← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 71

Sashe 61

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Abin mamaki dai baya karewa a duniya dan Baban mu ne ya maida hankalin shi kan mu kacokan yana mana nasiha akan hakuri da zaman duniya sannan yace mu tashi mu tafi gida kada dare yayi mana.

Godiya muka mishi muka mike muka fito ni duk jikina yayi sanyi akan yanda Baban mu ya dawo lalle ba karamin wuya ya sha a hannun su ba daya canza farat daya.

Shi ya bude min motan na shiga na zauna sannan shima ya zagaya ya shiga ya zauna yana kallon yanda na dawo so cool, marairaice fuska yayi kaman zaiyi kuka yace " Allah sarki ni,i na rasa ya zanyi komai nayi banyi daidai ba"

Ban san lokacin da nayi murmushi har hakorana suka bayyana saboda salon da yayi amfani dashi yayi maganan dole yasa mutum dariya, dariyan shima yqyi ganin ya saka ni murmushi sannan ya ja motan muka hau hanya.
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*Wannan page din naki ne rahama lawal Umar ( ummu Farhan ) kiyi yanda kike so dashi ,alkhairin Allah ya isa gare ki a duk inda kike nagode da soyayyar gare ni Allah ya bar zumunci Ameen*

*Sorry last page nayi mistake wajan saka number maimakon 54&55 , na saka 44 &45.

*56&57*

Baba gaba d'aya jikin shi a mace yake da jin bayanan Abdulbasit tabbas ya tafka kuskure ko Kuma yace yana cikin b'ata, son duniya da sharrin shaid'an ya kai shi ga aikata duk abinda yayi sai dai komai rubutattace ne a kundin kaddara wanda ba makawa sai ya samu mai shi, in da ya kasance mai kulawa da iyalin sa da duk haka bata faru ba.

"Na san ba zan kai labari ba dan kashe ni zasuyi kuma nima hakan nake fata domin tunda na rabu da Zareefa ban tab'a jin dad'in rayuwata daidai na second d'aya ba, nayi jinya a boye ba tare da kowa ya sani ba da naje asbiti doctor yace na kamu da ciwon zuciya mai tsanani , shiyasa na kudiri aniyar ganin bayan Emaka kamin in karasa 'yan kwanaki da suka rage min" Abdulbasit ya karasa da fashewa da kuka da bai samu daman yi ba duk watanin nan.

Hawaye da suka zubo mishi Baba ya share zaiyi magana Baban Hamis ya kashe system d'in shi ya juyo yana facing abokanen aikin shi da duk suma labarin ya girgiza su kaman yanda ya girgiza shi shima sai dai kowannen su ya shanye abin sa a rai ba zaka tab'a fahimtar komai akan fuskokin su ba.

Gyaran murya yayi sannan ya fara magana" duk da komai ya bayyana Ina son shi wannan Abdulbasit d'in ya amsa laifin shi da bakin shi sannan yayi jagora inda za'a samu gang d'in nasu gaba d'aya" babu wani ja suka nuna gamsuwar su kan hukucin da ya yanke bayan dan tattaunawa da sukayi suka wuce offices d'in su.

Zafar bai masu isowa gidan mu ba sai da ya tsaya yayi sallahn azahar ya tsaya a wani shopping mall yayi sayayyan kayan masurufi masu yawan gaske sannan ya karaso gida.

A waje yanzun ma yayi parking din motan shi ya samu yara a kofar gidan suna jiran a gama abincin sadaka a raba musu yace su shigar da kayan cikin gida nan da nan ko suka fara shigowa da sayayyan da yayi zuwa tsakar gida suna ajiyewa, Inna da fitowar ta kenan daga wanka tana neman Ibrahim ya fara kiran masu karban sakadan tayi arba dasu suna ta shigowa da kaya suna jibgewa hayaniyar su duk ya cika gidan.

Cike da mamaki tabi su da kallo kamin ta tambaya Ibrahim da shigowar shi kenan rungume da carton na indomie yace " Innan Zareefa mijin Zareefa ne yace mu shigo da kayan nan kuma yace wai ta fito su tafi".

Cizon yatsa Gwaggo Aisha da take leke ta window tayi tana jin bakinciki da takaici ya kume ta dole ne tayi maganin Inna ta shiyasa take ta d'agawa mutane hanci a gidan ita wai 'yar ta na auran mai kudi, Hajara da shigowan ta kenan zata wuce ciki ta ga yanda take rike da labule tana kallon yaran fuskarta kuwa kaman anyi gobara sai cizon d'an yatsa take, kain ta girgiza kawai tayi wucewar ta ciki tana mata addu'an shiriya ta barta anan tsaye tana faman leke .

