← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 71

Sashe 55

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Saura kiris wayan shi ya Fad'i saboda tsoratan da yayi na ganin mutum cikin parlour shi ba tare da yaji koda motsin shigowan shi ba, cike da takaici ya nufo shi ganin cewa Zafar ne ya shure shi da kafa yana" wallahi kai banza ne ,wani irin iskanci ne haka zaka shigo min babu ko sallama" .

Bud'e idon shi da sukayi ja ya zuba mishi ba tare da yace mishi komai ba na second 10 sannan ya maida kayan shi ya rufe, zama akan handle din kujeran Sadeeq yayi yana sauke numfashi dan babu karya ya san abokin nashi yana cikin matsala kwana 2 nan.

"Haba Zafar me yayi zafi ne haka kake neman saka kan ka a damuwa, ni dai a iya sani na ban san abinda zai saka a irin wannan yanayin ba tunda ba abinda ka rasa tun tasowar mu, please calm down and tell me what is going on?" Yace mishi cikin rarrashi.

Shiru yayi bai bud'e idon ba Kuma baiyi magana ba tun Sadeeq na sa ran zaice wani abu har ya cire saboda ganin shirun yayi yawa , yana shirin mikewa yaji ya bud'i baki cikin sanyin murya yace " na rasa ya zanyi ban tab'a tsintan kaina a cikin irin wannan yanayin ba".

Zama Sadeeq ya gyara tare da bashi dukkan attention d'in shi jin yanda yake magana so calm kaman ba Zafar da ya sani a baya ba.

"A kullum so nake in zauna a inda take inyi ta kallon ta dan idanuna basa taba gajiya da kallonta, jiki na da gangan jiki na basu da wani buri da ya wuce su ji dumin jikin ta, hanci na kullum cikin kishirwan kamshin jikin ta yake haka kuma kunnuwa na basa tab'a gajiyawa da jin zazzakar muryan ta.................. Hmmmmmm" yaja dogon numfashi sannan ya cigaba " but ba yanda banyi da ita ba ta tsaya ta saurare ko zamu samu mafita amma taki ta bani dama". Ya karasa tare da bud'e idon shi dake cike da damuwa ya zubawa Sadeeq dake jifan shi da wani kallo dan duk a zaton shi zancen wata macen yake bani ba.

"Hmmmm wacece haka kuma ?" Sadeeq ya tambaya cikin halin ko in kula.

Lumshe idon ya karayi sannan ya amsa mishi da " ZAREEFA...."

Waro ido Sadeeq yayi fuskar shi na nuna zallan farincikin da yake ciki yace " shegen gari kace ciwon sone yake dawainiya da kai mana kazo kana wani langwab'e min kwana 2" ya karasa yana kecewa da dariyan shakiyanci

A matukar zabure Zafar ya mike yana watsa mishi mugun kallo yace " dan na gaya maka damuwata ba shi zai baka lasisin yi min wulakanci ba, kafi kowa sanin babu macen da take gaba na balle akai ga ace ni Zafar zan so ta talk less of dis village girl".

Wani dariyan Sadeeq ya Kara sakawa yana nuna shi da yatsa yace " see you, wai babu macen da take gaban ka ko, sai kace ba yanzu ka gama ce min ( jikina da gangan jiki na basu da wani burin daya wuce suji dumin jikin ta) in ba so ba menene?". Ya karasa yana kwaikwayon muryan shi.

A matukar fusace ya mike tsaye yana " BA SONTA NAKE BA kuma I will never do that na san kawai Ina samun wannan nagetive feelings d'in kasancewa I have never been with a woman before Kuma muna zaune gida d'aya shi ya kawo haka, I can pay her any amount she need to be with her just once tunda akwai igiyan aure a tsakanin mu ban aikata zina ba".

" Kai da kake kyankyamin mata baka yarda ko party ne kaje dasu shine yau kake cewa ko nawa ne zaka bata dan ka kasance da ita ko sau d'aya ne, yaro yaro ne ni tunda kace min zaka iya auren ta tun a lokacin na san there is something special about her in your heart da kaima baka san da shi ba, but for now ya kamata ka sani cewa ka riga da kayi nisa a cikin son ta....."

" Enough of this bullsheet Sadeeq kada ka kara tara ta da wannan banzan maganan, ba son ta nake ba I repeat myself ba sonta nake ba....." Ya fad'a a tsawace tare da ficewa fuuu cikin fushi kaman zai tashi sama, dariya Sadeeq yayi yana " zaka dawo ne ka same ni yaro".
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*51&52*

A gidan mu Inna ta cigaba dafa abincin sadaka suna rabarwa , Inna Asabe da Hajara suna taya ta kullum sai dai har yau Gwaggo Aisha bata ce ci kan mu ba ko Kuma ta fito su jajantawa juna game da kame Baba da akayi , kullum tana d'aki ko motsinta ba'a cika ji ba.

