← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 42 OF 71

Sashe 42

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Duk wannan kokarin da nake bai hanawa in 'yan rashin mutuncin nashi suka motsa ya sauke su a kaina, ina dai daurewa bana nuna mishi rauni na sai na koma daki nake cin kuka na in more duk rayuwar gidan ya ishe ni.

Yau tunda na farka nake ta murna saboda a yau za'ayi yinin bakwai kuma a gidan nan za'a yi shi kaman yanda al'ada yake, babban farinciki na harda Inna za'a zo shima iyayen shi zasu zo a hadu gaba daya asan juna a kara karfafa zumunci.

Irin gyaran da nayiwa gidan yau na musamman ne tun 7:30 na shirya cikin wata hadaddiyar shadda ta blue dinkin doguwar riga yasha zubi har kasa, duk da ban iya wani d'aurin kirki ba na kokarta nayi yanda zan iya kuma cikin ikon Allah yayi kyau sosai sai na kara zama Amarya sak, duk d'auki ya hana ni sukuni sai kallon time nake ina jin lokaci baya tafiya, ina zaune ina ta kallon agogo naji an murd'a handle din kofan parlour cike da murna da d'auki na mike na tafi da gudu dan in rungume duk wacce ta fara zuwa, da gudu na kwasa nayi kofan sai dai kamin in karasa naja wani wawan briki na tsaya a tsoroce tare da mayar da kai na kasa.

Shiru banji yayi min magana ba Kuma banji alamun ya tafi ba, ina ta ayyanawa a rai na kila ya tafi ne in ba tafiya yayi ba me zai tsayar dashi anan? Hakan da na saka a raina yasa na dago da kaina karaf ido na a cikin nashi yana min wani kallo da ni dai ban san fassaran shi ba, mayar da kai nayi na shiga gulman shi a zuciya ta mutum sai shegen fadin ran tsiya da iyayi....

"Meye na gaya miki last time akan gidan nan?" Muryan shi ya katse min gulman shi da nake.

"Kace in rika share gidan nan kullum...."

"And then?" Ya katse ni tun kamin in karasa.

"Ina yi kuma harda girki" daki na fa?" Ya kara katse ni.

Harga Allah bai zata da gangan na zubar da ruwa ya fad'i ba a wancan ranan Kuma yaji dad'in gyaran da nayi mishi shiyasa ya biyo ni, ni kuma a tunani na ya sani shiyasa naki shiga d'akin kada ya kama ni na San halin shi na cin zali.

"Kayi hakuri zan rinka gyarawa " na bashi amsa cikin sanyin murya.

"Better " yace tare da juyawa ya fita nabi shi da ido har ya b'ace min dan yayi min masifan kyau cikin riga armless da wando 3 quater duka farare ne tass anr rubuta Gucci da manyan harufa da bakin fenti a gaban rigan mutum yana ganin well builded body shi a zahiri ga gashi kwance luf a fatan jikin shi kaman wani balarabe.

Kofan na rufe na dawo na zauna jiki na duk a mace me yasa kwanan man nake jin wannan yanayin in muna zaune waje daya kuma duk abinda yake yanzu birge ni yake ba kaman da danake jin haushin shi ba.

9:00 am dot Yasmeen da kannen ta 2 suka zo cikin farinciki na taro su bamu zauna a babban parlour ba naja zuwa nawa muka zauna naja karamin kanin ta da ba zai wuce 7 years ba ina tambayan shi ya sunan shi? Dan Allah ya daura min son k'ananan yara ko dan babu a d'akin mu ne oho.

"Muhsin " ya amsa min da karamin muryan shi mai dad'i, murmushi nayi nace " sunan ka mai dad'i".

"Aunty Amarya kin gan mu da sassafe ko, wlh muhsin ne ya takura mana tunda ya farka daga bacci yana ta kuka shi lalle sai an kawo shi nan shine fa da ya ishi Momy da fitina tace muzo kamin ta karaso" Yasmeen ta katse ni da murmushi a fuskar ta..

"Ni ai Muhsin ya burge ni ina zaune ni kad'ai kaman mayya gashi na samu abokanen hira, kema kince zaki dawo ban Kara ganin kafar ki ba tun ranan da kika fice daga gidan nan" na bata amsa ina dan dariya.

"Cab ai Momy ce ta hani ni zuwa wai zan zo in takura ku" ta karasa itama tana dariyan.

Kawar da wannan maganan nayi na kawo wata hirar daban nake tambayar ta ya matakin karatun ta yake, ta amsa min da zata rubuta jamb tayi joining next year, naga ashe matakin mu daya da ita a karatu.

*****************

Tun goma da rabi na safe gidan mu ya fara tara mutane amma na jiki sun zo ne dan raka Inna taga gida na, su Aunty's dina sune farko-farkon zuwa amma Inna tace musu babu inda zata je bata shirya zuwa a yau ba sai wani lokacin.

Ba yanda ba suyi da ita ba tace su suje kawai ta riga ta shirya duk kayayyakin da zasu kai min kaman su kayen lefe na da sauran kayan da ba'a samu kaiwa a ranan bikin ba, Aunty Batul cewa tayi shikenan tayi zaman ta tunda hankalin ta yaki kwanciya da zuwan nata.