Na fito daga bathroom d'in daki na kenan fuskata na d'igan ruwan alwala da nayi murmushi nake sosai ina jin kaman babu inda na tafi iya watanin nan kaman bacci nayi na tashi haka nake ji domin komai na dakina yana nan tsab ba abinda ya canza kaman lokacin da nake nan.

Kara fad'ad'a murmushi na nayi ganin Inna zaune a bakin gadon tana jiran fitowa na kamin in samu daman yi mata magana tace " kina idar da sallah ki fito ku tafi yazo yana jiran ki a waje" a take farar dake fuskata ya kau na kwab'e shi kuwa kaman zanyi kuka saboda ko kad'an ban saka ran tafiya yanzu ba na zata sai dare zai dawo.

"Bana son shashanci kiyi sallah ki fito nace sannan kada ki yarda in kara dawowa dakin nan baki fito ba kema kin san sauran" cewar Inna kenan tana barin d'akin, hawayen da suka zubo min na share tare da karasowa ciki na shimfid'a abin sallah na fara sanin halin Inna in ta shigo ba zatayi min da dad'i ba.

Har na idar da sallah ban daina hawaye ba dan ko kad'an bana son tafiyan, dole na na fito parlorn Ina sharar kwalla na samu Inna zaune da wani babban leda kusa da ita tace in shiga d'akin ta muyi sallama dasu Maa, jiki ba kwari na shiga na same ta harda 'yan uwan Baba duk sun idar da sallah kowacce rike da carbi suna lazimi.

Har kasa na zauna dan niyyan yi musu sallaman amma na kasa furta komai sai hawaye na da suka karu, dariya suka fara min wai Inna ta shagwab'ani dayawa daga baya kuma suka shiga yi min nasiha kan in kara hakuri domin zaman gidan miji saida hakuri, ba gidan miji ba duniyar kanta in kana son kaji dad'in ta toh sai da hakuri da kauda kai.

Tun ina kuka har na daina saboda yanda suka kashe min jiki daga nan suka ce in tashi in tafi yana Jira na, tashi nayi na fito Inna tana nan a inda na barta, miko min ledan tayi tace to in tafi mu gaida gida maimakon in karb'a kuka na saka mata ina sai naci abinci domin nayi missing girkin ta.

Kala bata ce min ba sai ganin ta nayi da wani madaidaicin warmer ta zubo min abincin sadaka da sukayi tace in naje gidana inci kuma in biya wajan sauran matan gidan inyi musu sallama, dole na karb'a na fito Inna Asabe ita na fara yiwa sallama sai maman Dije ban shiga wajan Gwaggo Aisha ba kasancewar Hajara tace min ta tafi anguwa, a kofar d'akin su na tsaya dan muyi sallama amma sai ta karb'i kayan hannu na ta fara taka min tare muka fito bakin gate.

Ta window Gwaggo Aisha take leken mu har muka fita bakinciki kuwa kaman ta had'ye zuciya ta mutu take ji wato na shiga ko Ina nayi musu sallama ita da na raina shine ban shiga mata ba ? Koda yake ta san Inna ce ta kitsa min hakan , ita kuma Hajara dan rashin zuciya ina kanwar bayan ta shine harda karban kayan hannu na tayi min rakiya.

Yana ganin fitowan mu yayi saurin bud'e min kofan mota dama yana tsaye a jikin motan ne, gaishe shi Hajara tayi tare da saka min kayan a mota sannan tayi min waving ta koma cikin gida.

Tsaye nayi ina kumbura fuska da tura baki gaba dan gaba d'aya haushi shi nake ji na me yasa bai barni na kai dare a gidan mu ba, fuskar shi d'auke da fara'a yace " shigo mu tafi mana 'yan mata na?"

Ko kallon shi banyi ba na shiga ina jin haushin sunan daya kira ni dashi wai 'yan matan shi ko ta ina na zama 'yan matan shi oho, rufe min kofan yayi ya zagaya ya shiga mazaunin driver yayi reverse muka kama hanya har sannan naki kallon side d'in da yake kacokan na maida hankali na kan hanya shi kuwa sai juyowa yake yana kallo na .

A wani restaurant ya tsaya yana kallo na nima jin mun tsaya kuma bamu kai gida ba yasa na juyo na dubi side d'in shi caraf ido na cikin nashi ya wani kashe min ido tare da daga gira daya alaman ya dai? Kawar da kaina nayi ina kara turo baki , da san irin wannan kallon yake min da ban juyo ba na kalli inda yake ba dan sosai ya kashe min jiki da salon shi.
Chapter 61 · 0% Book details