Sashe 12
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*🖊
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Addu'ar Wanda Ya ji Tsoron Faruwar Wani Abu Mummuna saboda Kambun Baka*
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Idan dayanku ya ga wani abu da ya kayatar da shi ga dan uwansa, ko ga kansa, ko ga dukiyarsa, to ya roki Allah ya sanya albarka gare shi; domin kambun baka gaskiya ne.
*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*
_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇
https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp
_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._
*Kuyi hakuri kunji ni shiru kwana biyu kun san jiki da jini sai a hankali amma yanzu Alhmdllh naji sauki, wayan da suka kira da wayan da suka turo sakonni duk ina godiya da kulawar ku Allah ya bar kauna.
Nagode sosai*😘😘😘
*9*
"Lafiya lau yaro.... lafiya lau" Baba ya amsa yana had'iyar yawu yana kara karewa motan kallo, ni dai sanin zai kwafsa min yasa ko d'ago kaina na kasa yi bare mu had'a ido da shi.
Yayana kuwa yana gama gaishe shi bai d'ago daga tsugunen ba yayi kasa da kai yana jiran Baba ya bar wajan, Baba ba dan yaso ba yaja kafa zuwa cikin gida yaso ya samu wani abu wajan mai tsallen motan nan, amma ba komai bari yaje wajan Bintu zai ji ko wanene shi d'in.
Wata b'oyayyen ajiyan zuciya na sauke ganin ya wuce gida salin-alin ba tare da yayi wani abu daya tsinka ni ba, nabi bayan shi da kallo kaman yanda shima Yaya na yabi sa da kallo sai faman gyara mayattacen binjimar sa ta tshohuwar shaddar sa fara ce amma saboda tsufa har ta koma ruwan toka .
"Allah sarki Allah baiyi zamu had'u da Baba ba duk shekaru nan ba sai yau" naji Yaya na ya katse min tunanin da nake.
Murmushi nayi ina gyada kaina.
"Amma nima ban kyauta ba da ban tab'a tambayan shi ba all this while,wallahi yanzu dana gan shi sai naji ban kyauta ba sam" ya kara fad'a cikin damuwa sosai.
"Laa! Kada ka damu Allah ne baiyi zaku had'u ba tun farkon amma yanzu daya so ba gashi kun had'u ba" na bashi amsa ina murmushi.
Shiru kawai yayi dan shi a tunanin shi rashi da iyali ne yayiwa Baban yawa shiyasa ya zama haka bai san cewa duk wani yanayi da hali da mutum zai gan shi a ciki shi ya jefa kan sa ba.
Har muka gama hiran mu a ranan yana cigaba da nuna min rashin jin dad'in sa ni kuma ina nuna masa ba komai da zai tafi dubu ashirin ya bani wai in bawa Inna ta ajiye min in case wai ko goben ba zai samu dawowa ba, na nuna mishi muna da komai ba sai ya bani kud'i ba amma yaki karb'a saima shopping bags daya maida farilla wajan kawo min su ya lodo min kusan su 3 yana complain wai dole ya nemawa inna fridge ko dan saboda rana irin ta yau, kasancewar na saba kullum sai ya kawo min ice cream na sha toh gashi gobe baya nan da Inna tana da fridge sai ya sayo dayawa a saka min a ciki ko na kwana nawa ne.
Amma tunda ya bani 'yan canji a hannu in naga ba zan iya hakura ba sai inje today's ko sidis in sayo abina in sha tunda na saba sha.
Ni dariya nayi ta masa ganin duk ya damu akan wai kawai ba zan sha ice cream gobe ba, in ba dan ba dan ba a da ina na san wani ice cream a rayuwa ta, dan gobe kad'ai ban sha ba me zai same ni, bai kyale ni.ba sai da nayi masa alkawarin zan je in sayo a today's d'in sannan ya hakura mukayi sallama ya tafi tare da bani hakurin inda zai tafi babu service dan haka ba zamu waya kaman yanda muka saba ba.
Haka ya wuce duk sai naji na damu domin sosai na saba kullum sai naji muryan shi nake iya bacci yanzu haka muryan sa shi ke tada ni a bacci.
