Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa, Shatu tana gaisheta ta fito.
Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa.
Ita kuwa Shatu falonta ta fito.
Bisa kujera ta zauna, tare da kiran
number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare.
Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa.
"Ban gane wake mgna ba".
Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace.
"Junaidu Adda Shatu ce fa".
Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa.
"Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah".
Cikin sauri tace.
"Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai.
Sai dan Baba Madune yana shan wuya,
Satin daya wucema an sake yi mishi aiki".
Cikin sanyi tace.
"To yanzu su waye ke kula daku".
Kanshi ya rausayar tare da cewa.
"Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci.
An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje".
Cike da jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi".
Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa.
"Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,".
Uhum tace a taƙaice.
Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi.
"Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado.
Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?".
Cikin dariya tace.
"Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu.
Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo."
Da sauri yace.
"Dan Allah Adda Shatu turo min number su".
To tace tare da gyara konciyarta.
Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama.
Sannan ta tura mushi number su ɗin.
Suna gamawa ta kira Number Bappa.
Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga.
Cikin jin daɗin jin muryarshi tace.
"Ina kwana Bappa na".
System ɗinshi ya ajiye kan Dinning table ɗin, tare da wayarshi.
Gefenta ya ɗan ratsa ya fara taka steps ɗin tare da kallonta a fakaice.
Yana gab da sauƙane ya ɗan motsa lips ɗinshi tare da cewa.
"Kaɗan kenan in dai baki dena samin ido a jikina ba,
Faɗuwa harda kareireyewa zakiyi in baki kiyayi yimin kallon ƙurillaba, na lura ku mutanen wancan dajin bakuda abinda kukafi so sama da kallon killataccen wuri na jikin mutun.
Muddin baki dena satan kallon jikina ba, sai waɗannan mayatattun idanun naki sun tsiyaye kin huta ki zama makauniya babu ɗan jagora.
Kiyi dai a hankali ko kya samu ki mutu da idonki,".
Ya ƙarishe mgnar yana tafi kamar bashi yayi mgnar ba.
Ita kuwa Shatu hannun tasa ta sharce hawayenta tare da rakashi da hararan kai mugune.
A falon ya samu su Ummi sunata dariya.
Cikin sauri ya kalli su Jamil yace.
"Kai wannan dariyar na menene, ku taso mu tafi masallaci".
Cikin dariya Jamil yace.
"Allah ko Hamma Jabeer ina zaton Hibba bata taɓa azumi ba sai bana.
Ga yadda ta dawo wuni ɗaya, wai a haka kuma har ta fara lissafin wai yauwa yau mun kai ɗaya mun rage".
Ɗan gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Muhibbata tashi kije kiyi salla sai ki ɗan konta ki huta kafin a kira isha'i ko".
Cikin sanyi tace.
"To Hamma MJ".
Jalal kuwa cikin yin ƙasa da murya yace.
"Gobe ma zakiyi ne ko zaki huta".
Cikin kwaɓe fuska tace.
"Zanyi Umaymah tace, bana ko ɗaya in nasha sai na biya".
Murmushi ya ɗan yi tare da cewa.
"Ashe dai kin girma".
Da sauri ta sunkuyar da kanta, shi kuwa yabi bayansu Jamil.
Duk sukayi gaba, Sheykh kuwa na bayansu.
har yaje tsakiyar falon sai kuma ya ɗan tsaya jin Ummi na ce mishi.
"Shetu fa".
Cikin saurin tafiya masallacin yace.
"Tana can ta faɗi wai ko ta karye ne naji tana cewa ban dai san mataba".
Yana kaiwa nan ya fita, ita kuwa Ummi da sauri ta miƙe cikin zaro ido tace.
"Karaya kuma? Innalillahi yaushe".
Tayi maganar tana nufar falonshi,
A bakin ƙofar shigowa sukayi kiciɓis da ita, da sauri ta tareta tare da tallabota, jin yadda jikinta ke rawane ta jawota suka fito falon cikin tausayawa tace.
"Sannu Shatu".
Cikin tausaya Hibba taketa jera mata sannu.
Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa.
"Baki sha ruwan ba ma ko?".
Kanta ta gyaɗa mata alamar eh.
Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo mata.
Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla.
Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su.
Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin shirin Fatawa.
Sai tara dai-dai ya dawo, gida.
A kitchen ya jiyosu.
Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi.
Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi.
Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu.
Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon.
zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah,
tana ɗagawa tace.
"Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?".
Gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28".
Dariya ta ɗanyi tare da cewa.
"Kaɗan ma daga aikin Hibba".
Sai kuma tace.
"Ina ɗiyata kuma, ya azumin?."
Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace.
"Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa.
"Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa".
Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace.
"Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa".
"To ya Amarya?".
"Ban sani ba".
Cikin dariya Haroon yace.
"Allah baka haƙuri".
Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah.
Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa.
A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne.
Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi.
To tace kana ta juya ta tafi.
Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba ɗayatare da cewa.
"Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito.
Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman.
Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su.
Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga.
Yauma kamar daren jiya haka sukayi.
Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin.
A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-kaɗan.
Yau wunin azumi na biyar kenan.
Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani.
Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa, Shatu tana gaisheta ta fito.
Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa.
Ita kuwa Shatu falonta ta fito.
Bisa kujera ta zauna, tare da kiran
number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare.
Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa.
"Ban gane wake mgna ba".
Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace.
"Junaidu Adda Shatu ce fa".
Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa.
"Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah".
Cikin sauri tace.
"Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai.
Sai dan Baba Madune yana shan wuya,
Satin daya wucema an sake yi mishi aiki".
Cikin sanyi tace.
"To yanzu su waye ke kula daku".
Kanshi ya rausayar tare da cewa.
"Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci.
An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje".
Cike da jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi".
Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa.
"Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,".
Uhum tace a taƙaice.
Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi.
"Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado.
Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?".
Cikin dariya tace.
"Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu.
Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo."
Da sauri yace.
"Dan Allah Adda Shatu turo min number su".
To tace tare da gyara konciyarta.
Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama.
Sannan ta tura mushi number su ɗin.
Suna gamawa ta kira Number Bappa.
Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga.
Cikin jin daɗin jin muryarshi tace.
"Ina kwana Bappa na".