← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 71

Sashe 67

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

maganan zuci da nake yasa ban san lokaci ya d'an tafi ba, ganin sha biyu ya d'an gota yasa na daura mana abincin rana, abu mara nauyi na girka mana sannan na fito na kimtsa parlor duk da ba wani datti yayi ba na share nayi mopping sannan na kunna coal na zuba turaren wuta na zallan itacen sandal.

Nan da nan ko gidan ya d'auki kamshi mai sanyaya zuciya, abincin da na gama kwashe mana cikin warmers na jera mana su kan dinning sannan na shiga wanka ganin ko ina yayi kal dashi, saida na kusan minti talatin ina wankan sannan na fito.

Zama nayi agan mirror nabi jikina da lotions masu kyau da kamshi, light make up nayiwa fuskata domin ni ba ma'abociyar son kwalliya dayawa bane.lungu da tsako na jikina nabi da body spray masu sanyin kamshi da sanyaya zuciya.

A gaban sip d'ina na tsaya ina karewa kayayyakina da suke a jere kallo ina tunanin wani kaya zan saka, cikin dube duben da nake ido na ya sauka kan wani english gown black color tsayin shi da kadan ya wuce guiwa ta sai adon stones da red flowers da akayiwa gaban rigan daya kara mishi kyau.duk da ban taba saka irin kayan tunda nazo gidan ba amma haka nan zuciya ta ta kwadaitu da saka kayan.

Ina sakawa kuwa yayi min cip na cika kayan ya lafe a jikina ya fito mun da shape d'ina sosai kayan ya min wani irin kyau nida kaina na san na canza,tsayawa nayi ina karewa kaina kallo sai naji sha'awan shafa lipstick a labba na

Red lipstick na shafa a labban nawa nan da nan ko ya kara haskani ko dan ni ba ma'abociyar lipstick bace oho.

Hijabi na zura na kabbara sallahn azahar jin har an fara sallah a wasu masallatan anguuwan.

Shi kuwa Zafar yana fita gidan su ya wuce kai tsaye ba tare da ya biya wani wajan ba,yana fitowa a motan shi bayan ya daidaita parking d'in shi ya hango Abba na saukowa daga steps d'in fitowa a parlour su cikin haraman fita hannun shi rike da 'yar brief case.

Da sauri Zafar ya karasa gare shi cikin natsuwa da ta fara zame mishi jiki ya rusuna ya gaida Abban shi, shima cikin jin dad'in canjin tilon d'an nashi ya amsa yana tambayan shi lafiya ta.

Cikin dan jin kunya ya amsa da " tana nan lafiya lau tana gaishe ku".

"Muna amsawa, daga gida kake ko"?
"Eh Abba naga kaman fita zakayi?"ya tambayi Abban yana kallon jakan hannun shi.

"Tafiyar gaggawa ce ta same ni zuwa kasar Germany, munyi order wasu kaya aka samu akasin da dole sai naje da kaina. Wayanan nan abubuwan kai ya kamata kayi su ko Kuma ka fara taya ni da wasu harkokin ne amma ban san meyasa baka son aiki ba sai zaman banza" Abba ya bashi amsa a d'an kausashe.

Murmushi yayi Yana sosa keya tare da fara in ina " ammm ummm Abba na kusa karban business din ka dawo gida ka huta da sweetie ka " duka Abba ya kaiwa keyar shi yana dariya tare da cewa " ja'irin yaro kana son maida ni kakan ka ko ganin babu su kusa da kai ko?"

Shima dariyan yayi ya nufi cikin parlour da gudu cikin nishad'i yace "safe trip Abba". Driver da tundazu yake jiran su gama tattauna tsakanin uba da d'an sa ya nufo Abban da saurin shi ya karbi jakan hannun Abban ya wuce gaba Abba na bin shi a baya har zuwa inda ya fito da motan da zai kai shi airport dashi,bayan motan ya bud'e mishi ya shiga ya zauna sannan ya ajiye jakan a gefen Abban sannan ya rufe murfin motan sannan shima cikin sauri ya zagaya ya bud'e mazaunin driver ya tada motan tare da nufo gate da mai gadi ya dade da wangale musu gate suna fita ya kama hanyan airport.

Shi kuwa Zafar da sallama a bakin shi ya shiga parlour amma bai samu Mom a nan ba sai masu aiki, direct sama ya hau zuwa dakin ta yayi sallama ya tura kofan ya shiga.

Amsawa Mom tayi tare da juyowa daga gyara gaban dressing mirror ta da take yi tana mishi sannu da zuwa.