A tsakar gida na tarar da Gwaggo Aisha da wata 'yar figaggiyar kaza guda d'aya ta saka a tire ta d'auko sharb'eb'iyar wuka sai faman kacan canawa take tana ta hura hanci,ni dariya ta bani ban ma kalli inda suke ba nayi shegewa ta d'akin mu anan na iske Baba yana zaune yana zaman jiran in shigo yaji karin bayani dan duk yanda yaso ji Inna kin bashi had'in kai tayi saboda ta san ba dan Allah yake neman sanin ba.
"'Yar albarka har kin shigo kenan"
"Eh Baba sannu da hutawa" na amsa ina ajiye kayan hannu na kusa da Inna amma kud'in yana hannu na cikin hijabina.
Ko kallon kayan Inna taki yi ta cigaba da d'inkin hulan ta hankali kwance, gefe na samu na zauna shima Baba zama ya gyara yana jiran Inna ta bud'e yaga menene a ciki amma ta basar, can daya gaji da zama ya ce," 'yar albarka me kika shigo mana dashi ne?"
"Kayan dad'i ne Baba na" na bashi da murmushi akan fuska ta ina kallon Inna ta gefen ido da take harara ta.
"A'a toh...toh... Wato Bintu yau kuma rashin kirkin ne ya tashi muna ji muna gani zaki hana mu kayan dad'i?" Cewar Baba cikin raha, Inna dai bata ce k'ala ba ta cigaba da d'inkin hulan ta.
"Mu kam bama zuciya kuma ba inda zamu je sai mun ci kayan dad'i ko 'yar albarka?"
Dariya nayi ina kallon Inna da tayi kicin-kicin da fuska dan ita al'amarin Baban mu sosai yake bata takaici da haushi, ya za'ayi ace wai kana ganin 'yar da ka haifa ta shigo da kaya masu yawa haka kuma kasan daga hannun saurayi ta samu, baka damu da binciken waye shi ko kuma ya akayi ya bata ko meye tsakanin su ba, saima jiki na b'ari kake son handame abinda ta kawo koma menene kai ba damuwar ka bane.
Cike da takaici halin sa da surutan sa daya ishe ta, ta bud'e d'ayan jakan da ta riga ta gane tambarin su kasancewar kullum ana kawowa, ba tare da ta lura da ko kaza nawa ne a ciki ba ta d'auko guda d'aya ta saka mishi a wata leda da babban roban juice d'aya duk ta had'a ta mik'a mishi .
Ba batun fushi ko zuciya yasa hannu yana washe baki ya amsa har zai fita na tsaida shi nima na jawo d'ayan jakan sanin cewa nawa shi saboda kullum aka kawo Inna bata tab'awa tarkacen kayan zaki na ne a ciki, roban ice cream babba dasu chocolate dasu snacks ne a ciki nima na cika mishi leda na mika masa harda dubu biyar na saka masa a kasan ledan bayan na faki idon Inna.
Ai Baba yanda kasan yayi hauka haka ya koma saboda murna dan akan idon shi na had'aa mishi kud'in yayin da Inna kuma hankalin ta yana kan hulan ta saboda dukkan mu haushi muke bata.
Fita yayi yana baza babban rigan shi, zai wuce Gwaggo Aisha ta tare shi da cinyar kaza a hannu cike da jin kai ta ce," Mallam tsaya ka saka albarka kaga 'yar ka Hajara Allah yayi ta samu saurayi mai mota, shine daga zuwa zance ya kawo mata gashasshiyar kaza na rabawa yara shine nace bari kai ma in kawo maka ka saka albarka".
"Amma Aisha kike kowa? Wallahi kin matukar raina ni, ni zaki tara ki tsamma wannan abu sai kace kin samu wani kwadayayye ko maye, toh tsaya kiji ni na fi karfin wannan abin naki mai kama da cinyar fara.
Dubi kiga inda ake cin arziki da kaza kuma aka san darajan miji ba watsatsu irin ku ba" yana magana yana nad'e hannun babban rigan sa nan manyan ledojin suka bayyana.
