← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 71

Sashe 69

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kawar da fuskata gefe nayi nima ina wani boyayyen murmushi sannan na dawo da duba na gare shi,da ido nayi mishi alaman daya zauna mana sai a lokacin ya lura da inda muke.nan ma bai musa ba ya zauna ni Kuma kayan daya sayo na wuce kitchen dasu na wanke na yanka mana a plate sauran Kuma na saka su a fridge,na dauki wanda na yanka mana na fito.

Ina fitowa muka had'a ido da alamu tunda na shiga idon shi anan yake har na fito, ajiye plate din nayi akan table sannan naja kujeran kusa da shi na zauna tare da fara zuba mana abincin a plate daya kaman yanda naga yake yi.

"Ina su Abba da Mom?" Na tambaya ina cigaba da aikin da nake, sai a nan ya samu bakin magana cikin washe hakora ya bani amsa" suna nan lafiya amma Abba yayi tafiya yau sai Mom ce kad'ai muka sha hira da ita har nake bata labarin yau da safe ni nayi mana breakfast bata yarda ba kasanewar tun taso wata ta san babu abinda na tsana kaman shiga kitchen".

Ajiye spoon din dake hannu na nayi ina jin babu dad'i a raina how could he tell her such things,na san iyayen mu na yanzu ba mamaki ta fara nagetive thinking balle ma Momy da nake ganin tsana ta a cikin idon ta.

"I think daga yau Zaki fara koya min wannan delicious da Innar mu ta koya miki" naji muryan shi ya katse min tunanin da nake, murmushi yake nayi ina " kada ka damu da koyan girki bayan kana namiji, girki ai aikin mata ne".

Dariya ya fara tare da debo abincin ya nufi baki na dashi nima babu musu na bud'e mishi baki ya zuba min na fara taunawa a nitse tare da zuba mishi kyawawan idanuwa na ina jin kaman in rungume shi dan wani matsacin soyayyar shi nake jin na kara ninkuwa a cikin zuciya ta.

Shima dariyan nashi ya tsayar tare da kurawa baki na ido yana kallon yanda nake motsa su a hankali, ji yake kaman ya kamo su yayi ta tsotsa amma babu hali.duk mancewa da cin abincin mukayi kowa ya tafi duniyan tunani wanda har ya abinda yake ran shi ya ingiza shi without any thoughts ya fara motso da fuskar shi zuwa nawa domin cikawa zuciyar shi muradin ta.

D'umin numfashin sa daya sauka akan fuskata shiya dawo da ni hayyacina cikin azama nayi saurin yin baya da tawa fuskar da saura kadan ya hadu da tashi, sai a lokacin ya ankara da abinda yake faruwa.cikin waskewa ya d'an had'a rai yana" ke tsaya abu nagani zan cire miki a saman ido kar ya shiga miki cikin idon" komo da fuskata nayi kaman yanda muke d'azu numfashin shi na cigaba da sauka akan fuskata daya sanya ni tsintan kaina cikin wani yanayi mara misaltuwa daya wajabta min lumshe idanu na hoping for mu tabbata a haka.

Fuskar nawa ya kurawa ido yana jin wani sabon yanayi a tare da shi,how he wish he could suck dis pink lips right now Amma babu halin yi, sai da yayi da gaske sannan ya aro jarumta ya saka hannun shi na dama ya dan goge min saman idon a sunan ya cire min sannan yaja baya nima sai a lokacin na samu daman bud'e ido na.

Haka dai a shirarance muka ci abincin da ko rabi bamu ci ba muka bari anan dining din ya hau bani labarin makarantan su muna ta kwasan dariya kaman ba Zafar din nan mai ji da kan shi ba.bamu tashi a wajan ba sai da aka Kira sallan la'asar,shi ya taimaka min muka kwashe kayan da muka bata zuwa kitchen na tsaya wanke su shi Kuma yayi alwalan ya fita masallaci.nima sai da nagama wanke-wanke na kintsa kitchen d'in sannan na wuce daki nayi alwala nayi sallahn.

Koda na idar kasa tashi a wajan nazauna tunanin rayuwar aure na, ina tuna yanda a sch ake labarin yanda daren farko yake kasancewa da yanda miji yake bawa matar shi kulawa a wannan daren,a lokacin da Yayana kawai nake imagining amma gashi cikin ikon Allah ashe ba shi bane mijina,ashe abinda nake ji akan shi ba so bane shakuwace kawai dan sai yanzu na san asalin menene so.sai dai kash wanda nake son bana gaban shi asalima auren manufa yayi dani.

Shima Zafar ana idar da sallah bai wani jima ba ya dawo gida dan yanzu in ba dole ba baya son abinda zai saka yayi nesa dani,yafi son mu kasance tare a kowani lokaci.sallamar da yayi shiya dawo dani daga duniyan tunani dana lula amsa mishi nayi ina kakalo murmushi don boye yar damuwa dake kan fuskata.

Karasa shigowa dakin yayi yazauna a bakin gado na abinda bai tab'a yi ba kenan dan haka da kallo na bishi zuciya ta na min sanyi duk da na san fake love ne Amma ina matukar jin dadi in yana nuna min kulawa komin kankantarsa.

