← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 71

Sashe 17

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da mamaki na d'ago na kalle ta na ce", ni fa kanwar Amaryar ce ga Amaryan can" na karasa ina nuna musu inda Hajara da kawayen ta sukayi sororo suna kallon mu.

"Eh ga Amaryar can wannan kanwar ta ce " wata kanwar Gwaggo Aisha ta fad'a tana harara ta.

Jiki a tsabule suka juya ga Amaryan su suna kallon ta har taji ta muzan ta, ni dai ban san ya suka kare ba na shige cikin gida na bar su.

Da daddare bayan an kai Amarya gidan ta Dije tazo d'akin mu a lokacin ina kwance ina chatting da Yaya na.

"Zo...zo...zo muje ki sha labari zo muje" ta ce tana jan hannu na ina ta tsaya in ajiye waya amma ina haka taja ni muka tafi bangaren su.

"Mijin Hajara da ake cewa mai kud'i ne ashe karya ne,kin ga gidan nata gidan yawa mutane sun fi shida a ciki ga d'akin nata ya yiwa kayan ta kad'an ke abun b dad'in gani wallahi.

Ina matar da ta zo tace ita 'yar uwar sa ce tayi magana a kan an fasa dinner ashe gidan haya ce ta had'a su".

*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*
[10/10, 7:42 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

*✍✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇

https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp

_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._

*12*

Bangane ba Hajara me kike nufi wai?" Na tambayi Hajara cike da rud'u.

Kamo hannu na tayi muka zauna a bakin k'ofar d'akin su sannan ta fara magana," hmmmm duk abinda Alhaji Khalid mai gidan gona ya fad'a a gidan nan ashe zuki ta malle ne sunan shi haladu kuma sana'ar sa kuma bawa dabbobi abinci a gidan gonan Alhaji Mukhtar dake Sabon layi".

Samun kaina nayi da matukar jin haushin sa sannan ga tausayin 'yar uwata daya rufe ni lokaci guda,cikin wani irin yanayi nace", amma Allah ya isan Hajara makaryaci kawai in bashi da kud'in menene amfanin shirga mata wannan karyan? Allah sarki Hajara ko wani halin take ciki yanzu?"

"Lalle Zareefa kin bani mamaki meye naki na wani zakewa haka, wallahi kada ma kiji tausayin ta ita ta jawowa kan ta ko ince su suka jawo dan harda uwar ta su ala dole dake zasu yi gasa, chab ni wallahi ko kad'an bata bani tausayi ba hasali ma dariya ta nayi ta sha, a mota ina ta tunanin yanda Gwaggo Aisha zatayi in taji wanga batu" ta karasa cikin shekiyanci tana dariya.

Girgiza kai na nayi hawaye na taruwa a ido na, na ce mata," Dije kenan taya ba zan tausaya mata ba ko kin manta cewa 'yar uwata ce jini d'aya yake yawo a cikin jikin mu"

"Na sani mana amma ba kya ganin yanda suka saka ki a gaba su da iyayen su sun hana ki sakat ke da mahaifiyar ki tun muna kanana har zuwa girman mu"

"Koma menene Dije su d'in 'yan uwa na ne, jini d'aya yake yawo a jikin mu daurewa kawai nake ina share su amma ina kaunar su har cikin raina ina kuma sha'awa in ga mun had'a kan mu kaman sauran 'yan uwa"

Hawayen da ya zubo min na share na mike na kama hanyan bangaren mu itama Dije ko motsi kasawa tayi dan maganganu na sun kashe mata jiki,ko da na shiga d'akin mu na samu Inna zaune gefen gado ta rafka tagumi da alamu itama taji zancen kenan.

"Tun d'azu ake kiran wayan ki" ta ce min ba tare da ta sauke tagumin ba saboda wannan al'amari ya bata mamaki da tsoro samarin yanzu mayaudara ne kuma macuta ne, in banda cuta kazo da wata siffa da suna dan a baka mata me yasa ba zai zo a yanda yake ba? Ko da yake Maman Dije ta ce wai sun riga sun nunawa duniya cewa in ba mai kud'i ba akai kasuwa shine yasa shi zuwa da wannan siffa.

Ajiyar zuciya ta sauke wanda sai da na juya na kalle ta dama rply na tex nake rubutawa 'yar ajin mu a islamiya ta kira bana kusa shine ta min tex tana min tuni kan abubuwa da muka shirya na walimar mu.

"Inna lafiya kuwa na gan ki haka?" Na tambaya.

"Hmmmm ba komai je ki wanke min hijabi na da da yake cikin bukiti a waje" da toh na amsa na fita wankin.

