← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 71

Sashe 27

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai da aka fara sallah a sauran masallatai sannan ta tashe ni na fita nayi alwala nazo na kabbara sallah, ko azkar kasawa nayi saboda baccin dake cin ido na kara bingirewa nayi na cigaba abina anan Inna ta fahimci bacci bai ishe ni ba jiya cikin tausaya min ta kama 'yan aiyukan ta nan cikin d'akin ba tare da ta fita ba, bata kawo komai a zuciyan ta ba duk a zaton ta ban dawo dai-dai daga shock na rabuwa da Yaya na ba.

A wannan Gwaggo Aisha tayi bine-binne ta a mashigar kitchen d'in mu ta saka kujera a k'ofar d'akin ta tana jira mu fito mu tsallaka kaman yanda bokan ta yace.

Cikin ikon Allah Inna itama baccin ta koma tunda babu wani abu na azo a gani da zatayi, cikin bacci muka ji kaman ana tonon abu cikin k'asa, ko motsi banyi ba amma na farka sai Inna tace tayi karfin halin fitowa jin muryan maza kuma bakin murya ya cika gidan.

Maza tayani sun kai su biyar kowanne da abu a hannun shi yana tono Baban mu na tsaye daga gefe , kamin Inna ta bud'i baki tayi tambayi me yake faruwa suka ji muryan Gwaggo Aisha tana" kai! Kai!! Ku dakata me kukeyi haka?"

Duk suka juyo suna kallon ta duk ta had'a zufa sai wurwurga ido take, Baba ne ya bata amsa da " meye naki na ihu haka sai kace gidan ki ake tono,

Toh gini zanyi zan canza ginin gidan nan ya zama na zamani".....
[1/26, 7:12 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*21&22*

"Haba Mallam ba zaka bari mu d'an kimtsa ba gyara da sassafe haka?" Gwaggo Aisha ke fad'an haka cikin matukar tashin hankalin gani za'a saka ta wahalan banza.

"Wani irin kimtsawa sai kace daga kofar ki aka fara, ki bari in aka zo kofar ki sai ki kawo korafin naki" Baban mu ya amsa a dakile.

"Ni ba wani abu nake nufi ba naga safiya ce kuma ai ko ita Bintun zata so a bar ta ta d'aura abin karyawa ita da 'yar ta, ko ba haka ba Bintu?" A zuciyar ta kuwa tana ta addu'an Allah yasa Inna ta amince da abinda ta fad'a a fasa tonon sai bayan mun shiga kitchen d'in mu munyi girki, kamin nan mun sallake abubuwan da ta binne shiyasa dama ta zab'i binnewa a kofar kitchen d'in mu sanin ba wanda zai taka wajan sai mu.

"A'a in ta nine bakomai suyi aikin su, ba zamu rasa yanda zamuyi ba, wannan ai abin farinciki ne kuma cigaba ne muma zamu zama 'yan gayu" Inna ta amsa tana dariya sauran mutane da suke wajan suma dariyan sukayi suka cigaba da aikin su ba tare da sun lura da halin da sun lura da halin da Gwaggo Aisha ta shiga ba.

Afujajjan ta shiga d'akinta sai safa da marwa take duk ta had'a zufa ta kasa zama sai neman hanyar da zata dakatar dasu take amma kasan zuciyar ta kuwa gargad'i take mata na kar ta tsauwala har ta tonawa kanta asiri cikin mutane, da wannan shawaran ta nemi waje ta zauna sai karkad'a kafa take tana sharce gumi,Hajara tana ankare da ita amma taki tanka mata.

Ni kuwa tunda naji Baba yace ginin zamani za'a yiwa gidan mu na kasa ko daga yatsa na sannan kuma na tabbatar da zancen bawan Allah nan na jiya gaskiya ne kenan in ba haka ba ina Baba yaga kud'in ginin zamani,

"Ya Allah ka dube ni ka fidda ni cikin wannan fitinan" nace cikin raina.

Basuyi wani nisa ba suka fara tono tsirkullen Gwaggo Aisha, cikin mamaki suka tsaya cirko-cirko suna kare musu kallo an rasa mai magana cikin su.

"Mu cigaba da aikin mu mana" cewar d'aya daga cikin su.

"Kaman yaya mu cigaba bayan wannan abubuwa da muka tono,kamata yayi a sanarwa mai gidan sai ya san matakin da zai d'auka" nan duk sukayi na'am da shawaran nan suka tura karamin cikin su kiran Baba.

"Innalillahi wa inna ilahi rajiun" shine Kalmar da Inna ta samu daman maimaitawa fitowar ta kenan daga bayan gida taga sun tara tsirkullen a gefe suna ta tattaunawa akai.

Kasa wucewa tayi tana mamakin me ya kawo layu da guraye kofan kitchen d'in ta, fargaba fal a zuciyar ta na kada ace itace ta binne su,har Baba iso wajan tana tsaye sai ambaton sunan Allah take.