"Kar dai sai yanzu ki kayi sallah?" Ya tambaya yana kallo yanda nake ninke doguwar hijabi na sallah dana cire,ban bashi amsa ba sai da na ajiye shi a mazaunin shi sannan na juyo na dawo kusa dashi na zauna a gefen shi sannan nace" a'a tundazu na idar ban dai tashi daga wajan da nayi sallah bane...." Kallon da yake bina dashi yasa na hadiye sauran maganan nayi mishi alama da hannu wato "ya dai".

"I'm just thinking ne ko Abba ya isa lafiya gashi bai kirani ba ko za kira shine ban sani ba" ya fadi hakan cikin waskewa,duk da na gane amma nima sai na basar nace" kana da no shi na kasar daya tafi ne?"

"Roaming no shi yake a duk kasar daya tafi,so baya canza sim in yayi tafiya" ya bani amsa yana ciro wayar shi daga aljihun rigan sa ya shiga neman layin Abban cikin sa'a kuwa sai gashi ya shiga ya fara ringing, yana gab da katsewa ya daga cikin murya dake nuna zallar gajiya ya amsa sallaman da yake mishi.

Bayan sun gaisa yayi mishi ya hanya yake tambaya ta ya nake, wayar ya daura min a kunne ba tare daya amsa tambayar ba yana min alama da ido da in mishi magana.sallama nima na mishi ya amsa muka gaisa daga nan ya dauke wayan daga kunne na ya daura a nashi suka cigaba da magana,kokarin mikewa na fara yi ganin hirar tasu ba mai karewa bane amma ya dakatar dani ta hanyan rike min hannu.

Hannuna daya rike na kalla sannan na kalle shi naga shi hankalin shi gaba daya yana kan wayan da suke yi da mahaifin shi,shagala nayi da kallon shi yanda yake magana cikin natsuwa da wannan tsadadden murmushun akan fuskan shi, he is looking damned cute dan ever b4.sam ban san lokacin da suka gama wayan ba har ya juyo shima ya zuba min nashi idon sai ya lura hankali na yayi nisa cikin tunani.

Bai ce min komai ba sai murza hannu na da yake cikin nashi daya fara shiya dawo dani hayyacina,cikin sauri na kwace hannun nawa tare da dauke Kai ina dan murmushi kunyan kamani ina kallon shi, dan dariya mara sauti yayi yana" ina zaki je kuma bayan na shigo tayaki hira?"

"Kitchen zan shiga naga har 5:30 ta gota" na amsa ina kallon gefe dan har yanzu ban gama warwarewa daga kunyan kamani da yayi ina kallon shi ba.

"Me Kuma zakiyi a kitchen d'in?" Ban san lokacin da na juyo ba jin tambayar daya min kaman bai san meye kalmar kitchen d'in yake mufi ba,dauke kaina nayi ganin har yanzu idon shi a kaina suke.

"Girki zan daura" na bashi amsa a takaice.

"No yau ki huta ba sai kin dafa komai ba we re having our dinner outside today dan haka ki huta yau".

"Toh" nace kawai ina jin dad'in cewa zamu fitan da yayi,nan ya zauna muna dan hira jefi-jefi har aka Kira sallah magarib.tashi yayi ya shiga bathroom dina dan yin alwala na bishi da kallo hankali tashe saboda na shanya su panties dasu bra dana wanke dazu ban kwashe ba dan koda na shiga alwalan la'asar basu gama bushewa ba,aiko kaman in tashi in kamo shi nake ji sai dai babu dama.

"Shikenan ya gama gane min sirri" nace kaman zan fashe da kuka.shi kuwa yana shiga bathroom din sai da ya lumshe ido saboda kamshin sabulai da nake wanka duk sun kama bathroom din ga Kuma turaren wuta da nake sakawa shima, tsayawa yayi Yana karewa bathroom din kallo kasancewar yau shine karon farko daya fara shiga, gashi nan fes komai a kimtse a bushe. Har ya fara takawa zuwa gaban sink da niyyan yin alwala karaf idon shi ya sauka kan shanya da nayi kaman Wanda aka sakawa magnet ana jan shi zuwa gare su haka ya karasa yana kallon su kaman bai taba ganin abu makamancin su ba.
.

Hannu yasa yana duba size d'in cikin mamaki ya sake tare da toshe baki yana dariya" wai dama haka yarinyan nan take ban tab'a gani ba,koda yake suna cikin kaya tayaya zan gane" duk shi kad'ai yake surutan sa a bayin yana mamakin ya akayi bai sani ba all this while,can kuma ya tuna ashe fa ko eye pencil bai saya an saka a lefe na ba,sai yaji Kuma babu dad'i " all this are fake zan hado mata nawa da kaina" yace yana nufan sink din ya fara alwala murmushi bai bar fuskan shi ba.

Ni Kuma ina zaune ne kawai amma gaba daya hankali na baya tare da ni I was thinking maybe yana can yana kalle min sirri shiyasa ya dade,ina cikin maganan zucin sai gashi ya bud'e kofa ya fito.wani irin kallo daya min yasa na dauke Kai na da sauri ina jin kaman in fashe da kuka saboda tsab na fahimci ma'anar kallon " kiyi sallah sai ki shirya ba zan shigo ba sai bayan sallah Isha'i" gyada kaina kawai nayi ba tare da na kalle shi ba.
Chapter 69 · 0% Book details