← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 71

Sashe 63

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Tun jiya mun saka shi Abdulbasit d'in gaba ya kai ma'aikatan mu mab'oyan gang d'in nasu dake can dajin mafa Kuma Alhmdlh Allah ya basu sa'an cafke su duka yanxu haka duk suna hannun mu zamu tura su Abuja inda za'a yanke musu hukunci" cewan Baban Hamis kenan, nan ma kara godewa Allah sukayi sannan suka gode mishi shi kuwa Zafar taf ya cika saura kiris ya fashe dan lokacin an tafi d'auko musu Baba suke maida labarin irin soyayyan da mukayi yayan nawa.

Suna zaune a wajan aka shigo da Baba da ko mikewa baya iyayi jikin sa kuwa duka ba kyan gani saboda kumburin da yayi hatta fuskan shima a kumbure yake, da gudu Baban Dije ya taro shi dan suna zuwa tsakiyar office d'in suka sake shi suka juya abin su.

Duk kan shi sukayi suna yi mishi sannu , Baban Hamis hakuri suka basu tare da cewa zasu iya tafiya dashi ,haka suka fito dashi suna rirrike dashi suka saka shi a mota direct wani private hospital dake nan wulari area Zafar ya kai Baba, nan da nan kuwa suka karbe shi su fara mishi treatment su kuma suka fita masallaci dake nan cikin asibitin yin sallah azahar.

Koda suka dawo rigima suka tarar tsakanin Baba da likitocin sunce dole ne su bashi gado yayi kwana 2 har yaji kwarin jikin sa shi kuma ya ce sam bai san zancen ba shi gida zai tafi, su Baban Dije suma sun saka baki amma fa Baba ya kafe kan cewa ba zai zauna ba.

Zafar ne yace a bar shi su tafi gidan in yaso zai d'auko doctor ya rinka zuwa yana duba shi kullum, su Baban Dije sun gamsu da bayanin Zafar dan haka ba b'ata lokacin suka saka shi a mota sai gida.

A gida kuwa dana shiga na iske kowa na cikin farinciki kaman Baban ya dawo duk yan uwa sun taru ana taya juna murna na samun labarin sa da akayi sai sakawa Zafar albarka suke da addu'oin gama wa da duniya lafiya.

La'asar dai-dai mukaji muryan su Ibrahim suna ihun murna ga Baba ga Baba, har rigen-rigen fitowa muke a tsakar gida muka gan su suna kokarin wucewa dashi d'akin shi.

Duk sai murnan mu ya koma ciki ganin yanayin shi kad'ai ya tabbatar mana ba karamin wahala ya sha a hannun su ba, rufa musu baya mukayi jiki a sanyayaye suka kwantar dashi a parlour shi nan kowa ya shiga yi mishi sannu ans barka da arziki.

Gwaggo Aisha da tunda abin nan ya faru bata tab'a shiga cikin mutane ayi jaje da ita ba sai kawai ganin ta mukayi sulum ta fado parlour harda kukan munafurci wai ai tunda aka kama shi ta shiga halwa tana addu'a bata fito ba sai yau da taji labarin fitowan shi.

Cike da mamakin karya da ta sambad'o kowa yake kallon ta amma babu wanda yace mata wani abu sai Baban Dije da ya shiga mayar mana labarin yanda baba ya shiga hannun sojoji dalilin Yaya na Abdulbasit.

Jagwab na koma ta zauna dabas tare da fashewa da kuka sosai , na tausayin Yaya na Allah sarki ashe ba abinda nake tunani bane ashe babban sadaukarwa yayi da soyayyar mu dan ya ceci rayuwata , ina ma zan iya ganin shi yanzu ina ma ina ma..........

Zafar kuwa zuciya da kishi me ya d'ebe shi ya bar mana parlour ba tare da kowa ya lura dashi ba dan a tunanin shi kukan rabuwa dashi nake yi.....

[2/23, 8:12 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*60&61*

Tunda muka d'auki hanya motan ya d'auki shiru babu mai magana cikin mu,kaina a kasa ina wasa da yatsun hannu na, shine dai yana tukin hankalin shi yana kaina sai juyowa yake yana kallo na dan baya so mu zauna shiru in har muna tare.

Tunawa yayi da babu abinda yake sakani farinciki da nishafld'i kaman hiran 'ya gidan mu yasa yace;

"yau baki kawo mana kayan dad'i a wajan Momy ba ko?" Yace yana d'an dube-dube ta wajan kafa na, ban san lokacin da murmushi ya tsubuce min ba na d'an kalle shi naga shima ni d'in yake kallo ya wani narkar da fuskar shi kaman yaro mai ji da shawgwab'a, sauke nawa idon nayi cikin sauri jin yanda zuciyata ta harba da karfi sabon kaunar shi na bin jikina nace;

"Ban kawo komai ba kasan muna can muna ta murnan dawowan Baba shiyasa Babu wanda ya mayar da hankali wajan yin wani abu a gidan dama naso sai dare ka dawo na san Inna zata yiwa Baba special amma shine ka dawo da wuri...." Nima na karashe cikin shawgwab'a da ya kara tafiya da imanin shi.

