← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 71

Sashe 9

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ban kula ta ba sai da na kwashe sharan da nayi sannan na shiga d'aki nima na fito da robobin ice cream da kuma takardan naman kaza da muka ci harda warwarewa yanda za'a ga kasusuwan cikin sannan na ajiye a wajan wanke-wanke nima inayi mata murmushi na koma d'aki karb'o omo da zanyi mana wanke-wanken.

Da na karb'o omo sai da na d'auko Baby na na fito ina danna madannin jikin ta fara wak'an larabci,ina fitowa na tarar da Gwaggo Aisha tana leken inda na ajiye kwanukan mu.

Dariya nayi na ajiye Baby na a gefe na fara wanke-wanke na hankali kwance,ina jin Gwaggo Aisha tana jan tsaki tare da cewa," karyar banza bayan mun san komai me za'a nuna mana. Tana magana ne tare da shigewa d'akin ta sai dai tana shiga naji suna rigima da Jameela wai a saya mata irin Baby na,tun tana rarrashi naji an kai mata maka ta tsala ihu tayi waje da gudu.

Ko a ido ka kalli babyn ka san mai tsada ce shiyasa tayi mata haka domin bata da kud'in sayan shi.

Ranan muna zaune a d'aki bayan magariba ana gobe Inna zata karb'i girki muka ji muryan wani abokin Baban mu yazo yana ta masifa kan wai Baban ya ranci kud'in shi naira dubu biyu bai biya ba, ashe tun bayan la'asar Baba yake gida ya kasa fita majalisa saboda bashin da ake bin shi bamu sani ba.

Abu kamar wasa fitinan yayi girma dan ana ta bashi hakuri yace babu inda zai je sai Baba ya biya shi kud'in sa yau kusan wata 2 kenan ana abu d'aya kuma shi ya gaji da yanda Baba ke cewa yau ko gobe.

Jakar kayanta Inna ta bud'e ta ciro dubu biyun tace min in kaiwa Baban mu,karb'a nayi na fito kai mishi ba dan raina yaso ba saboda shima baya tausayin mu baya nuna kulawa gare mu sai sauran 'yan gidan shiyasa nima banga dalilin da yasa zamu tausaya mishi ba.

Sai dai ina zuwa saida na tausaya mishi,yana rab'e jikin k'ofan shi yayi abin tausayi shi kuwa mai bashi sai ci mishi mutunci yake, ga kanin Baban mu da muke kira da baffa shima sai hakurin yake badawa amma a banza

Ina zuwa kusa dashi na tab'a shi ya d'ago ya kalle ni da idon shi daya canza kala, mika mishi kud'in nayi na ce," gashi inji Inna tace ka biya su kud'in.

Baba kasa karb'an kud'in yayi ya tsaya kallo na haka sauran matan ma suka tsaya kallon kallo.

*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/3, 9:06 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp

حَدَّثَنَا سَعِيدُ بْنُ مَنْصُورٍ وَقُتَيْبَةُ بْنُ سَعِيدٍ وَأَبُو كَامِلٍ الْجَحْدَرِيُّ وَاللَّفْظُ لِسَعِيدٍ قَالُوا حَدَّثَنَا أَبُو عَوَانَةَ عَنْ سِمَاكِ بْنِ حَرْبٍ عَنْ مُصْعَبِ بْنِ سَعْدٍ قَالَ دَخَلَ عَبْدُ اللَّهِ بْنُ عُمَرَ عَلَى ابْنِ عَامِرٍ يَعُودُهُ وَهُوَ مَرِيضٌ فَقَالَ أَلَا تَدْعُو اللَّهَ لِي يَا ابْنَ عُمَرَ؟ قَالَ إِنِّي سَمِعْتُ رَسُولَ اللَّهِ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ يَقُولُ لَا تُقْبَلُ صَلَاةٌ بِغَيْرِ طُهُورٍ وَلَا صَدَقَةٌ مِنْ غُلُولٍ وَكُنْتَ عَلَى الْبَصْرَةِ.

*It was narrated from Simak bin Harb, that Mus`ab bin Sa`d said: "`Abdullah bin `Umar came to visit Ibn `Amir when he was sick and he said: `Won`t you supplicate to Allah for me, O Ibn `Umar?` He said: `I heard the Messenger of Allah (s.a.w) say: "No Salat is accepted without Wudu` (purification), and no charity (is accepted) that comes from Ghulul," and you were the governor of Al-Basrah."`*

[ Sahih Muslim ]

*7*

Baban mu jikin sane yayi sanyi sosai, wai Bintu ce ta biya mishi bashi. Bayan duk abubuwa da yayi mata basu da misali bayan wa'yan da ya fifita duk suna tsaye babu wanda yayi gigin biya mishi alhalin suna dashi, more especially 'yar gaban goshin sa wato Gwaggo Aisha, ga Baffan mu duk suna wajen taya zai iya kallon idon ta nan gaba?.

"Amma Mallam Hassan ka cika mugu azzalumi,wato yanzu a baka kud'in da zaka biya ni shine ka rike ka maida ni d'an iska wato inyi in gama ko? Allah ma yasa a gaba na aka aiko da kud'in da shikenan sai ka cigaba da raina min hankali kana cewa babu" yana banbani ya matso kusa da Baban mu ya kwace kud'in a hannun sa ya fita yana," Allah ya so ka Mallam".

