Sashe 4
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Cikin ikon Allah satin hulan 4 Inna ta kammala shi baiyi kyau irin na kwararre ba amma da yake cikin tsafta ta dinka shi babu datti ko kad'an a jiki sai ya zama abin sha'awa.
Ya'ana wacce ta koya mata itama ta gama nata zata kai sayarwa Inna tace muje tare sai ta sayar a bani kud'in kasancewar ita zata wuce gidan kakanni ta daga can kuma zata kwana 2 kamin ta dawo.
Bayan ta shirya ta biyo min muka tafi can London ciki wai can sun fi sayan hula da daraja, dubu da dari biyar aka sayi na inna ta ita kuma Ya'ana dubu tara aka sayi nata da saboda ita nata tangaran ne.
A leda baki ya'ana ta kulle min kud'in ta saka ni a napep na zuwa anguwan mu ita kuma ta wuce,muna zuwa kusa da layin mu suka sauke ni suka wuce.
Har nazo kusa da layin mu na had'u da wani mutum yace min," ke ana sadaka a wacan kwanan" kamin in bashi amsa wasu yaran su 4 suka zo wucewa ya fad'a musu ba musu suka bi hanyan daya nuna nuna musu,ganin sun bi hanyan yasa nima na bisu a guje muna shan kwanan ashe mutumin yana bin mu sai muryan shi muka ji yana cewa," kai ku tsaya in akwai abu a hannun ku,ku kawo in ajiye muku kar ya fad'i wajan karb'an sadakan".
Gaba d'aya mu muka mika mishi duk kud'add'en hannun mu da alamu suma sauran yaran aiken su akayi,yana karb'a yace mana ga gidan can mu shiga shi yana jiran mu anan.
Ga gudu muka shiga gidan da sunan karb'an sadaka amma me sai aka ce mana ai ba anan akeyi ba,wata da zata girme mu a ciki tana jin haka ta fita da gudu muka mara mata baya amma muna fita muka nemi mutumin nan sama ko kasa muka rasa shi,kuka ko wannen mu ya fara dan sai yanzu muka gane cewa ashe b'arawo ne yayi mana dabara ya sace mana kud'add'en mu.
Gefen titi na samu nayi zama ta ina kuka na kasa komawa gida in naje me zan cewa Inna ta bayan kwanaki tayi min fad'a akan irin haka sai gashi na maimaita,bayan haka hulan nan yanda ta dage tayi ta d'inka shi ba dare ba rana dan ta samu saka ni a secondary school amma sai in koma ince mata wani ya min dabara ya kwace? gaskiya ba zan iya komawa ba.
Ina zaune ina kuka na d'aya daga cikin yaran da shima an sace mishi kud'in yazo ya zauna kusa dani muka cigaba abin mu,kaman daga sama naji ance," kanwata yauma kukan kike?"
Da sauri na d'aga kaina dan ganin waye sai naga wannan bawan Allah daya biya min kud'in jarrabawa ne hannun shi rike da bottle water inaga a shagon kusa damu ya saya ga mutane a wajan suna ta shiga da fita babu wanda ya kula mu sai shi da yazo yanzu.
Kin kula shi nayi na d'auke kaina ina goge hawayen ido na.
"Kai meya same ku kuka zauna anan kuke kuka?"ya tambayi yaron kusa dani.
Shi kuwa kama jira yake ya fad'a mishi duk abinda ya faru nan ya tambayi shi nawa ne kud'in?.
"Dari uku ne akace in sayo taliya da mai da maggi" ya bashi amsa.
Dari biyar ya ciro a aljihu usual sabo dal ya bawa yaron,cike da murna yaron ya karb'a yana godiya ya ruga da gudu ya tafi shagon kusa damu ya sayi kayan yanda ya fad'a ya dawo mishi da canjin shi,amma sai yaki karb'a yace ya tafi ya bar mishi.
Murna fal ranshi ya kama hanyan gida da gudu ya bar mu a wajan,ganin ban bi yaron ba yace min," ba tare kuke bane?" Jiki a mace na girgiza kaina saboda na zata yaron yana amsan kudin zai zama doya kaman yanda inna ta ta fad'a sai naga ba haka bane lafiya lau yayi sayayyar shi ya tafi gida.
