← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 57 OF 71

Sashe 57

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin rashin jin dad'in kotobarar da tayi dan ita duk a zaton ta na sani shiyasa ta kira ta min jaje dan duk zuwanta gidan mu bata gani na ashe ban ma ji ba, maimakon ta bani amsa kawai sai ta katse kiran.

Cikin tashin hankali na kara Kiran ta amma sai naji wai switch off, jefer da wayan nayi ina kara fashewa da kuka na kama jeka ka dawo a tsakar parlour na rasa ina zan saka raina inji sanyi.

Kafadata naji ya riko ta baya tare da juyo dani muna fuskantan juna ya saka hannu ya share min hawayen da suke ambaliya a fuska na wasu na zubowa yace" shhhh ya isa haka kada ki sakawa kan ki ciwon kai, naji duk abinda aka fad'a miki a waya kada ki tashi hankalin ki kina da ni duk inda sojojin suka kai Baba nayi Miki alkawarin ni zan tsaya har sai naga ya fito".

Kallon shi kawai nake kaman yau na fara ganin shi murna zanyi akan abinda ya fad'a ko akasin ta, duk bayan maganganun da ya fad'a min jiya why zai cigaba da nuna min kulawa haka?

"Komai maza zasu iya yi dan cimma burin su " zuciya na ta kwab'e ni kamin in samu amsan bashi ya katse da " shhhhh kada kice komai kije ki d'auko hijabin ki mu tafi gidan ku muji ya maganan take"...

Ban San lokacin da murmushi ya subuce min na farincikin zanje gidan mu cikin matukar jin dad'i nace " thank you Ya Zafar....."

Nagode da soyayyar ku gare da wannan novel Allah ya bar kauna, nima ina muku fatan alkhairi my fans.
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*43&44*

Shiru motan ya d'auka babu mai magana a cikin mu sai dai yana tuki amma duk hankalin shi a kaina yake, ni kuma na maida kaina gefe ina kallon titi lokaci-lokaci na kan share hawaye da suke zubo min na kasa dannewa sai tunanin halin da Baban mu yake ciki nake, toh meya aikata haka da har sojoji suka tafi dashi...

Sojoji bama police ba, Baba da ko police ya gani duk sai ya gigice balle ace yana barracks na sojoji ya Allah ya fitar da shi cikin sauki, duk a zuciyata nake ta wasi-wasin nan har muka iso kofar gidan mu cikin azama na fara kokarin bud'e kofan in fita naji ashe ya saka lock.

Juyowa nayi na watsa mishi wani kallo da yake nufin menene haka? Bai nuna fushi ko b'acin rai ba yace " calm down pls ki bi komai a sannu insha Allah ba abinda zai samu Baban mu I promised u this, in kin shiga ciki pls ki min iso wajan kanin Baban inji ta ina zan fara" yana karasa maganan shi yayi unlocking d'in kofan jiki a mace na bud'e na fita.

Ina fitowa Kuma sai naji kaman in d'iba da gudu in shiga ciki nake ji amma na daure banyi gudun ma sai uban sauri da nayi ta zubawa na tura gate din na shiga daga can na hango Inna ta da Inna Asabe suna ta kiciniya da murhun itace a tsakar gida zasu daura abincin sadaka, ai ban san lokacin da na kwasa da gudu na isa gare su sai kawai Inna ji tayi an fad'o mata akai .

A zabure ta juyo muka had'a ido sai washe baki nake dan farincikin da nake ciki bai zai tab'a misaltuwa ba, itama cikin farincikin ta rungume ni fuskarta d'auke da zallan murnan gani na cikin koshin lafiya ga wani dan haske da na kara kana gani kasan ina cikin hutu.

"Zareefa kece haka sulum bako waya?" Inna Asabe tace tana kallon mu cikin farinciki itama, sai a sannan na fashe da kuka sosai jin ta ambaci sunan waya nace " yanzu Baban mu yana cikin wannan halin shine babu wanda ya kira ni dan a gaya min?"

"Baban ku karami shi ya hana a gaya miki sanin cewa ba zaki tab'a kwantar da hankalin ki ba dole kice zaki fito shi kuma baya son fitowan naki saboda ko cikakken wata 3 baki yi a d'akin ki ba" Inna Asabe ce ta bani amsa a daidai wannan lokaci kuma Baban mu karami da Zafar suka shigo tare da sallama.

Amsawa su Inna sukayi suna gyara lullub'in jikin su ya durkusa har kasa ya fara gaishe su kai a k'asa, amsawa sukayi suma kawunan nasu a kasa sun kasa kallon shi a zuciya ta na fara gulman shi ina dube shi yanda yake ta tsunne kai kaman da gaske.

Suna gama gaisawa Baban mu karami yaja shi zuwa b'angaren Baban mu da yake a rufe ya bud'e suka shige ciki, bayan wucewar su Inna ta ture ni daga jikin ta tana " ke Kam ban san ranan da zakiyi hankali ba ya zaku taho tare da mutum ki shigo ki bar shi a waje ba tare kinyi mishi iso ba?"

Baki na turo mata na shagwab'a zanyi magana ta nuna min hanyan ciki tare da had'e fuska, banyi gardama ba na juya zan shiga kenan naji muryan Hajara cikin ihu ta ambaci suna na nima na juyo cikin murna ina amsa mata da d'an karfi ta taho cikin sauri muka rungume juna sannan muka shige ciki su Inna kuma suka cigaba da aikin su.

A can b'angaren Baban mu kuma koda suka shiga Zafar zubewa ya karayi a k'asa ya fara gaida shi cikin sauri Baban mu karami ya dakatar dashi yana haba ya zauna akan kujera mana ai sun riga sun gaisa a waje.

Tashi yayi ya zauna amma bai hau kan kujeran ba ya sunkuyar da kai yana sauraron Baban Dije daya fara koro mishi bayanin yanda al'amarin ya faru da irin wahalhalun da suka sha amma ko takamaimai inda yake basu sani ba balle akai ga maganan fito dashi.

"Tun farko da na samu labari da ba zai kai har war haka a hannun su ba kasan wani lokacin mutane suna yiwa mutum cune su Kuma ba zasu bi diddigi ba su kama mutum su jefa cikin barracks d'in su shikenan in mutum bashida gata sai a nemi labarin shima a rasa but insha Allah akwai abokina da mukayi karatu tare a abroad Baban shi Marshal ne zanyi mishi magana in Allah ya yarda komai zai zo karshe" .

Cike da farinciki Baban mu karami ya fara mishi godiya amma ya dakatar dashi yana " haba nima ai Baba nane dan bana son Abba na yaji labarin ne saboda wasu dalilai amma da waya kawai zaiyi ba tare da mutum yaje ba zasu sako shi".

Nan ma Baban Dije gyad'a mishi Kai yake cike da gamsuwa da bayanin nashi domin karshen ta in Abban Zafar d'in yaji wannan labarin babu dad'i ko dan kare mutuncin sa hakan yana da kyau, sai yaji Zafar d'in ya kara birge shi .

Sun dan kara tattaunawa sannan yace zai tafi wajan friend din nashi duk yanda sukayi zai zo musu da labari kamin nan nima zai barni anan sai in ya dawo sai mu koma tare, har bakin gate ya rako shi sannan suka rabu.

Ni kuma muna parlour Inna da ya sha gyara sai kamshin turaren wutan sandal yake nake ce ma Hajara " ni dai nayi fushi tunda irin wannan abu ya faru ace harda ke wajan masu boye min, ba dan Dije ta Kira ni tayi min jaje ba Ina can ban san me yake faruwa ba aiko ba abinda zan iya yi zan taya shi da addu'a".

" Ke ni tunda abun ya faru da washe gari naso a fad'a miki ko dan mijin ki kila zai iya yin wani abu amma Baban Dije ya hana kuma yayi gargadi kan kada a kuskura a gaya miki wai yaushe aka miki aure " Hajara ta tari numfashi na.

Haka muka yini muna ta hiran mu da Hajara a parlour Inna har kusan Azhar sannan Maa da yan uwan Baba da suke gidan ta suka shigo nan suma suka hau murnan zuwa na daga baya kuma muka jajantawa juna aka zauna ana maida abinda ya faru har wannan lokaci Gwaggo Aisha tana ciki bata leko ba duk da hayaniyan mutane da ya cika gidan dan harda makota duk sun shisshigo.

Kasa hakuri nayi na sassauta murya na tambayi Hajara ko ina take? Ita kuwa cewa tayi ta fita anguwa tunda sassafe ta boye min, ni kuwa abin ya bani mamaki ace ana cikin wannabe halin har ta iya zuwa anguwa.

Zafar tun a mota ya kira abokin shi mai suna Hamis kan yana Ina?
Chapter 57 · 0% Book details