Karasa shigowa yayi ya zauna kusa da kafar ta ya fara zuba mata shawgwab'a kaman yanda ya saba itama tana biye shi, " ga breakfast a dinning room if u re hungry" tace mishi tana shafa mishi gashin kan sa.

"Haba Mom I'm a married man fa now how comes ba zanyi breakfast ba har zuwa wannan lokacin" ya bata amsa cikin turo baki kaman karamin yaro, kamin tabashi amsa cikin sauri ya daura hannayen shi duka 2 kan guiwa ta yace" Momy guess What"?

Dan dariya tayi tana " just tell me what is going on kaima ka san I'm not good at guessing" shima dariyan yayi yace " yau ni na girka mana breakfast a gida".

Cikin mamaki Momy tace " bangane kai ka girka breakfast ba".

Gyara zaman shi yayi ya fara cewa "yes Mom yau ni na shiga kitchen tana ma bacci na girka mana breakfast chips nd fried eggs nd tea" ya karasa so excited.

Zuciyar Momy na bugawa ta kara tambayan shi" kai da ko ruwan zafi baka iya tafasawa ba ya akayi har ka soya dankali da kwai?"

"Google " ya bata amsa kai tsaye kuma cikin kwarin guiwa.

Kai ta jinjina ta tafi duniyan tunani dole nema ta tashi tsaye kamin komai ya ida juye mata, ita fa shiyasa tun farko bata maraba da wannan auren domin talaka in Bai iya samun wuri ba balle Kuma ni yar malamai.shikenan iyaye na sun asirce mata yaro da mijinta ma baki daya duka-duka yaushe akayi auren amma gashi duk mun saye zuciyar su,l Abba yayi min kyauntan company nd yanzu Kuma tilon d'an nata yazo yana fad'a mata Wai ya girkawa yar yarinya karama abinci abinda duk tsawon shekaru da sukayi tare ko sha'awan shiga kitchen d'in bai tab'a nuna mata ba?.

Tayi nisa da bata jin yanda Zafar ya dage yana mata bayani dalla-dalla ta yanda yabi yayi girkin shi cikin sauki, tab'a ta da yayi ne ya dawo da ita hayyacin ta.

"Na'am me kace boy?"

"Let me sleep kadan " yace yana hamma ya hau gadon ta ya kwanta, da ido kawai tabi shi tana tunanin abin yi

Sai kusan karfe daya ya tashi daga baccin bai tsaya bata lokaci ba ya shiga bathroom yayi alwalan azahar ya fito yayi mata sallama zai wuce gida daga masallaci, tana ce mishi ya tsaya yayi lunch before ya wuce shi kuma yace mata " no zanje gida in ci na san by now ta gama mana delicious tana jirana".ya fita abin shi

Ajiye serving spoon dake hannun ta tare da rafka tagumi da hannu 2 zuciya na kuna.

Ina idar da sallah na fito main parlour shima a lokacin yayi sallama ya shigo muna had'a ido ledan daya sayo mana fruits ya tsubuce a hannun shi suka zube a kasa, ido ya zuba min kaman ya cinye ni domin tunda muke bai tab'a gani na cikin irin wannan shigan ba ga hot red lipstick dana shafa ya bala'in tsotse mishi ruwan kai.

Hannu ya ware min alamun he needs a hug, cikin wani irin taku da ban san na iya shi ba na nufo shi.gyara tsayuwan shi yayi yana jiran in karaso, ina zuwa dab da shi har kamashin turaruka na sun fara ruda shi maimakon in fad'a jikin shi yanda yake tsamani sai gani yayi na durkusa na fara rattare fruits da ya zubar ina maida su cikin ledar.

Pls kuyi hkr kuyi manage da wannan.
[2/23, 8:16 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*.

*64&65*

Innalillahi kawai nake maimatawa a zuciyata ganin yanda ya mayar min da kitchen up side down, saboda soya dankali da kwai gaba daya ya hargisa kitchen d'in ko ina kaya ne a warwatse ga b'awon dankalin da ya b'are suma zube a k'asa.

Karasa shiga kitchen d'in nayi na ajiye kayan hannu na sannan na fara gyarawa ina yi ina maganan zuci" ina ma ace kulawar da yake bani da kuma soyayya da yake nuna min da gaske ne, dan ni kam kullum soyayyar shi ƙaruwa take a zuciyata sai dai nasan abin da yasa yake wannan draman dan ya samu jiki na ne, kuma na san yana samu ni kuma na gama yawo domin lokacin da ya d'ibawa auren mu ya kusa cika".
Chapter 67 · 0% Book details