"Ke kuma nawa ya sace miki?" Muryan shi ya katse min tunanin da nake.
"Kud'in hulan Inna ta ya karb'e gaba d'aya" na bashi amsa.
"Stop crying kanwata kinji,gashi karb'i ki kai mata".
Kallon kud'in na tsaya yi ina tunanin in karb'a ko a'a?
"Karb'a mana ki goge hawayen ki" saka hannu 2 nayi na karb'a cikin sanyin murya nace," nagode!"
Girgiza min kai yayi ya ce," kada ki damu tashi ki tafi gida".
Da azama na tastashi nayi gidan mu ba tare da nasan nawa ya bani ba.
A gida kuwa Inna duk ta damu tana tunanin me yasa na dad'e haka,tana ganina ta sauke ajiyan zuciya ta ce," zareefa me yasa kika dad'e haka?"
Banyi kasa a guiwa ba na kwashe duk abinda ya faru na gaya mata,karban kud'in tayi ta kirga taga dubu uku ciff,fincikoni tayi da karfin tsiya na fad'i akan simintin d'akin na bud'i baki zanyi ihu ta ce kada na kuskura inyi mata ihu anan dole na had'iye kukana ina zaro ido saboda ganin Inna ta ta fusata yau sosai.
" Wato ke ba kya jin magana ko zareefa duk abinda na gaya miki ta bayan kunnen ki suka wuce ko,baki san ki kama kan ki a matsayin ki na ya mace ba duk ko wani d'an iska ya baki kud'i karb'a kike yau kuma harda bin wani, Inna ilahi wa inna ilahi rajiun!!!
Toh tunda kunnen kashi gare ki yau zanyi maganin ki wallahi" ta karasa tare da murd'e min kunne.
Sosai ranan inna tayi min abinda tunda na san kaina bata tab'a yi min ba daga baya tayi min nasiha sosai mai ratsa jiki.
Tun daga wannan rana nayi hankali ya kasance babu ruwana da duk abinda zai had'a ni da wanda ban sani ba sosai na kama kaina.
Kullum Baba inya shigo gida Gwaggo Aisha itace zatayi ta dawainiya dashi dan ko Maman su Hafsa bata samu wannan matsayi a wajan shi ba,shi irin mazan nan ne da mace in zata rike shi tayi mai komai toh dad'i zaiji kwata-kwata bashi da zuciya d'aukan nauyin iyali da Allah ya d'aura mishi shiyasa gidan namu kullum sai kara hargitsewa yake.
Maman su Hafsa abin na damun ta sai dai babu yanda ta iya tayi-tayi amma ta kasa kamo Gwaggo Aisha dan tafi ta samu nesa ba kusa ba.
Ranan wani juma'a daya kasance girkin inna ta ne kuma a ranan munyi sa'a Baba ya kawo mana masara kusan kwano 10 ya ce a nik'a tunda babu garin tuwo.
Maimakon manyan gidan su kai sai suka ce ba zasu kai ba tunda ba girkin iyayen su bane,shikenan sukayi zaman su babu wanda ya ce musu wani abu.
Dole yasa wheelbarrow inna ta aro ta saka min a ciki ta ce in kai, ina turawa da kyar na kama hanya na fita a gida ga kuma inda zan kai nikan da d'an tazara da gidan mu.
Inna ta ana cewa tana da girki a gidan ne amma baba baya shigowa d'akin ta kaman yanda yake shiga sauran d'akin matan shi kuma baya cin abincin ta,na sha jin yana cewa nima Allah ne ya kaddara sai na taka duniya amma har yau yana jin takaicin wannan abin.
Na isa lafiya sannan nabi layi har aka zo kai na aka nik'a min mutumin shiya taimaka ya mayar min cikin wheelbarrown na kama hanyan dawowa gida.
Ina cikin turawa jikina duk gumi ban san taya wannan yaron ya shiga gaba na ba da keken sa da alamu ma dan koyo ne dan da kyar ma in ya kaini shekaru,duk yanda naso kaucewa amma abin bai yiwu ba saboda nik'an da nauyi kamin kace me dani dashi duk muka zube a wajan tare da kurkurjewa buhun nik'a na kuma sai cikin kwata da yake kusa damu.