" Kinga wannan dakwaliyar kaza ce ta gidan gona da taji gashin inji ga lemon roba mai dad'in gaske, sannan kinga nan kuma kayan makulashe ne da sai in rantse da Allah ko wuka aka d'aura miki baki tab'a ganin irin su ba balle ki san sunan su, bayan nan kalli kasan kiga" yace yana nuna mata kud'in kasan ledan sannan ya mike tare da mai da komai cikin ledan ya cigaba da masifa," na dai gaya miki kada ki kara tare ni da maganan banza ko ranki yayi mugun b'aci ba abinda kika iya sai shegen surutu tsiya " nan ya shige d'akin shi ya bar Gwaggo Aisha da mataceccen jiki.
Tabbas sai sun sake shiri babba ma kuwa dan bata tab'a sanin haka Bintu tayi nisa ba,gaskiya dole ne ta nemi shawaran aminiyar ta dan samun mafita ko kuma suna ji suna gani wankin hula zai kai su dare.
Dariyan yaran gida ne ya dawo da ita hayyacin ta, sun had'a kai kusan su biyar suna mata dariyan yanda Baba ya bar ta da cinyar kaza a hannu, bata kula kowa a cikin su ba ta shige d'akin ta dan ji tayi gaba d'aya jikin ta ya mutu.
A d'aki kuwa Baba yana fita Inna har ta juyo da niyyan yi min fad'a dramar su da Gwaggo Aisha ya dakatar da ita, bayan sun gama ya wuce ya bar ta na ce," haba Inna ta, me yasa kike fushi haka yanzu fa kin zama 'yar lele a gidan Mallam".
Waje na fice da gudu da roban ice cream d'ina d'aya a hannu ina dariya ganin Inna ta shiga neman abinda zata buga min a kusa da ita bata samu ba.
Ciki na shiga b'angaren su Dije muka zauna sha muna hiran Yaya ina bata labarin yanda yau muka rabu da juna dan kawai zaiyi tafiyan kwana d'aya.
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ 🖊 *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Addu'ar Wanda Ya ji Tsoron Faruwar Wani Abu Mummuna saboda Kambun Baka*
Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya ce; "Idan dayanku ya ga wani abu da ya kayatar da shi ga dan uwansa, ko ga kansa, ko ga dukiyarsa, to ya roki Allah ya sanya albarka gare shi; domin kambun baka gaskiya ne.
*~INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?~*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*
_Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samun wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook_. 👇
https://www.facebook.com/101594048306878?referrer=whatsapp
_Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu._
*Kuyi hakuri kunji ni shiru kwana biyu kun san jiki da jini sai a hankali amma yanzu Alhmdllh naji sauki, wayan da suka kira da wayan da suka turo sakonni duk ina godiya da kulawar ku Allah ya bar kauna.
Nagode sosai*😘😘😘
*9*
"Lafiya lau yaro.... lafiya lau" Baba ya amsa yana had'iyar yawu yana kara karewa motan kallo, ni dai sanin zai kwafsa min yasa ko d'ago kaina na kasa yi bare mu had'a ido da shi.
Yayana kuwa yana gama gaishe shi bai d'ago daga tsugunen ba yayi kasa da kai yana jiran Baba ya bar wajan, Baba ba dan yaso ba yaja kafa zuwa cikin gida yaso ya samu wani abu wajan mai tsallen motan nan, amma ba komai bari yaje wajan Bintu zai ji ko wanene shi d'in.
Wata b'oyayyen ajiyan zuciya na sauke ganin ya wuce gida salin-alin ba tare da yayi wani abu daya tsinka ni ba, nabi bayan shi da kallo kaman yanda shima Yaya na yabi sa da kallo sai faman gyara mayattacen binjimar sa ta tshohuwar shaddar sa fara ce amma saboda tsufa har ta koma ruwan toka .
"Allah sarki Allah baiyi zamu had'u da Baba ba duk shekaru nan ba sai yau" naji Yaya na ya katse min tunanin da nake.
Murmushi nayi ina gyada kaina.
