← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 71

Sashe 19

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ko inda yake Zafar bai kalla ba ya wuce bedroom d'in sa da yaji royal bed fari kal,komai na d'akin farare ne hatta da curtains tsab'a parlour kuma komai na ciki royal blue ne, bai tsaya cikin bedroom d'in ba ya fad'a bathroom domin yin wanka.

Girgiza kai Sadiq yayi ganin Zafar yaki kula shi ya wuce ciki in da sabo yaci a ce ya saba kam duk da cikin abokan sa jinin su yafi had'uwa da Sadiq d'in kuma tare suka taso tun suna kanana har zuwa girman su babu abinda ya tab'a raba su ko a makaranta.

Baban Sadiq yana da wadata shima amma ko rabin kudin su Zafar bashi dashi, saboda aminitar dake tsakanin su 2 yasa iyayen su maza da mata kulla zumunci sannan Baban Zafar shi yake biya Sadiq kud'in makaranta ganin cewa shine farincikin d'an su.

Zafar yana da fara'a sosai da wasa da dariya amma fa sai ga Mommy sa dan ko shi Sadiq da suke tare shekara da shekaru bai cika ganin dariyar sa ba sai jifa-jifa wanda shima in mutum ya bibiya toh yaga abin mugunta ya sami shi Sadiq d'in anan zaki ga dariyar sa harda rike ciki.

Zafar yana da wani hali ko kuma ince buri, ya raina 'yan matan mu na gida kwata-kwata basa burge shi a cewar sa bai ga abin so ba a tare dasu ba, 'ya'yan masu kud'i da masu fad'a aji na cikin kasar nan babu wacce bata kawo mishi kokon barar soyayyar ta ba duk yayi watsi dasu dan ko kallo basu ishe shi ba,sai dai in zasu tafi party wanda sai da chick ake zuwa toh shine zai kula ki shima da ya fito shikenan amfanin ki ya kare amma hakan ma farinciki wacce ta samu wannan daman take ko ba komai ta samu na canza status kenan tana sham kamshi cikin kawayen ta.

Wannan halin nashi yasa mutane da yawa suke mishi kallon mai neman mata alhalin ba haka yake ba.

Murya... Ya d'aga cikin k'osawa da zaman jira da yake ya ce " man wai me hakane, sai b'ata mana time kake pls ka fito mu tafi ba party zuwa da beb bane in dan wannan kake ja mana...…"

Ganin ya fito yasa ya had'iye sauran maganan shi yana bin shi da kallo ko makiyin shi ne bai isa ya kushe shi ba, toh duk iya dai bin kwakwafin mutum babu abin kushewa a halittar sa dan ko dama aka bashi aka ce yayi kan sa iya kar sa kenan.

Ya matukar had'u cikin dark blue polo shirt da wandon jeans baki sosai kayan sun matukar dacewa da farar fatar shi sai canvas dark blue dake kafar shi sai zuba kamshin tsadaddun perfumes din shi yake kasancewar sa mai son kamshi shiyasa baya amfani da turare daya kusan 4 ko 5 yake amfani dasu at a time dan haka ba zaka tab'a bambamce kamshin da yake ba.

Yana gyara agogon Rolex dake hannun shi ba tare da ya kalli inda sadiq yake zaune ba yace,' muje"

Girgiza kai kawai yayi ya mike yabi bayan shi dan har ya fita basu tsaya b'ata lokaci ba suka fad'a wata sport car d'in sa suka fice daga gidan.

********************

Gidan mu dai yana nan yanda kuka san shi babu abinda ya canza cikin zamtakewar da muke, cikin shekaru 2 da suka shud'e sai dan abinda ba za'a rasa ba, muna final year a makaranta sai shirye-shirye rubuta waec muke hankali kwance.

In ka san ni a shekaru 2 da suka wuce ba lalle ne ka gane ni yanzu ba na canza matuka na kara wayewa ga girman jiki dana kara sosai ,kyau na kuwa ba'a magana duk inda na wuce sai an dad'e ana magana ta wasu ko cewa suke wai ni balarabiya ce,ko a makaranta na sha raba musu musu cewar ba abinda ya had'a ni da larabawa ni asalin hausa Fulani ce amma wasu basa yarda sai dai suce b'oyewa nake bana son asan gaskiya.

Godiya sun tabbata ga Allah mahallacin komai da kowa sannan ga mutane 2 na cikin rayuwa ta wanda a dalilin su na zama abinda na zama wato Yaya na da besty na Maryam, dukan su 2 sun taka muhimmiyar rawa a rayuwa ta.