Hannu 2 na d'aura a kai na rusa ihu ina gari na dan ko zafin kurjewan na daina ji saboda nasan in na koma gida babu garin nan wallahi Baban mu zai iya babbake ni da raina.
Sosai nake kuka kaman raina ya fita mutane sun taru suna mana sannu ko jin su bana yi har yaron ya d'auki keken shi ya tafi babu wanda ya hana shi kasancewar karami ne babu abinda zai iya yi.
"Oh not again yauma kuka take,meya same ta?"naji muryan shi kaman daga sama.
"Karo sukayi da me keke nik'an ta ya fad'a kwata" wani yaro ya bashi amsa yana nuna mishi buhun da aka ciro a kwata wanda ko akuyoyi ba zasu iya cin garin da yake ciki balle mutum.
Baice komai ba ya koma ya motan shi ya wuce,ajiyar zuciya nayi da Allah yasa bai ce zai ban wani abu ba yau,mutane suna bani bakin in tashi in tafi gida amma kirmitsitsi naki motsawa balle su saka ran zan tashi.
Bayan kaman mint 5 na kara jin muryan shi yana cewa," ga wannan tashi in ajiye ki a gidan ku".
Kallon inda yake nayi naga buhun shinkafa da wasu kwalaye harda jerrican mai ana saka mishi a boot din mota,kaman wanda aka jona da remote na tashi jiki na na b'ari na fara tura wheelbarrow na da gudu nayi hanyan gida na bar shi tsaye anan.
Ana gama saka masa kayan ya tambaya ko akwai wanda ya san gidan mu anan?
Wani yaro yayi caraf yace ya san gidan mu gashi can babu nisa sosai daga nan.
Motan shi ya shiga tare da cewa yaron yazo ya raka shi,ba musu yaron ya shiga suka bi baya na.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*_4_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Addu'ar Tsayuwa a Kan Dutsen Safa da Na Marwa*
Jabir, Allah ya yarda da shi ya ce, yayin da yake siffanta hajjin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; yayin da ya kusanto dutsen Safa sai ya karanta:
Ya'ana wacce ta koya mata itama ta gama nata zata kai sayarwa Inna tace muje tare sai ta sayar a bani kud'in kasancewar ita zata wuce gidan kakanni ta daga can kuma zata kwana 2 kamin ta dawo.
Bayan ta shirya ta biyo min muka tafi can London ciki wai can sun fi sayan hula da daraja, dubu da dari biyar aka sayi na inna ta ita kuma Ya'ana dubu tara aka sayi nata da saboda ita nata tangaran ne.
A leda baki ya'ana ta kulle min kud'in ta saka ni a napep na zuwa anguwan mu ita kuma ta wuce,muna zuwa kusa da layin mu suka sauke ni suka wuce.
Har nazo kusa da layin mu na had'u da wani mutum yace min," ke ana sadaka a wacan kwanan" kamin in bashi amsa wasu yaran su 4 suka zo wucewa ya fad'a musu ba musu suka bi hanyan daya nuna nuna musu,ganin sun bi hanyan yasa nima na bisu a guje muna shan kwanan ashe mutumin yana bin mu sai muryan shi muka ji yana cewa," kai ku tsaya in akwai abu a hannun ku,ku kawo in ajiye muku kar ya fad'i wajan karb'an sadakan".
Gaba d'aya mu muka mika mishi duk kud'add'en hannun mu da alamu suma sauran yaran aiken su akayi,yana karb'a yace mana ga gidan can mu shiga shi yana jiran mu anan.
Ga gudu muka shiga gidan da sunan karb'an sadaka amma me sai aka ce mana ai ba anan akeyi ba,wata da zata girme mu a ciki tana jin haka ta fita da gudu muka mara mata baya amma muna fita muka nemi mutumin nan sama ko kasa muka rasa shi,kuka ko wannen mu ya fara dan sai yanzu muka gane cewa ashe b'arawo ne yayi mana dabara ya sace mana kud'add'en mu.