"Amma nima ban kyauta ba da ban tab'a tambayan shi ba all this while,wallahi yanzu dana gan shi sai naji ban kyauta ba sam" ya kara fad'a cikin damuwa sosai.
"Laa! Kada ka damu Allah ne baiyi zaku had'u ba tun farkon amma yanzu daya so ba gashi kun had'u ba" na bashi amsa ina murmushi.
Shiru kawai yayi dan shi a tunanin shi rashi da iyali ne yayiwa Baban yawa shiyasa ya zama haka bai san cewa duk wani yanayi da hali da mutum zai gan shi a ciki shi ya jefa kan sa ba.
Har muka gama hiran mu a ranan yana cigaba da nuna min rashin jin dad'in sa ni kuma ina nuna masa ba komai da zai tafi dubu ashirin ya bani wai in bawa Inna ta ajiye min in case wai ko goben ba zai samu dawowa ba, na nuna mishi muna da komai ba sai ya bani kud'i ba amma yaki karb'a saima shopping bags daya maida farilla wajan kawo min su ya lodo min kusan su 3 yana complain wai dole ya nemawa inna fridge ko dan saboda rana irin ta yau, kasancewar na saba kullum sai ya kawo min ice cream na sha toh gashi gobe baya nan da Inna tana da fridge sai ya sayo dayawa a saka min a ciki ko na kwana nawa ne.
Amma tunda ya bani 'yan canji a hannu in naga ba zan iya hakura ba sai inje today's ko sidis in sayo abina in sha tunda na saba sha.
Ni dariya nayi ta masa ganin duk ya damu akan wai kawai ba zan sha ice cream gobe ba, in ba dan ba dan ba a da ina na san wani ice cream a rayuwa ta, dan gobe kad'ai ban sha ba me zai same ni, bai kyale ni.ba sai da nayi masa alkawarin zan je in sayo a today's d'in sannan ya hakura mukayi sallama ya tafi tare da bani hakurin inda zai tafi babu service dan haka ba zamu waya kaman yanda muka saba ba.
Haka ya wuce duk sai naji na damu domin sosai na saba kullum sai naji muryan shi nake iya bacci yanzu haka muryan sa shi ke tada ni a bacci.
A tsakar gida na tarar da Gwaggo Aisha da wata 'yar figaggiyar kaza guda d'aya ta saka a tire ta d'auko sharb'eb'iyar wuka sai faman kacan canawa take tana ta hura hanci,ni dariya ta bani ban ma kalli inda suke ba nayi shegewa ta d'akin mu anan na iske Baba yana zaune yana zaman jiran in shigo yaji karin bayani dan duk yanda yaso ji Inna kin bashi had'in kai tayi saboda ta san ba dan Allah yake neman sanin ba.
"'Yar albarka har kin shigo kenan"
"Eh Baba sannu da hutawa" na amsa ina ajiye kayan hannu na kusa da Inna amma kud'in yana hannu na cikin hijabina.
Ko kallon kayan Inna taki yi ta cigaba da d'inkin hulan ta hankali kwance, gefe na samu na zauna shima Baba zama ya gyara yana jiran Inna ta bud'e yaga menene a ciki amma ta basar, can daya gaji da zama ya ce," 'yar albarka me kika shigo mana dashi ne?"
"Kayan dad'i ne Baba na" na bashi da murmushi akan fuska ta ina kallon Inna ta gefen ido da take harara ta.
"A'a toh...toh... Wato Bintu yau kuma rashin kirkin ne ya tashi muna ji muna gani zaki hana mu kayan dad'i?" Cewar Baba cikin raha, Inna dai bata ce k'ala ba ta cigaba da d'inkin hulan ta.
"Mu kam bama zuciya kuma ba inda zamu je sai mun ci kayan dad'i ko 'yar albarka?"
Dariya nayi ina kallon Inna da tayi kicin-kicin da fuska dan ita al'amarin Baban mu sosai yake bata takaici da haushi, ya za'ayi ace wai kana ganin 'yar da ka haifa ta shigo da kaya masu yawa haka kuma kasan daga hannun saurayi ta samu, baka damu da binciken waye shi ko kuma ya akayi ya bata ko meye tsakanin su ba, saima jiki na b'ari kake son handame abinda ta kawo koma menene kai ba damuwar ka bane.