Ina fara wankin naga Gwaggo Aisha sun shigo da kannen ta 2 duk sunyi wujiga-wujiga ko kallon inda nake ba suyi ba suka wuce, a zuciya ta na ce," chab Gwaggo Aisha ana cikin tashin hankali tunda bata harare ni ko ta tsaya ta zage ni ba, lalle yau tana cikin matsala, d'aki suka shige suna neman mafita.

Har gari ya waye ba'a cimma abu d'aya ba sai shige da fice suke, sun samu Baban mu da maganan yace toh me zai mata, ta riga da ta fita a hannun sa lafiya dan haka sauran ya rage musu ita da mijin ta.

Gwaggo Aisha takaici ya hana ta sauran sauran bayanin nashi tayi ficewar ta, ta rasa ina zata kai kukan ta a share mata hawaye, babban burin ta shine a raba auren domin jiya da daddare ita da kannen ta daga gidan Hajaran suke suka ja mata kunnen kada ta yarda ta bashi kan ta duk rintsi duk wuya dan gobe-goben za'a raba auren nasu sai gashi har sha biyu ta kusa babu alamun nasara ko kad'an.

Gwaggo Aisha bata gama shiga tashin hankali ba sai da d'ayan kanwar ta da ta tura gidan Hajara dan a dubo mata lafiyr ta ta dawo da mummunan labarin cewa Haladu yayi nasaran kusantan Hajara jina-jina suka same ta abun babu kyan gani ko taimaka mata bai tsaya ba ya tsallake ta yayi tafiyar shi.

"Yanzu fisabillilahi duk fad'an da muka yi mata sai da ta sakewa wannan mayaudarin jiki ya gama da ita?" Gwaggo Aisha ke tambaya tana goge hawaye da gefe zanin ta.

"Ba laifin ta ba ne shi mijin ne tantiri, ta bamu labarin komai cewa da ta fara mishi taurin kai shine d'aure ta a jikin gado yayi abinda ya ga dama da ita wai bata isa ta hana shi more kud'in sa ba" 'yar uwar ta ta bata amsa.

"Amma wannan yaro anyi tsinanne Allah ya isa tsakani da shi, ina zan shiga da wannan abin kunyan, kayyah " yanzu kam kuka Gwaggo Aisha take tsakani da Allah tana tunanin tayaya zata kalli idon 'yan gidan bayan duk abubuwa da tayi musu wai ita 'yar ta zata auri mai mota.

"Mama kada ki tada hankalin ki domin nayi miki alkawarin saka ki farinciki, ba zan tab'a kula kowa ba kuma ba zan auri talaka ba sai mai kud'i" Jamila ke fad'an haka da take sauraron su tun d'azu ba tare da sun sani ba,d UK kallon juna suka tsaya yi babu wanda ya iya bata amsa sai dai ita Gwaggo Aisha ido ta zuba mata tana nazari tare da hasko yiwuwa da nasara a cikin abinda ta fad'a domin Jameela tafi Hajara kyau da tsarin jiki nesa ba kusa ba.

Haka akayi wannan wunin a tsaye babu wanda ya lek'a gidan Amarya wasu ma saboda bakinciki a ranan suka koma inda suka fito shiyasa gidan namu ya zama shiru kaman ba biki ake ba.

Bayan kwana 2 da bikin Hajara Yaya na yazo da rana bayan azahar cikin kananan kaya wandon kaman na sojoji sai bakin t shirt da bakin glass sosai yayi kyau, muna hira a kofar gidan mu yana tambaya ta me da me nake bukata a walimar saukar mu? Ni kuma ina ce mishi bana bukatan komai duk abinda ake bukata mun gama shirya su.

A wannan lokacin ashe Baba yana gida ya dawo saboda wata bukatar shi lokacin da yazo Yaya na bai zo ba yana ciki ya zo dan haka bai san da zuwan shi ba,yana d'aki Gwaggo Aisha tabi shi tana magiya akan yayi wani abu akan al'amarin Hajara a raba auren domin muddin tana raye ba zata tab'a barin auran nan ya dad'e ba.

Bata san duk haushi ya cika shi ba tazo ta ishe shi da surutu alhalin shi in ya tuna tsoro ya hana shi gaisawa da Yaya na da yanzu yana cikin kud'i yanzu gashi bashi da kud'i a hannu, tsaki yaja yana bin ta da mugun kallo ya ce," ke Aisha wai wace irin mace ce ke da zaran kin ga mutum ya shigo gida sai ki bi shi da korafin ki na banza da na wofi yarinya tana gidan mijin ta shine kike neman wai ni uban ta inje in fito da ita wannan wani irin rashin kan gado ne, toh ba dani ba wallahi kije can ki gama haukan ki kada ki kara tunkara ta da wannan iya shegen ko kuma ranki yayi mugun b'aci". Yana gama maganan shi ya mike a fusace zai fita ya juyo ya ce," ba sai kin kara gani na a gidan ba balle ki zo ki takura ni"
Chapter 17 · 0% Book details