← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 71

Sashe 18

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fita yayi rai a b'ace yana ta masifa shi yasa kai zai fita da sauri ya koma baya yana tunanin anya idon shi dai-dai ya nuna mishi kuwa?

Kara lek'a kan shi waje yayi yaga dai da gaske ne Yaya na ya gani fuska a murtuke wai shi ala dole yayi fushi me yasa ban fad'a mishi maganan saukar namu ya d'auki nauyin komai na ba nayi da kai na.

"Innalillahi wa inna ilahi rajiun wai shi wannan yaro banda bala'i irin nasu na sojoji meya kawo shi da rana tsaka yana muzurai sai kace anyi mishi dole" Baba ke fad'in haka bayan ya koma cikin zaure ya manne da bango wai duk dan kada Yaya na ya gan shi.

Da kyar na shawo kan sa ya daina fushin muka ci gaba da hiran mu cikin annashuwa da shaukin soyayya, abinda bamu sani ba ashe Baba yana nan mak'ale a zaure yana jiran tafiyan Yaya na ya samu shima ya tafi majalisa, yaki komawa cikin gida kuma saboda rigimar su da Gwaggo Aisha kada taga ya koma ta mishi dariya.

A takaice mun kai good 1 hour sannan mukayi sallama ya wuce ni kuma na shigo gida cikin farinciki hannu na d'auke da sayayyar da yayi min.

Ina shigowa zaure saura kad'an in zubar da kayan hannu na saboda firgita ganin mutum manne a jikin bango yana goge zufa, sai da na tabbatar Baban mu ne sannan na samu natsuwa amma kuma mamaki da tambaya fal cikin zuciya ta me kuma yau Baba yake a nan ?

Hanyan fita ya nufa yana masifa kallon inda nake bai yi ba hakan ko ya kara saka ni cikin konkonto, a yanda nasan Baba da son dad'i amma yau ko kulanin baiyi ba bayan ga shopping bags a hannu na, juyawa nayi da niyyan shiga gida naji muryan Baban mu yana," wallahi Allah yau yaron nan ya cuce ni, in banda ina gudun abin kunya cikin anguwa kada a ce ga Mallam Hassan can yana fad'a da sirikin sa ba Allah da na nuna mishi ko ni waye, Aikin banza wa zai yiwa barazana har kofar gida har da wani sako kayan sojoji toh sai me...?"

Dariya na tintsire da shi har da dukawa sai yanzu na gane me Baba yake a zaure, da kyar na tashi na kwashi kayana zuwa cikin gida.

Bayan kwana 2 akayi bikin saukar mu a islamiyar mu wanda ya tara duban jama'a ciki kuwa har da Yaya na sai dangin Inna a 'yan gidan mu Inna Asabe ce kad'ai ta tafi dan Gwaggo Aisha cewa tayi karatun karuwanci dama nake shine yau kuma za'a je party toh ba da ita ba.

Bajintar da Yaya na yayi ba a cewa komai kayan rabo kala-kala ya kawo aka raba harda na malamai suma nasu daban ga gifts nima daya kwaso min ba zasu lissafi ba duk da haka cewa yake komai ya min gani yake bai yi ba saboda sauke Al' Qurani mai girma ba abin wasa bane.

A islamiyar ma na samu kyauta daban-daban saboda hazaka ta daga karshe taro ya watse bayan mun sha pics saboda tarihi.

*************************

Wato ka mai da ni mutuniyar banza a gidan nan saboda ban isa in fada kaji ba ko, fisabillilahi ka kyauwa kan ka kenan?"cewar wata 'yar dattijuwa mai kamala da kyau da haiba wacce ba zata haura shekaru hamsin ba.

Wani kyakkyawan saurayi ne zaune a gaban ta shi take takewa fad'a amma shiru yayi kan shi a kasa yana kallon lallausan rug da yake malale a katafaren parlour nasu wanda kallo daya zaka mishi ka kira shi da aljannan duniya domin babu ne kawai babu a ciki, just ku hasaso shi a cikin zuciyar ku domin in nace zan tsaya zayyano muku tsari da kyan gidan sai mu kusan cika novel din bamu gama ba

Duk da kan shi a kasa yake bai hana ni hango dogon hancin sa ba ga sajen sa baki wuluk na lallausan gashin sa sun kewaye fuskar shi, gashin kan sa kuwa kaman na larabawa saboda laushi da tsantsi sai dai yayi mata wani aski wanda an kwashe daga gefe-gefe da keya sai tsakiya da ta gaba ne da gashi kana ganin gashin ka san ya sha gyara da kulawa wajan mai shi.