Ta d'auki fushi da Hajara sosai kan taki yarda su karasa aikin da suka fara akan Zafar ga kuma aikin abincin sadaka da take taimakawa su Inna ya kara tunzura ta shiyasa ko kallon inda take bata yi, itama Hajaran share ta tayi domin tana cike da takaicin halin ko in kula da take nunawa akan halin da Baban mu yake ciki dan haka kowa tsabgar gaban shi yake.

Jameela kuwa yau ta kai kusan wata bata leka gida ba sannan babu wanda ya san inda take kuma babu wanda ya damu da ya neme ta ko dan sun saba ganin haka sai ranan da taga dama take dawowa gida.

Yauma su Inna suna cikin aikin su sai gata ta shigo cikin maye kaman yanda ta saba, ko sallama batayi ba ta fad'o musu cikin gida tana layi.

Cak ta tsaya tana bin su da kallo baki bud'e cikin murya irin na 'yan maye tace " wato biki ma kuke a gidan nan shine babu wanda ya fad'a min, da ban zo na iske ba shikenan sai kuyi ya wuce ni ko? Ala dole kun mayar dani saniyar ware...."

Tab'e baki Hajara tayi ta cigaba da aikin ta ba tare da ta kara kallon inda take ba sai kanwar Baban mu Gwaggo Hinde da suka iso yau da safe ta bata amsa da " kaji min ja'irar yarinya a gidan uban wa aka ganki da za'a fada miki abinda yake faruwa a gidan, keda kika saka yawo a gaba da shaye-shaye toh uban ku sojoji suka tafi da shi yau kwana 2 bamu san ina suka kai shi ba....."

Ga mamakin su dariya suka ga ta kyalkyale dashi harda rike ciki, saida tayi mai isar ta sannan tace " dan Allah ku kaini wajan sojojin nan in basu tukuicin abinda sukayi koda round d'aya-d'aya ne, wallahi sun matukar birge ni su Baba ana can ana girban abinda aka shuka.

Ke kuma Inna ya kamata kifi kowa murnan wannan al'amarin ko dan cin kashin da yayi akan ki amma dan rashin zuciya shine wai harda ke ake addu'an fitowan shi, Allah yasa ya dauwama acan su gana mishi irin azaban da yayi ta gana mana tun tasowar mu" Tana kaiwa nan tayi hanyan d'akin su tana cigaba da wasu suratai da ita kanta bata san ma'anar su ba.

Da ido duk suka raka ta har ta shige sannan kanwar Baban mu tace " toh Allah ya shirya mana zuri'a" da ameen suka amsa mata suka cigaba da aikin da yake gaban su.

Gwaggo Aisha ce ta tare ta cike da farinciki dan duk abinda ya faru akan idon ta akayi shi domin tana tsaye ta jikin windown ta tana kallon su.

"Allah miki albarka jameela ta kece kad'ai kika biyo halina a cikin ku, inama ace baki b'ata kan ki da shaye-shaye nan ba da kin cika duk wasu buruka na da 'yar uwar ki ta kasa cika min" cewar Gwaggo Aisha.

Cikin muryar ta na 'yan maye tace " ke wai umma meyasa ba'a hiran arziki dake ne, kina wani zancen shaye-shaye ki sani ko kece kika tab'a ba zaki iya rayuwa ba sai da shi,kin san nishadi'i da ake samu kuwa in ansha......" Ta karasa harda lumshe ido alamun abinda ta fad'a har cikin zuciyar ta haka take Gwaggo Aisha kuwa kallon takaici ta bita dashi ba tare da iya cewa uffan ba.

**********************

"Kai kar ka b'ata mana lokaci ko a kara mayar da kai inda aka fito da Kai ne?" D'aya daga cikin manyan sojojin da ya fara fusata da inda-indan Baba ya daka mishi tsawa.

"A'a zan fad'a wallahi....wallahi zan fad'a ranka ya dad'e" Baba ya amsa cikin sauri.

"No ka bari a kawo d'ayan partner shi d'in zaifi sai suyi mana bayani gaba ki d'aya" cewar babban cikin su, ba musu wasu 2 daga cikin kananan sojojin suka juya zuwa wani b'angare dake can nesa dasu shi kuwa Baba har a wannan lokacin kan shi a kasa yake ya kasa d'agowa sai had'a zufa da yake kaman ana mishi wanka.
Chapter 55 · 0% Book details