Da ido kowa ya bi bayan shi har ya ida ficewa, bai san cewa mamaki ne daya cakud'u da mutuwar jiki su suka hana shi bayar da kudin ba, bai kara kallon kowa a wajan ba ya koma d'akin shi ya zauna a bakin gado tare da rafka uban tagumi yana tunanin ta yayane zai shawo kan Bintu yaci dad'i kuma ya samu na kashewa, dubu biyu fa?.

Can shi kad'a ya saki murmushin jin dad'i alamun ya samu mafita kenan.

A waje kuwa Baban mu yana shiga d'akin sa Baffan mu shima ya bar wajan yana tab'e baki dan bai ga dalilin da zai saka ya biya mishi bashi ba, da ace wannan kud'in yayi amfani dasu wajan ciyar da iyalin shine zai iya biya amma tunda kansa kad'ai ya sani bai san hakkin daya rataya akan sa ba shi ya sani yaje can ya karata.

"Allah sarki Bintu Allah dai yasa ba mugun halin kema kika fara kaman sauran matan ba saboda mugun halin d'an uwana duk shi ya jefa iyalin shi cikin halaka" yana magana ne tare da shigewa b'angaren shi.

Gwaggo Aisha da Inna Asabe duk sun kasa barin wajen suna tsaye a wajan kaman wanda aka dasa su kowacce da irin tunanin da take a zuciyar ta saboda Abin ya mugun daure musu kai sosai ita da duk gidan itace wacce bata dashi amma yanzu ta dara kowa a gidan.

Gwaggo Aisha fargaban ta d'aya shine kada Inna tazo ta kwace mata matsayi a wajan Baban mu domin ta san halin shi tsab zai iya juya mata baya dama saboda tafi kowa kud'i a gidan yake fifita ta, kai dole ne tayi wani abu akai dan ba zata tab'a zuba ido Inna ta ta kwace mata ba.

Da washe gari ina dawo daga makaranta a nesa na hango motan Abdulbasit a k'ofar gidan mu, aiko da gudu na karaso wajan motan cike da murna dan yanzu na daina tsoro tunda Innata da kanta take cewa inje mu gaisa bayan haka ga kayan dad'i da kullum in zai zo yake kawo min, yana zaune a ciki motan amma kafafun shi a waje hankalin shi yana kan wayar shi ban san me yake dan dannawa ba.

"Sannu da zuwa Yaya na" na fad'a da d'an karfi bayan na karasa kusa dashi,a d'an razane ya d'ago sai kuma ya saki murmushin sa mai kyau da baya barin fuskan sa.

"Har kin tsorata ni saura kad'an in ruga da gudu" ya ce yana dariya.

Nima dariyan na kyakyale dashi sannan na ce," toh ya zakayi da motan ka in ka gudu ka barta?"

"Sai in bar miki ita ki rink'a zuwa makaranta dashi" toh ai ban iya yanda ake tukawa ba" na fad'a a shagwab'e.

"Kada ki damu zan koya miki, kije ki cewa Aunty zan shigo mu gaisa".

Da toh na amsa sannan na juya na shige gida da sauri na, su Hajara duk sun tafi tallah iyayen nasu ma ban gan su ba da alamu duk sun fita.

Inna tana k'ofar d'aki tana shara na shigo da sallama ta amsa tana yi min sannu da zuwa,ciki na shige na ajiye jaka ta sannan na kara fitowa na ce mata," Inna Yaya yazo yana waje yace zai shigo ku gaisa".

"Ciki nan zai shigo yace?" Ta tambaya da alamun tsoro da damuwa akan fuskan ta, gyad'a mata kai nayi ina kallon duk yanda ta zama wani iri.

"Toh ya shigo" ta ce tana komawa d'aki ni kuma na fita waje na sanar dashi kan ya shigo, a bakin k'ofan d'aki muka tadda Inna zaune cikin tagumi amma tana ganin mu ta saki ran ta tana mishi sannu da zuwa.

Kallon gidan namu yake tare da nazarin sa,har k'asa ya duka suka gaisa da Inna a mutunce tare da bata hakurin rashin zuwan sa akai-akai kaman yanda yayi mata alkawari, nuna mishi tayi babu komai kana ta d'aura dayi mishi godiya tare da addu'oin gamawa da duniya lafiya.

Cikin jin dad'i yake amsawa da Ameen sannan ya mike yace zai wuce dai-dai lokacin kuma iska mai karfi ya d'aga d'an yalolon labulen mu karaf idon sa sai a d'akin mu da ko arzikin leda babu sai siminti dasu ghana must gon mu a gefe.

Tare muka fito dashi har zuwa wajan motan sa ya ciro manyan jakuna na shopping daya saba kawo mana ya mik'a min sannan ya kara da kud'i masu yawa yace in bawa Inna ince ta sayi carpet na tsakar d'aki dasu gado.

Cikin tsananin murna na dawo cikin gida da kaya niki-niki sannan na nunawa Inna kud'in daya bata tare da fad'a mata abinda yace tayi dasu.

Karb'a Inna tayi ta ajiye gefe ba tace komai ba dan yanzu zuciyar ta ta fara amincewa dashi sannan ta fara sabawa da lamarin sa.

Ni kuwa duk na k'ogu ta bud'e kayan domin na san duk tsaraba nane a ciki, tana bud'ewa kuwa sune ice cream da sauran kayan dad'i sai kaza gasassu biyu,ice cream na na d'auka na koma gefe na fara sha domin ni yafi min kaza sau dubu.
Chapter 9 · 0% Book details