Gefen titi na samu nayi zama ta ina kuka na kasa komawa gida in naje me zan cewa Inna ta bayan kwanaki tayi min fad'a akan irin haka sai gashi na maimaita,bayan haka hulan nan yanda ta dage tayi ta d'inka shi ba dare ba rana dan ta samu saka ni a secondary school amma sai in koma ince mata wani ya min dabara ya kwace? gaskiya ba zan iya komawa ba.
Ina zaune ina kuka na d'aya daga cikin yaran da shima an sace mishi kud'in yazo ya zauna kusa dani muka cigaba abin mu,kaman daga sama naji ance," kanwata yauma kukan kike?"
Da sauri na d'aga kaina dan ganin waye sai naga wannan bawan Allah daya biya min kud'in jarrabawa ne hannun shi rike da bottle water inaga a shagon kusa damu ya saya ga mutane a wajan suna ta shiga da fita babu wanda ya kula mu sai shi da yazo yanzu.
Kin kula shi nayi na d'auke kaina ina goge hawayen ido na.
"Kai meya same ku kuka zauna anan kuke kuka?"ya tambayi yaron kusa dani.
Shi kuwa kama jira yake ya fad'a mishi duk abinda ya faru nan ya tambayi shi nawa ne kud'in?.
"Dari uku ne akace in sayo taliya da mai da maggi" ya bashi amsa.
Dari biyar ya ciro a aljihu usual sabo dal ya bawa yaron,cike da murna yaron ya karb'a yana godiya ya ruga da gudu ya tafi shagon kusa damu ya sayi kayan yanda ya fad'a ya dawo mishi da canjin shi,amma sai yaki karb'a yace ya tafi ya bar mishi.
Murna fal ranshi ya kama hanyan gida da gudu ya bar mu a wajan,ganin ban bi yaron ba yace min," ba tare kuke bane?" Jiki a mace na girgiza kaina saboda na zata yaron yana amsan kudin zai zama doya kaman yanda inna ta ta fad'a sai naga ba haka bane lafiya lau yayi sayayyar shi ya tafi gida.
"Ke kuma nawa ya sace miki?" Muryan shi ya katse min tunanin da nake.
"Kud'in hulan Inna ta ya karb'e gaba d'aya" na bashi amsa.
"Stop crying kanwata kinji,gashi karb'i ki kai mata".
Kallon kud'in na tsaya yi ina tunanin in karb'a ko a'a?
"Karb'a mana ki goge hawayen ki" saka hannu 2 nayi na karb'a cikin sanyin murya nace," nagode!"
Girgiza min kai yayi ya ce," kada ki damu tashi ki tafi gida".
Da azama na tastashi nayi gidan mu ba tare da nasan nawa ya bani ba.
A gida kuwa Inna duk ta damu tana tunanin me yasa na dad'e haka,tana ganina ta sauke ajiyan zuciya ta ce," zareefa me yasa kika dad'e haka?"
Banyi kasa a guiwa ba na kwashe duk abinda ya faru na gaya mata,karban kud'in tayi ta kirga taga dubu uku ciff,fincikoni tayi da karfin tsiya na fad'i akan simintin d'akin na bud'i baki zanyi ihu ta ce kada na kuskura inyi mata ihu anan dole na had'iye kukana ina zaro ido saboda ganin Inna ta ta fusata yau sosai.
" Wato ke ba kya jin magana ko zareefa duk abinda na gaya miki ta bayan kunnen ki suka wuce ko,baki san ki kama kan ki a matsayin ki na ya mace ba duk ko wani d'an iska ya baki kud'i karb'a kike yau kuma harda bin wani, Inna ilahi wa inna ilahi rajiun!!!
Toh tunda kunnen kashi gare ki yau zanyi maganin ki wallahi" ta karasa tare da murd'e min kunne.
Sosai ranan inna tayi min abinda tunda na san kaina bata tab'a yi min ba daga baya tayi min nasiha sosai mai ratsa jiki.
Tun daga wannan rana nayi hankali ya kasance babu ruwana da duk abinda zai had'a ni da wanda ban sani ba sosai na kama kaina.