Ita kuma Aunty Fatima bata yiwa kowa magana cikin su ba ta fita a gidan zuwa gidan Yar uwar su wato Maa ta same ta zaune cikin shirin tafiya su kawai take jira, tana ganin Aunty Fatima ta mike tana nad'a latfayan ta tace " aini tun d'azu ku nake jira sai yanzu Bintun ta gama ne?"

"Bintu fa cewa tayi babu inda zata je wai sai dai mu muje..." Ban gane babu inda zata je ba, zuwan uwa taga gidan 'yar ta ranan bakwai ai al'ada ce da ta kafu tuntuni balle tace akan ta za'a fara, maza wuce kice mata ta fito yanzu kuzo mu tafi".Maa ta katse ta a zafafe.

Ba musu Aunty Fatima ta juya zuwa gidan mu dama zuwa tayi ta fad'awa Maa ta san ita kad'ai ce zata iya saka ta zuwa ko bata so.

Masu rakiya duk sunyi jigum jin cewa uwar Amarya ba zata je ba Aunty Fatima ta shigo taja ta gefe tace mata maza ta shirya inji Maa su tafi, ba yanda ta iya haka ta shirya suka kama hanya a motoci kusan 3 da aka aiko musu daga gidan su Zafar.

Ni kuwa hira sosai muka Sha da yasmeen Wanda yawanci labarin Yayan ta take bani kan yanda yake tsoron Abban shi Kuma hakan baya hana shi tsula tsiyar shi Mom tana rufa mishi asiri, sosai nake ta shan dariya harda rike ciki bamu tsagaita ba saida su Maryam suka zo sannan ta bar labarin nashi muka shiga wata daban.

Sai bayan azahar su Inna suka iso baki na ya kasa rufuwa da gudu na fad'a jikin ta na kenkeme ta ina hawayen farinciki, ajiyar zuciya Inna take ta saukewa akai akai na kwanciyar hankali dan bata ga alamun tashin hankali a tare da ni ba.

Sai a lokacin ta samu kwanciyar hankali ganin gida tana ta jero min addu'oi a zuciya na samun farinciki mai daurewa a gidan mijina, duk wani abu na tarban baki maman Yasmeen ta aiko mana har manyan kuloli na abinci dan haka bamu nemi komai ba aka shiga serving din baki mu dai muna can ciki muna ta hayaniyar mu.

A daidai wannan lokacin Momyn Zafar da gayyar ta suka iso ,sai huhhura hanci suke suna kallon mutane a d'age su Inna basu kula su suka karbe su da hannu 2 har ana ce musu ga wajan Zama budan bakin wata daga cikin su tace;

"Yau naga ikon Allah mu da gidan dan mu wasu bare ke kokarin nuna mana iko" ta karasa harda rike haba irin abin ya bata mamakin nan, Aunty Batul da bata da hakuri kaman gudawa ta yunkura zata basu amsa Inna da take kusa da ita tayi saurin rike hannun ta Maa da suke zaune opposite da ita ta girgiza mata kai alaman kada tayi magana.

Haka ta koma ta zauna tana ta girgiza kafa bala'i na cinta, su Kuma sai da suka gama dariyar su na wulakanci sannan suka nemi waje suka zauna suna zama cikin ikon Allah ko sai ga Maman Yasmeen da wasu mata 3sunyi sallama sun shigo da fara'ar su a take fuskar Momyn Zafar da mutanen ta ya kuntata dan basuyi tsammanin zuwan ta a wannan lokacin ba sun so su gama tsula tsiyar su kamin ta iso ba dan wai suna tsoron ta ba sai dan sun san duk abinda da sukayi zaije kunnen Abba kuma bata manta warning din da yayi mata ba akan bikin ba.

A mutunce suka gaggaisa dasu Maman Yasmeen har suna tambayan ina 'yar su take basu ganta ba , Aunty Fatima ce ta shiga ta fito dani bayan ta nada min laffaya ta kara bulbule ni da humra.

A kunyace Kuma kaina a kasa na gaishe su suka amsa da kulawa banda su Momyn Zafar da suke amsawa kaman anyi musu dole ko masu ciwon baki, ina gama gaishe su ko minti 1 ban kara ba na koma ciki daman gaba daya a takure nake jina a wajan.

Zuwan Baawa duk ya rusawa Momy badget kuma zaman su a inuwa daya babu riba dan haka suka mike da niyyan tafiya Baawan taso tsaida su amma suka ki tsayawa suka Kara wuta, suma ba wani jimawa sukayi ba suka ce zasu tafi aka rabu cikin mutunci.

Karfe 3 su Inna suma sukayi haraman tafiya suka saka ni a gaba da nasihu sosai masu ratsa jiki sannan suka tafi suka bar ni ina ta kuka, su Maryam dasu Yasmeen suna ta bani baki suka taya ni gyara gidan sannan suma suka wuce suka bar ni.
[6/16, 9:20 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Chapter 42 · 0% Book details