Cike da takaici halin sa da surutan sa daya ishe ta, ta bud'e d'ayan jakan da ta riga ta gane tambarin su kasancewar kullum ana kawowa, ba tare da ta lura da ko kaza nawa ne a ciki ba ta d'auko guda d'aya ta saka mishi a wata leda da babban roban juice d'aya duk ta had'a ta mik'a mishi .
Ba batun fushi ko zuciya yasa hannu yana washe baki ya amsa har zai fita na tsaida shi nima na jawo d'ayan jakan sanin cewa nawa shi saboda kullum aka kawo Inna bata tab'awa tarkacen kayan zaki na ne a ciki, roban ice cream babba dasu chocolate dasu snacks ne a ciki nima na cika mishi leda na mika masa harda dubu biyar na saka masa a kasan ledan bayan na faki idon Inna.
Ai Baba yanda kasan yayi hauka haka ya koma saboda murna dan akan idon shi na had'aa mishi kud'in yayin da Inna kuma hankalin ta yana kan hulan ta saboda dukkan mu haushi muke bata.
Fita yayi yana baza babban rigan shi, zai wuce Gwaggo Aisha ta tare shi da cinyar kaza a hannu cike da jin kai ta ce," Mallam tsaya ka saka albarka kaga 'yar ka Hajara Allah yayi ta samu saurayi mai mota, shine daga zuwa zance ya kawo mata gashasshiyar kaza na rabawa yara shine nace bari kai ma in kawo maka ka saka albarka".
"Amma Aisha kike kowa? Wallahi kin matukar raina ni, ni zaki tara ki tsamma wannan abu sai kace kin samu wani kwadayayye ko maye, toh tsaya kiji ni na fi karfin wannan abin naki mai kama da cinyar fara.
Dubi kiga inda ake cin arziki da kaza kuma aka san darajan miji ba watsatsu irin ku ba" yana magana yana nad'e hannun babban rigan sa nan manyan ledojin suka bayyana.
" Kinga wannan dakwaliyar kaza ce ta gidan gona da taji gashin inji ga lemon roba mai dad'in gaske, sannan kinga nan kuma kayan makulashe ne da sai in rantse da Allah ko wuka aka d'aura miki baki tab'a ganin irin su ba balle ki san sunan su, bayan nan kalli kasan kiga" yace yana nuna mata kud'in kasan ledan sannan ya mike tare da mai da komai cikin ledan ya cigaba da masifa," na dai gaya miki kada ki kara tare ni da maganan banza ko ranki yayi mugun b'aci ba abinda kika iya sai shegen surutu tsiya " nan ya shige d'akin shi ya bar Gwaggo Aisha da mataceccen jiki.
Tabbas sai sun sake shiri babba ma kuwa dan bata tab'a sanin haka Bintu tayi nisa ba,gaskiya dole ne ta nemi shawaran aminiyar ta dan samun mafita ko kuma suna ji suna gani wankin hula zai kai su dare.
Dariyan yaran gida ne ya dawo da ita hayyacin ta, sun had'a kai kusan su biyar suna mata dariyan yanda Baba ya bar ta da cinyar kaza a hannu, bata kula kowa a cikin su ba ta shige d'akin ta dan ji tayi gaba d'aya jikin ta ya mutu.
A d'aki kuwa Baba yana fita Inna har ta juyo da niyyan yi min fad'a dramar su da Gwaggo Aisha ya dakatar da ita, bayan sun gama ya wuce ya bar ta na ce," haba Inna ta, me yasa kike fushi haka yanzu fa kin zama 'yar lele a gidan Mallam".
Waje na fice da gudu da roban ice cream d'ina d'aya a hannu ina dariya ganin Inna ta shiga neman abinda zata buga min a kusa da ita bata samu ba.
Ciki na shiga b'angaren su Dije muka zauna sha muna hiran Yaya ina bata labarin yanda yau muka rabu da juna dan kawai zaiyi tafiyan kwana d'aya.