"Zafar... Wai ba da kai nake magana ba ka min shiru" wannan kyakkyawar dattijuwar ta fad'a cikin tsawa.

Wanda ta kira da Zafar ya d'ago kai masha Allah ashe da kan sa yake kasa ban ga komai ba sai yanzu.

Zafar fari tas irin farin nan mai yellow yana da dogon hanci wanda ya kawata kyakkyawan fuskan shi ga maidaicin bakin sa mai d'auke da jajayen lips sun kara fiddo ainihin kyan fuskar sa, idon sa kuma kaman mai jin bacci suke a takaice Zafar ya had'u iya had'uwa sai dai ya kasance d'an shan minti ne kasancewar shi d'a tilo ga multi millionaire.

A shagwab'e ya d'ago da kai yana d'an tale baki kaman d'an karamin yaro alhalin ya kai shekaru ashirin da takwas yana kallon mahaifiyar tashi da lumsassun idon shi da baturai sukewa lak'abi da sexy eyes ya ce," wai ya kuke so inyi ne Mom for god sake ni komai nayi kice bai yi ba, look at dis " yace yana nuna mata gashin kan sa sannan ya cigaba.

"Wats wrong with it nayi wancan kunce baiyi ba nayi wannan ma kice baiyi ba then which 1 do u want me to do?" Ya karasa yana watsa hannayen sa cikin iska.

Wacce ya kira da Mom ido kawai ta zuba mishi ta kasa cewa komai domin lamarin tilon dan nata ya fara bata tsoro a ce d'an da ka haifa shi zai rink'a mayar maka da magana haka, babu wanda yake shaka a gidan sai Abban shi, sanin haka yasa ta cewa," ok haka kace ko? Kaje kayi duk abinda kake so amma kafin ka fita inayi maka albishir da gobe Abban ka zai taso daga Portugal zuwa gida sai ka tanadi bayanin da zakayi mishi in ya ga askin naka".

A rikice ya dawo kusa da ita, da ya kai har tsakiyan parlour da niyyan komawa part d'in shi yana zuwa ya zauna a gaban ta tare da d'aura hannayen shi duka 2 kan guiwoyin ta ya ce," na san ko Abba ya dawo my sweet Mom zata kare ni kaman yanda ta saba ko Mommy naaaa just once daga wannan shikenan ba zan kara ba I promise shima wannan dan zamu yi bachelor's eve na Musaddiq ne shiyasa".

Murmushi tayi tana shafa gashin kan nashi ta ce," promise.. promise dai wanda ban san sau nawa aka yi min su ba remember jiya me kace?"

Dafe goshin sa yayi yana d'an tuno yanda yake mata in taki yi mishi abu, zai fara yi mata ta dakatar dashi tana," bana son wannan shagwab'an naka jeka let me think about it"

"Yesss.... dats my sweet Mom" yace yana d'an tsalle a gaban ta sannan ya fita da gudu yana dariya, itama dariyan take a zuciyar ta kuwa tana blaming kan ta da duk abinda Zafar yake itace sila domin a koda yaushe itace mai kare shi wajan Abban sa in yayi wani laifi, ita da kan ta bata jin dad'in abinda take wasu lokutan amma ya zata yi shine fa kad'ai kwan ta a duniya dan ma Allah ya tsare baya wasu mugayen dabi'un na 'yan zamani shi dai bar shi da zuwa parties da kula 'yan mata sai kuma son swagger.

*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[1/26, 7:04 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

*13*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*13*

Yana fitowa daga parlourn Mommy shi fara'an fuskar sa ta d'auke lokaci daya dif kaman wutan NEPA sai ma wani shan kamshi da yake wanda ya kara fiddo da kyan sa, a nan na fahimci wato babu mai ganin wannan fara'ar tashi sai mahaifiyar sa.

Wani haÉ—aÉ—É—en madaidaicin flat house ne dake gefensa na mahaifan sa, ya nufa ko kula masu aiki da suke gaida shi baiyi ba ya shige abin sa.

"Dude ka san I have been waiting for you amma ka wani shanya ni, tun dazun su Sabeer suka dame ni da waya wai kowa ya hallara sai mu ake jira" cewar wani guy dake zaune kan sofa shima kana ganin shi kaga classic guy saidai ko rabin kyan Zafar bai kai ba.
Chapter 18 · 0% Book details