Yaya na shine gata na shine abin alfahari na ba dan shi ba da ban kai wannan matsayin da nake ba, sai Maryam ita ta kasance kaman roll model na domin komai na 'yan gayu ita ta koya min na fito cikin 'yan mata masu aji, dalilin Maryam da ta nace muka shiga wani catering school da sai da muka shafe watan ni sannan aka yaye mu yanzu ba wani nau'in girki da ban iya ba da snacks da drinks kala-kala, mostly in Yaya na zai zo sai nayi mishi.

Auren Yayan Maryam shi muka saka a gaba da za'ayi nan da wata 3 masu zuwa,sosai muke zuba tsare-tsaren mu dan so muke muke mu fita daban cikin 'yan biki.

Soyayyar mu da Yaya na kuwa sai abinda ya karu domin a kullum kaman kara wutan son junan ake a cikin zukatan mu tun Inna tana d'ari-d'ari har ta saduda ta tabbatar son so yake min lokaci kawai ake jira da zaran na kammala secondary school na za'a saka mana rana, tsakani na dashi ban san wa yafi zumud'i ba kullum cikin kirga kwanaki muke na zuwan lokacin.

Tsakanin su da Baba kuwa 😂😂 babu abinda ya canza dan Baba baya tab'a yarda su had'u duk yanda Yaya na ya kai ga son su gana amma yaki yarda kowani lokaci akwai excuse da zai nemo ya bada dan kaurace had'uwan nasu.

Dije anyi auren ta kusan wata biyar da suka wuce ta auri mijin ta mai suna Bala ba mai arziki bane amma akwai wadatar zuci da rufin asiri, ko bikin ma kowa sai son barka yake kasancewar anyi komai cikin tsari.

Hajara tana gida an kawo ta wanka satin da ya wuce bayan ta haifi d'a ba rai sakamakon yawan dukan da take sha wajan mijin nata ga yunwa da yake barin ta dashi sai dai Gwaggo Aisha tayi musu aike na kayan abincin domin yanzu tana samu ko sana'a ta daina yi duka bukatun ta Jameela ta d'auke mata su sakamakon samari masu kud'i da ta samu amma fa a cewar Gwaggo Aisha kenan dan ni dai ban tab'a ganin wani yazo kofar gidan mu neman ta da sunan zance ba sai dai inga taci kwalliya cikin matsattsun kaya ta fita kan zata je gidan kawaye in anyi sa'a ta dawo cikin dare ta kwana a gida wata rana kuma sai tayi kwana biyu bata dawo gidan ba, ta goge ta kara haske da kyau duk da hasken na shago ne.

Dawainiya kula da Yayar ta ma itace ta d'auka babu abinda ta rage ta dashi shi kuwa mijin tunda aka kawo ta gida bai kara bi ta kansu ba balle yazo ya duba ta ko yayi musu aike, wannan dalilin yasa Gwaggo Aisha d'aukan alwashin 'yar ta ta gama auren shi ko uban wa yayi mishi tsaye ta gama auren shi kenan.

Hura hanci da d'aukan kai da Gwaggo Aisha take a cikin gida sai wanda ya gani Inna Asabe take kula ta wani lokacin suyi tayi dan Inna ta kam ko iskar daya d'ebo ta bai ishe kallo ba.

Sosai take kokari na son ta burge Baban mu dan ta dawo da matsayin ta na da amma hakan ta bai cimma ruwa ba kasancewar Baban mu gaba d'aya hankalin shi ya dawo kan Inna ta domin ita komai zata yi mishi ko ta bashi bata yi mishi gori tsabanin Gwaggo Aisha da sai ta tsaya a tsakar gida take mishi terere kowa yana ji yana gani hakan yasa Baban fifita Inna fiye da kowa a gidan ita kuma Gwaggo Aisha wannan dalilin yasa tace asiri Inna tayi mishi kuma ko zata tafi tsirara sai ta karya shi.

*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

*14*

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Addu'ar Mash'arul Haram*

Jabir, Allah ya yarda da shi, ya ce: Manzon Allah, tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya hau taguwarsa mai suna Al-Kaswa har ya zo Mash'arul haram, sai ya fuskanci alkibla ya yi addu'a ga Allah, ya yi kabbara, ya yi hailala, ya kadaita Allah. Bai gushe ba a tsaye yana addu'a har sai da gari ya waye sosai, sannan ya dauki hanya kafin rana ta fito.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*14*
Chapter 19 · 0% Book details