"Wannan ai ba wani abin tada hankali bane, ta yiwu tun na kakanin mune sune zasu iya ajiye irin wayan nan abubuwan su jima haka kasa haka" cewar Baba kenan cikin rashin d'aukan abin da muhimanci.

"A'a wayanan tsurkullen basu dad'e a kasa ba ta, da gani kwananan aka binne su" cewar d'aya daga cikin su.

"Matsalaha daya ne shine a k'ona su kurmus in ma mai shi da wata manufa ya binne toh zai zo da sauki"

Inna da jikin ta yayi sanyi sosai barin ma irin kallon tuhuma da taga Baba na aiko mata da shi yasa duk taji ba dad'i, tana jin anyi maganan konawa yasa cikin sauri ta wuce d'aki ta d'auko ashana a cikin drowern d'aki inda take ajiyewa in ta sayo kwali.

Kamin ta fito har sun tara su a gefe sun zuba kalanzir suna neman ashana, Baban mu ta mikawa ta koma gefe ta tsaya babu b'ata lokaci wanda ya karba ya ketta ashana bayan yayi addu'oi nan da nan kuwa wuta ya kama ya fara ci bakin hayaki na tashi a jiki kaman ana kona taya.

A d'akin Gwaggo Aisha kuwa tunda aka cinnawa layun nata wuta ta fara ganin d'akin na juya mata ga wani zafi-zafi da take ji a jikin ta kaman ana hura mata wuta, tun tana iya daurewa har abin yafi karfin ta ta fara ihu tana birgima a tsakiyar d'aki.

Sharewa nayi kaman banji ba dan nima ina fama da nawa matsololin inda zan samu daman ihun nima da nayi ko zanji sauki cikin raina.

Tsaki naja ina mikewa tsaye da d'an sauran kuzarin daya rage min na fita saboda yanda naji ihun yaki tsayawa kuma kana ji kasan wanda yake yana cikin mamuyacin hali.

Kus-kus na tarar masu aikin nayi ban kula su ba nayi wucewa ta zuwa d'akin Gwaggo Aisha da zan iya kirga shiga ta ciki tunda aka haife ni.

Da gudu na karasa nima ina kokarin rike ta kaman yanda naga Inna da Hajara sukayi Inna sai tofa mata addu'oi take, ban tsaya b'ata lokaci ba nima na fara taya ta muka cigaba da tofa mata har ta daina birgima sai jikin ta da yake rawa sosai, tuni Baban mu ya fice abin shi zuwa d'akin shi ya bar mu da ita.

Mun Kai good 30 mins muna yi mata sannan ta dawo hayyacin ta sai ajiyan zuciya take a kai- akai hawaye na bin gefen fuskan ta amma koda wasa bata bud'e ido ba, ganin taji sauki yasa Inna mikewa tacewa Hajara ta lullub'a mata abin rufuwa da alamu ta samu bacci, amsawa tayi da toh tare da mana godiya muka fito zuwa d'akin mu Inna bata zauna ba ta d'auki dubu d'aya ta bawa Ibrahim kan ya sayo mana abin karyawa a waje.

Tunda ta bada sakon ta dawo d'aki ta zauna shiru na san shirun nata baya rasa nasaba da abinda ya faru a safiyar yau, ba Inna da take shekaru ba ko ni nan na fahimci abinda ya faru da Kuma musababbin ta.

Allah sarki Inna ta kamin ka samu mai irin zuciyar ta a wannan zamnin sai an tona, tsab ta gane komai amma taje tayi mata addu'a, da wata ce sai dai ta mutu ko nice nan Yasin ko kurar da ya debo ki ba zan kallah balle har in nema miki waraka barin ki zanyi ki girbi abinda kika shuka.

Shi kuwa Baban mu akwai shi da kyaluwa ba kasafai kake gane mishi ba in ba harkan kud'i bane, ko ya fahinmci abinda ya faru ko bai fahimta ba oho.

*************

A b'angaren Zafar kuma yau cikin farinciki ya tashi ko ba komai ya ragewa kan shi tention da kuma fad'an Abban shi, ba komai yake kara mishi nishad'i ba kaman in ya tuno da hiran shi da Abban shi jiya a kaina.

Murmushi ya kara saki lokacin da ya tuna Abba shi yace" ina matukar alfahari da kai ka birge ni sosai da ka tashi neman aure baka nema cikin 'ya'yan masu kud'i ba ka nema a irin gidan da nake son in samu sirka,

Naji dad'i da baka bi halin mahaifiyar ka ba na wajan kin talaka, da mai kud'i da talaka duka Allah ne yayi mu saboda hikimomin shi ba yayi hakan bane dan baya son su ba.
Chapter 27 · 0% Book details