"Ohhh Soo sorryy my babe ban san cewa kina bukatan kaiwa dare ba ai da ban zo yanzu ba nd kema da naki laifin why not ki Kira ni ki fad'a min time d'in da kike son zuwa na" yace min cikin muryan lallqshi.

Ban bashi amsa ba amma har cikin raina naji dadin maganan shi, haka ya rinka jana da hira har muka iso gida shi ya bud'e min kofan motan muka shiga ciki ni dai sai kallon shi nake ta kasan ido ina mamakin sauyawan shi.

A parlour ya zube Yana" gosshh I'm tired" murmushi nayi na wuce ciki ina ce mishi "sai kace da kafa ka dawo gida?"

"Babu maraba 'yan mata na zo ki dafa mana abinci kalan na Momyn mu, I'm damned hungry" yace min cikin d'an d'aga murya yanda zan iya jiyo shi, ban bashi amsa ba sai dariya da nayi na ajiye su jakana na fito zuwa kitchen.

Tunanin me zan dafa mana mai sauki na tsaya yi sai gashi ya fad'o kitchen d'in yana " pls ina abincin nan da kika tab'a yiwa su Abba irin shi, kiyi mana shi dan Allah".

Zaro ido nayi nace " kai tuwon ndalayi.... wallahi akwai wahala fa" na karasa cikin shawgwab'an da ya kara zautar dashi domin yana bala'in son yaga ina yin hakan sai dai ba ko yaushe yake nasaran gani ba.

"Alright just cool anything else you want since daga hannun ki ya fito na san it will be delicious" yace cikon sanyi da kasala da suka sauko mishi lokaci d'aya, ni kuwa na zata saboda nace ba zan girka choice d'in shi bane ya zama haka cikin sauri nace " no shi zan girka mana saboda nima it's my favorite amma akwai sharad'i in ka aminci?"

Sai da ya jingina da fridge d'in dake bayan shi sannan yace " wani irin sharad'i ne haka?" Ya karasa yana aika min da wani irin kallo da ya haddasa min dauke ido na daga kan shi babu shiri.

" Tare zamuyi zaka taya ni aikin " nace ina dariya, nad'e hannun rigan shi ya fara yana " dame zan taimaka miki?"

"Laaaaa! Wasa fa nake maka kaje ka zauna yanzu zan gama insha Allah" nace masa ina cigaba da dariya.

"No ai tunda kika fad'a hakan toh tabbas tare zamuyi, ki bani ko albasa da tomatoes in yanka miki".

"Albasa akwai zafi fa ba zaka iya ba" na kara ce mishi . " No don't worry just give me" yace yana kara gyara tsayuwan shi a jikin kitchen cabinet d'in, ban musa mishi ba na dauko albasan daidai yanda nake bukata da wuka da chopping board na ajiye mishi sannan na juya na kama aikina.

Jan hanci da yake akai akai yasa na juya na kalle shi, ban san lokacin da na tuntsire da dariya ba harda dukawa kasa ganin Zafar da hawaye shame shame kuma bai fasa yankawan ba.

Shi kuwa tsayawa yayi yana kallo na wani abu yana tsirga mishi a zuciyar mai kama da nishald'i nishad'i farinciki farinciki dan bai tab'a gani na ina dariya haka ba, ashe in ina dariya nafi kyau, inko hakane zai kara d'aura dantse wajan ganin ya sanya ni cikin dariya kullum.

Yana kallo na tare da cigaba da yanka albasan shi fuskar shi cike da annuri mai kayatarwa, "ouchhh" yace yana jefar da wukan sakamakon yanke yatsan shi da yayi abinka da lafiyayye nan da nan sai ga jini kaman an bud'e tap, had'iye dariyan nayi babu shiri na taso da gudu na kama hannun.shi da yake yarfewa mukayi wajan sink na bud'e tap na saka hannun shi a kasan ruwan yana wankewa sai sannu nake jera mishi.

"Kaga abinda nake gudu ko? Gashi ka yanke yatsanka ji yanda jini yake zuba " nace ina kokarin d'aure inda ya yanke da farin handkie saboda jinin ya tsaya, shi kuwa kawai kallon fuskana da yake mai dauke da damuwa kaman in fashe da kuka haka nake ji.
Chapter 63 · 0% Book details