Kullum Baba inya shigo gida Gwaggo Aisha itace zatayi ta dawainiya dashi dan ko Maman su Hafsa bata samu wannan matsayi a wajan shi ba,shi irin mazan nan ne da mace in zata rike shi tayi mai komai toh dad'i zaiji kwata-kwata bashi da zuciya d'aukan nauyin iyali da Allah ya d'aura mishi shiyasa gidan namu kullum sai kara hargitsewa yake.
Maman su Hafsa abin na damun ta sai dai babu yanda ta iya tayi-tayi amma ta kasa kamo Gwaggo Aisha dan tafi ta samu nesa ba kusa ba.
Ranan wani juma'a daya kasance girkin inna ta ne kuma a ranan munyi sa'a Baba ya kawo mana masara kusan kwano 10 ya ce a nik'a tunda babu garin tuwo.
Maimakon manyan gidan su kai sai suka ce ba zasu kai ba tunda ba girkin iyayen su bane,shikenan sukayi zaman su babu wanda ya ce musu wani abu.
Dole yasa wheelbarrow inna ta aro ta saka min a ciki ta ce in kai, ina turawa da kyar na kama hanya na fita a gida ga kuma inda zan kai nikan da d'an tazara da gidan mu.
Inna ta ana cewa tana da girki a gidan ne amma baba baya shigowa d'akin ta kaman yanda yake shiga sauran d'akin matan shi kuma baya cin abincin ta,na sha jin yana cewa nima Allah ne ya kaddara sai na taka duniya amma har yau yana jin takaicin wannan abin.
Na isa lafiya sannan nabi layi har aka zo kai na aka nik'a min mutumin shiya taimaka ya mayar min cikin wheelbarrown na kama hanyan dawowa gida.
Ina cikin turawa jikina duk gumi ban san taya wannan yaron ya shiga gaba na ba da keken sa da alamu ma dan koyo ne dan da kyar ma in ya kaini shekaru,duk yanda naso kaucewa amma abin bai yiwu ba saboda nik'an da nauyi kamin kace me dani dashi duk muka zube a wajan tare da kurkurjewa buhun nik'a na kuma sai cikin kwata da yake kusa damu.
Hannu 2 na d'aura a kai na rusa ihu ina gari na dan ko zafin kurjewan na daina ji saboda nasan in na koma gida babu garin nan wallahi Baban mu zai iya babbake ni da raina.
Sosai nake kuka kaman raina ya fita mutane sun taru suna mana sannu ko jin su bana yi har yaron ya d'auki keken shi ya tafi babu wanda ya hana shi kasancewar karami ne babu abinda zai iya yi.
"Oh not again yauma kuka take,meya same ta?"naji muryan shi kaman daga sama.
"Karo sukayi da me keke nik'an ta ya fad'a kwata" wani yaro ya bashi amsa yana nuna mishi buhun da aka ciro a kwata wanda ko akuyoyi ba zasu iya cin garin da yake ciki balle mutum.
Baice komai ba ya koma ya motan shi ya wuce,ajiyar zuciya nayi da Allah yasa bai ce zai ban wani abu ba yau,mutane suna bani bakin in tashi in tafi gida amma kirmitsitsi naki motsawa balle su saka ran zan tashi.
Bayan kaman mint 5 na kara jin muryan shi yana cewa," ga wannan tashi in ajiye ki a gidan ku".
Kallon inda yake nayi naga buhun shinkafa da wasu kwalaye harda jerrican mai ana saka mishi a boot din mota,kaman wanda aka jona da remote na tashi jiki na na b'ari na fara tura wheelbarrow na da gudu nayi hanyan gida na bar shi tsaye anan.
Ana gama saka masa kayan ya tambaya ko akwai wanda ya san gidan mu anan?
Wani yaro yayi caraf yace ya san gidan mu gashi can babu nisa sosai daga nan.
Motan shi ya shiga tare da cewa yaron yazo ya raka shi,ba musu yaron ya shiga suka bi baya na.
[8/31, 6:05 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*_4_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Addu'ar Tsayuwa a Kan Dutsen Safa da Na Marwa*
Jabir, Allah ya yarda da shi ya ce, yayin da yake siffanta hajjin Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi; yayin da ya kusanto dutsen Safa sai ya karanta: