Sashe 13
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Hmmmm gaskiya ke kam Zareefa Allah ya baki, ki ga yanda yake mutuwan son ki kuma yake nuna kulawa yake tarairayan ki, a gidan ku ma ya kula dake haka ina ga ya aure ki ya killa ce ki a gidan sa abin ba magana". Cewar Dije kenan.
"Allah gaskiya soyayya akwai dad'i Dije, kin san yanda nake jin sa a cikin raina kuwa? Allah ya nuna min ranan auren mu" duka Dije ta kai min a gadon baya na tana dariya tace.
"Shegiya Zareefa har nawa kike da zaki zauna kina maganan aure?" Murkud'a mata baki nayi ina ," eh d'in kema ai shirin yi miki ake nan da shekara d'aya idan munyi sauk'a, toh nima ina gama secondary shekaru biyu da rabi suka rage za'ayi mana ni da Yaya naaa" na karasa ina rungume hannye na biyu a kirji na tare da rufe ido nayi baya kaman zan fad'i Dije ta taro ni tana tafa hannu ta ce," ke yarinyan nan haka kika zama baki tafasa ba zaki kone mana mu shiga uku?"
"Wai da kike fad'an haka shekaru nawa kika bani da kike ta cika baki tun d'azu , ina biyu ne kawai harda wani ........ zaki kone mu shiga uku" na fad'a cikin kwaikwayon muryan ta, ta kai min duka na goje haka muka cigaba da shan ice cream muna hiran mu cikin raha..
Dije itace babban 'ya a wajan Maman Dije ta bani kusan shekaru biyu amma hakan bai hana mu zama kawaye ba domin yaran gidan dukan su iyayen su sun hana su wasa dani tun muna yara dan haka babu wani shakuwa ta 'yan uwan taka tsakanin na dasu sai dai kallon kallo.
Ba Yaya na kad'ai ba nima na shiga damuwa sosai na rashin sa a kusa da ni, cikin kwana biyu da yayi baya nan duk sai na zama kaman ba ni ba abinda yafi tayar mun da hankali rashin samun sa a waya, duk da ya gaya min inda zai tafi ba service amma hakan bai hana ni kwana da waya a hannu ina gwadawa ba, Inna tana ankare dani amma bata ce min cikan ki akai ba.
A ranan da ya cika na uku ne kiran shi ya shigo min yana fara ringing na d'aga cikin d'auki na ce," wayyoo Yaya naaa"
"Na'am k'anwa taaaa" shima yaja kaman yanda nake jan nashi.
Dariya muka sanya dukkan mu sai da mukayi mai isar mu kaman sabobbin kamu sannan ya ce," na kusan shigowa gari k'anwa ta, insha Allah gobe war haka muna tare"
Tsalle na daka da wayan a kunne na na ce," yessss Alhamdullilahi Allah ya shigo da ku lafiya Yaya na" da Ameen ya amsa sannan ya katse kiran.
Dije da take gefe tana min dariya tare da min signal ga Maman su a kusa inyi a hankali ko kula ta banyi ba, ita kuma Maman Dije murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta shige kitchen d'in ta ta kyale mu tana mamakin wai yarinya kamata da iya soyayya, hmmm duniya kenan in da ran ka zaka sha kallo.
Zama nayi tare da rafka tagumi ina tunanin ya kamata nima ko sau d'aya ne in kyautata mishi yanda yake kyautata min kullum ko ba komai shima zai ji na damu da shi.
"Ke kuma lafiya, ba yanzu naga kina murnan masoyi zai dawo ba kuma inga kin zabga tagumi kina tunani kaman wacce akaiwa mutuwa?" Cewar Dije kenan.
"Dije kawai so nake inyi wani abu da zai faranta ran Yaya na tunda bai tab'a tafiya ba shiyasa nake son inyi wani abu na tarban shi".
"Gaskiya kinyi tunani mai kyau Zareefa in dai akwai kud'i a hannun ki ni zan taya ki ko abinci ne kiyi mishi".
Cikin jin dad'i na amsa mata da akwai kud'i a waje na, nan da nan muka tsara yanda zamuyi da abinda zamu girka masa.
Da washe gari tare muka je kasuwa muka sayo doya da nama sai kwai creast d'aya da mai muka dawo, gidan Maa muka kai kayan da muka sayo da taimakon Dije mukayi mishi yam balls da kwai cikin kwai da yake shine sana'an da suke ta kware sosai, Maa kuma tayi mana dambun nama mai dad'in gaske.
'Yan kulolli da Inna ta fara min tarun su nan gidan Maa na fito da set d'aya muka zuzzuba a ciki muka shirya a cikin tiren plastic mai kyau shima cikin kayan tarun muka d'auko.
"Kinga yanda kayan nan sukayi kyau kuwa kuma sunyi dad'i da zamu had'a da kunun aya mai sanyi zai fi tafiya" Dije ta kawo sabon shawara nima ba b'ata lokaci na amince sanin yanda shima Dije ta kware da yin sa shima suna sayarwa amma a lokacin zafi.
Da yake mu biyu ne bamu b'ata lokaci ba shima muka had'a ta muka zuba jug na glass haddade muka saka kankara, ni sai a ranan ma nasan na san cewa Inna tayi min taru dayawa haka, sai da muka gama tsab sannan muka wuce gida dan inyi wanka in shirya ita kuma Dije zata fita sana'a ta.
Sai da na shigo Inna ta rutsa ni da tambayoyi ina naje tun dazu?
Na amsa mata da ina gidan Maa tace karya nake bata yarda ba ta kira yaro ina gani ta tura gidan Maa dan a tambayo mata ni dai na shige wanka dan ina gudun kada Yaya na ya dawo ban shirya ba.
Ko da na fito daga wankan bata kuma kula ni ba da alama an tambayo mata Maa,sai da nayi sallah naci ado na da riga da skirt na lace pure cotton dark blue ya sha adon flowers pink, sosai kayan suka min kyau domin Yaya na ya iya zab'en kayan da zasu yi min kyau.
Inna duk tana kallon sabon falli da nake bata min magana ba sai da na gama sannan ta zaunar da ni ta fara min nasiha kan rike mutunci na na 'ya mace a duk inda nake, duk da ta amince da Abdulbasit amma tace kada in kuskura in bar shi ya rike min ko da hannu nane tunda shi ba muharrami na bane kuma ba aure na yayi ba, in ko na bari hakan ta kasance toh tabbas ciki ne zai bayyana a tare da ni wanda har jikokina zan barwa wannan bakin fenti.
Sosai Inna tayi min nasiha daya kashe min jiki ba shiri na fad'a mata duk abinda mukayi a gidan Maa, nan tace ai ba wani abu bane kyautatawa wanda yake kyautata maka,kar inji komai in dan wannan ne ko yaushe na tashi yi inyi anan gida bai sai naje gidan Maa ba.
Cikin jin dad'in fahimta da tayi muka zauna muna hira cikin dabara ta cigaba da wayar min kai akan zaman duniya da kalubalen da yawanci 'yan mata ke fuskan ta wajan kwad'ayi da bin maza kuma daki-daki suke shiga kaina, kiran wayan Yaya na ne ya katse mana hiran na saka hijabi na fito.
Center kofan gidan mu yake kallo fuskar shi d'auke da murmushi na musamman, yana gani na ya kara fad'ad'a murmushi nasa cikin sabon takun da na koya saboda shi na karaso gaban shi sai dai ina zuwa na b'ata fuska ta.
Cikin d'an damuwa yake tambaya ta me ya faru kuma nake b'ata fuska?
"Ba kai bane yau baka kallon waya na fito balle in tsorata ka yanda na saba" na bashi amsa a shagwab'e.
Dariya yayi yana shafa gashin kansa da hannun sa ya ce," ayi min afuwa k'anwa ta yau d'in ne nayi missing d'inki dayawa shiyasa na kasa hakuri har ki ban tsoro"
"Nima nayi missing d'inka sosai Yaya naaa"
"Ina son ki k'anwa ta"
Rufe fuska ta nayi ina dariya kasa-kasa sannan na bashi amsa da ," nima ina son ka Yaya naaa".
A take na bud'e fuska ta tunawa da nayi da abincin da na had'aa mishi a gidan Maa.
"Dan Allah bani minti biyu ina zuwa" ban jira amsar shi ba nayi gaba na kira Bakura wani yaron makotan mu muka tafi tare na d'aura mishi tiren akai ni kuma na d'auko jug d'in muka dawo wajan shi.
Tunda muka fito yake kallo na da mamaki har muka iso bai iya d'auke idan shi daga kaina ba,
"Ban san a ina zan ajiye maka ka ci ba,ko zaure zan saka maka tabarma?"
Girgiza kai yayi tare da nuna min motan shi, ban musa ba yayi gaba muka bi bayan shi ya bud'e seat na bayan motan ya karb'i tiren akan yaron ya saka a ciki sannan ya min nuni da in shiga ciki nima.
Sororo nayi da jug a hannu na kasa shiga kasancewar ban tab'a shiga motan shi ba kuma ga nasiha da Inna ta min d'azu, sai da ya shiga ya zauna ya ganni nan tsaye banida niyyan shiga.
Kara cewa in shiga yayi nayi shiru ni ban shiga ba kuma ban tafi ba sai raba ido nake nan ya fahimci cewa tsoro nake,sai da ya nuna min cewa tunda ban yarda da shi duk shekaru da muka d'auka tare in d'auke abinci na baya ci.
Ganin kaman ran shi ya b'aci yasa na d'an dosana duwawu na kad'an na zauna, yana murmushi yace toh in bud'e yaga me na dafa mishi mai dad'i.
Ina bubude mishi ya ce," iyye lalle k'anwa ta an girma,ke kika girka min ko Inna ce?"
*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/23, 4:26 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾
"Allah gaskiya soyayya akwai dad'i Dije, kin san yanda nake jin sa a cikin raina kuwa? Allah ya nuna min ranan auren mu" duka Dije ta kai min a gadon baya na tana dariya tace.
"Shegiya Zareefa har nawa kike da zaki zauna kina maganan aure?" Murkud'a mata baki nayi ina ," eh d'in kema ai shirin yi miki ake nan da shekara d'aya idan munyi sauk'a, toh nima ina gama secondary shekaru biyu da rabi suka rage za'ayi mana ni da Yaya naaa" na karasa ina rungume hannye na biyu a kirji na tare da rufe ido nayi baya kaman zan fad'i Dije ta taro ni tana tafa hannu ta ce," ke yarinyan nan haka kika zama baki tafasa ba zaki kone mana mu shiga uku?"
"Wai da kike fad'an haka shekaru nawa kika bani da kike ta cika baki tun d'azu , ina biyu ne kawai harda wani ........ zaki kone mu shiga uku" na fad'a cikin kwaikwayon muryan ta, ta kai min duka na goje haka muka cigaba da shan ice cream muna hiran mu cikin raha..
Dije itace babban 'ya a wajan Maman Dije ta bani kusan shekaru biyu amma hakan bai hana mu zama kawaye ba domin yaran gidan dukan su iyayen su sun hana su wasa dani tun muna yara dan haka babu wani shakuwa ta 'yan uwan taka tsakanin na dasu sai dai kallon kallo.
Ba Yaya na kad'ai ba nima na shiga damuwa sosai na rashin sa a kusa da ni, cikin kwana biyu da yayi baya nan duk sai na zama kaman ba ni ba abinda yafi tayar mun da hankali rashin samun sa a waya, duk da ya gaya min inda zai tafi ba service amma hakan bai hana ni kwana da waya a hannu ina gwadawa ba, Inna tana ankare dani amma bata ce min cikan ki akai ba.
A ranan da ya cika na uku ne kiran shi ya shigo min yana fara ringing na d'aga cikin d'auki na ce," wayyoo Yaya naaa"
"Na'am k'anwa taaaa" shima yaja kaman yanda nake jan nashi.
Dariya muka sanya dukkan mu sai da mukayi mai isar mu kaman sabobbin kamu sannan ya ce," na kusan shigowa gari k'anwa ta, insha Allah gobe war haka muna tare"
Tsalle na daka da wayan a kunne na na ce," yessss Alhamdullilahi Allah ya shigo da ku lafiya Yaya na" da Ameen ya amsa sannan ya katse kiran.
Dije da take gefe tana min dariya tare da min signal ga Maman su a kusa inyi a hankali ko kula ta banyi ba, ita kuma Maman Dije murmushi kawai tayi tana girgiza kai ta shige kitchen d'in ta ta kyale mu tana mamakin wai yarinya kamata da iya soyayya, hmmm duniya kenan in da ran ka zaka sha kallo.
Zama nayi tare da rafka tagumi ina tunanin ya kamata nima ko sau d'aya ne in kyautata mishi yanda yake kyautata min kullum ko ba komai shima zai ji na damu da shi.
"Ke kuma lafiya, ba yanzu naga kina murnan masoyi zai dawo ba kuma inga kin zabga tagumi kina tunani kaman wacce akaiwa mutuwa?" Cewar Dije kenan.
"Dije kawai so nake inyi wani abu da zai faranta ran Yaya na tunda bai tab'a tafiya ba shiyasa nake son inyi wani abu na tarban shi".
"Gaskiya kinyi tunani mai kyau Zareefa in dai akwai kud'i a hannun ki ni zan taya ki ko abinci ne kiyi mishi".
Cikin jin dad'i na amsa mata da akwai kud'i a waje na, nan da nan muka tsara yanda zamuyi da abinda zamu girka masa.
Da washe gari tare muka je kasuwa muka sayo doya da nama sai kwai creast d'aya da mai muka dawo, gidan Maa muka kai kayan da muka sayo da taimakon Dije mukayi mishi yam balls da kwai cikin kwai da yake shine sana'an da suke ta kware sosai, Maa kuma tayi mana dambun nama mai dad'in gaske.
'Yan kulolli da Inna ta fara min tarun su nan gidan Maa na fito da set d'aya muka zuzzuba a ciki muka shirya a cikin tiren plastic mai kyau shima cikin kayan tarun muka d'auko.
"Kinga yanda kayan nan sukayi kyau kuwa kuma sunyi dad'i da zamu had'a da kunun aya mai sanyi zai fi tafiya" Dije ta kawo sabon shawara nima ba b'ata lokaci na amince sanin yanda shima Dije ta kware da yin sa shima suna sayarwa amma a lokacin zafi.
Da yake mu biyu ne bamu b'ata lokaci ba shima muka had'a ta muka zuba jug na glass haddade muka saka kankara, ni sai a ranan ma nasan na san cewa Inna tayi min taru dayawa haka, sai da muka gama tsab sannan muka wuce gida dan inyi wanka in shirya ita kuma Dije zata fita sana'a ta.
Sai da na shigo Inna ta rutsa ni da tambayoyi ina naje tun dazu?
Na amsa mata da ina gidan Maa tace karya nake bata yarda ba ta kira yaro ina gani ta tura gidan Maa dan a tambayo mata ni dai na shige wanka dan ina gudun kada Yaya na ya dawo ban shirya ba.
Ko da na fito daga wankan bata kuma kula ni ba da alama an tambayo mata Maa,sai da nayi sallah naci ado na da riga da skirt na lace pure cotton dark blue ya sha adon flowers pink, sosai kayan suka min kyau domin Yaya na ya iya zab'en kayan da zasu yi min kyau.
Inna duk tana kallon sabon falli da nake bata min magana ba sai da na gama sannan ta zaunar da ni ta fara min nasiha kan rike mutunci na na 'ya mace a duk inda nake, duk da ta amince da Abdulbasit amma tace kada in kuskura in bar shi ya rike min ko da hannu nane tunda shi ba muharrami na bane kuma ba aure na yayi ba, in ko na bari hakan ta kasance toh tabbas ciki ne zai bayyana a tare da ni wanda har jikokina zan barwa wannan bakin fenti.
Sosai Inna tayi min nasiha daya kashe min jiki ba shiri na fad'a mata duk abinda mukayi a gidan Maa, nan tace ai ba wani abu bane kyautatawa wanda yake kyautata maka,kar inji komai in dan wannan ne ko yaushe na tashi yi inyi anan gida bai sai naje gidan Maa ba.
Cikin jin dad'in fahimta da tayi muka zauna muna hira cikin dabara ta cigaba da wayar min kai akan zaman duniya da kalubalen da yawanci 'yan mata ke fuskan ta wajan kwad'ayi da bin maza kuma daki-daki suke shiga kaina, kiran wayan Yaya na ne ya katse mana hiran na saka hijabi na fito.
Center kofan gidan mu yake kallo fuskar shi d'auke da murmushi na musamman, yana gani na ya kara fad'ad'a murmushi nasa cikin sabon takun da na koya saboda shi na karaso gaban shi sai dai ina zuwa na b'ata fuska ta.
Cikin d'an damuwa yake tambaya ta me ya faru kuma nake b'ata fuska?
"Ba kai bane yau baka kallon waya na fito balle in tsorata ka yanda na saba" na bashi amsa a shagwab'e.
Dariya yayi yana shafa gashin kansa da hannun sa ya ce," ayi min afuwa k'anwa ta yau d'in ne nayi missing d'inki dayawa shiyasa na kasa hakuri har ki ban tsoro"
"Nima nayi missing d'inka sosai Yaya naaa"
"Ina son ki k'anwa ta"
Rufe fuska ta nayi ina dariya kasa-kasa sannan na bashi amsa da ," nima ina son ka Yaya naaa".
A take na bud'e fuska ta tunawa da nayi da abincin da na had'aa mishi a gidan Maa.
"Dan Allah bani minti biyu ina zuwa" ban jira amsar shi ba nayi gaba na kira Bakura wani yaron makotan mu muka tafi tare na d'aura mishi tiren akai ni kuma na d'auko jug d'in muka dawo wajan shi.
Tunda muka fito yake kallo na da mamaki har muka iso bai iya d'auke idan shi daga kaina ba,
"Ban san a ina zan ajiye maka ka ci ba,ko zaure zan saka maka tabarma?"
Girgiza kai yayi tare da nuna min motan shi, ban musa ba yayi gaba muka bi bayan shi ya bud'e seat na bayan motan ya karb'i tiren akan yaron ya saka a ciki sannan ya min nuni da in shiga ciki nima.
Sororo nayi da jug a hannu na kasa shiga kasancewar ban tab'a shiga motan shi ba kuma ga nasiha da Inna ta min d'azu, sai da ya shiga ya zauna ya ganni nan tsaye banida niyyan shiga.
Kara cewa in shiga yayi nayi shiru ni ban shiga ba kuma ban tafi ba sai raba ido nake nan ya fahimci cewa tsoro nake,sai da ya nuna min cewa tunda ban yarda da shi duk shekaru da muka d'auka tare in d'auke abinci na baya ci.
Ganin kaman ran shi ya b'aci yasa na d'an dosana duwawu na kad'an na zauna, yana murmushi yace toh in bud'e yaga me na dafa mishi mai dad'i.
Ina bubude mishi ya ce," iyye lalle k'anwa ta an girma,ke kika girka min ko Inna ce?"
*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/23, 4:26 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