Sashe 50
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*45&46*
A guje Ibrahim ya shigo gida har yana fad'uwa kasa Inna da take tsakar gida ta nufo shi tare da d'aga shi tana karkad'e mishi jiki tace " toh d'an tsokana wa ka tsokano ya biyo ka, ka shigo a guje haka?"
Yana haki irin na alamun ya sha gudu yace yana nuna mata kofan waje " Baba ne..... Baba ne sojoji suka tafi dashi".
"Wani Baban kuma Ibrahim"?" Ta tambaya cikin rashin fahimta.
"Baban mu, Baban mu na gidan nan" ya amsa mata tare da fara kuka.
Salati Inna ta fara tana tafa hannu cikin tashin hankali murya na rawa ta d'aga murya tana " kuna ina matan gidan ku fito dan Allah kuji abinda yaron nan yake fad'a"
Inna Asabe ce ta fito da gudu har tana tuntube bakin ta d'auke da salati itama nan suka kacame dasu da sauran yaran suna ta cacekuce dan sun rasa ta ina zasu fara kasancewar kowa ya san harkan sojoji wuyan sha'ani ne dashi a nan maiduguri.
Duk hayaniyar nan daya cika gidan mu har makota sun shigo 'yan jin gulma da da masoyan gaske ana ta jajantawa amma gwaggo Aisha bata leko ba balle asan tana gidan ko bata nan a wannan yanayin Baban Dije ya shigo shima hankali tashe amma ganin su Inna a wannan yanayin yasa yayi kokarin boye nashi tashin hankalin ya shiga kwantar musu da hankali kan cewa kada su tada hankalin su su bi komai a sannu insha Allah Baba zai dawo gida tunda ko makiyin sa zai bada shaida akan sa baya aikata wani mummunan abu shi dai bar shi da son kud'i.
Da wannan bayanan ya samu suka d'an natsu kowacce ta koma daki makota kuma suka koma gudajen su da addu'an Allah ya sauwaka.
Hankali tashe Hajara tayi sallama ta shiga cikin gida dan saukowan ta kenan daga napep 'yan suka tare ta da mummunan labarin nan, ganin babu kowa a tsakar gidan yasa ta nufi d'akin su tana kwad'awa Gwaggo Aisha kira kaman zata tsaga gidan amma bata ji muryan ta amsa mata ba, a zaton ta bata gidan ta fita ko sun fita da sauran matan gidan.
Turus tayi fuskarta cike da al'ajabi ganin mahaifiyar nata kishingid'e tana cin gyad'a mai gishiri hankali kwance, d'ago kai tayi ta kalle ta sannan tace meya faru kike ta kwala min kira kaman zaki tsaga gidan nan ko dai yauma kin zo min da labari me dad'i ne?"
Had'iye mamakinta tayi tace umma ni ba dan wannan nake kiran ki ba yanzu ina saukowa a napep naji ana ta kananan maganganu a anguwa wai sojoji har mota 2 sun zo sun tafi da Baban mu?"
Tab'e baki tayi tare da watsa gyad'an hannun ta a baki ta fara taunawa tana hararan ta tace" toh sai akayi me ko ni na aike shi yin mummunan aikin da zasu kama shin, kema kin san Baban ku da shegen son kud'i kinga kuwa wani ta'asan yaje yayi musu, tsuntsun da yaja ruwa shi ruwan zai doka".
Tunda ta fara magana Hajara take kallon ta cike da takaicin abinda take fad'a wai Baban mu ne mayen kud'i, toh ita fa in banda ance laifi tudu ne yanzu bata ganin laifin munanan ayyuka da take sai na Baban mu wanda ta tabbata da wata akasa dan bai aikata abinda mutane suke cewa ba.
"Ke ina tambayan ki kin min shiru, nace dai yauma aikin ya tafi yanda ya kamata ko?" Ta katse ta cikin tsawa.
Gyad'a mata kai kwai tayi dan wani malolon bakinciki ne yazo ya tokare mata wuya, washe hakora tayi cike da farin ciki tana ," Alhamdulillah hankali na ya kwanta amma ya ban ganki da kaya irin na jiya ba, saboda na saka rai zaki kawo mana kayan dad'i ko girki ban daura ba na zauna jiran ki".
Daki kawai ta nufa ta san in ta tsaya takaici ne zai kashe ta, saida ta kusan shiga daki sannan tace mata " mahaifiyar shi ta kira shi ya tafi"
"Uwar shi? Dan uwar shi ta kira sai ya tafi ya bar ki, lalle muna da sauran aiki a gaban mu dole ne mu raba shi da ita in ba haka ba zata kawo mana barazana cikin aikin mu".ta fad'a a masifance ita dai Hajara bata kara kula ta ba ta ida shigewa ta bar ta da kumfan baki.
***************************
Tunda Hajara ta tafi ban kara jin motsin sa ba ina ciki duk haushi ya ishe ni sai kunci nake ni kad'ai, koda naga zaman kuncin ba zai fishe ni ba fitowa nayi na kama dan aikace-aikace na ko zan ragewa kaina damuwa, cikin ikon Allah ko Ina farawa na mance da abinda ya faru.
Kitchen na shiga na had'a kayan da b'ata ina wankewa naji a jiki na alamun ana kallo na da sauri na waiwaya na gan shi tsaye yana karewa baya na kallo, yana ganin na juyo ya basar yayi kaman yanzu ne zuwan shi, karasa shigowa yayi cikin kitchen din ya bud'e fridge ya d'auko malt mai sanyi ya koma bakin kitchen din ya bud'e ya fara sha.
Ban kara juyowa ba amma ji nake kaman na juya nayi ta kallon shi dan ba karamin kyau yayi min ba, kama gulman shi nayi a cikin zuciya ta ina mutum kaman wani aljani ko wani Kaya ya saka sai yayi mishi kyau dubi dai singlet ne da 3 quater a jikin shi amma sai ya zama kaman wani dressing yayi na gani na fad'a ga kamshin sa kuwa duk inda zai je kamin ya isa kamshin ya riga shi isowa haka kuma ko ya tafi zai dad'e a wajan.
Ta kasan ido na kara kallon shi yana tsaye a inda yake bai motsa ba gashi ni kuma na gama wanke-wanken ina son fita amma na rasa yanda zanyi saboda duk ya tare hanya yayi bake-bake babu wajan wucewa ni kuwa bana son yi mishi magana dan har yanzu haushin shi nake ji.
Wasu ayyukan na shiga kirkira wai ko zai gaji ya bar hanyan amma saima gani nayi ya gyra tsayuwar shi ya jingina da kitchen cabinet din ya cigaba da kurb'an malt din yana kara tsare ni da ido, gajiya nayi da kirkire kirkiren nayi shahada na nufo kofan wai ko in yaga nayi niyyan fitan zai bani hanya amma ga mamakina ko motsawa baiyi ba balle ya matsa.
"Zan wuce" nace ba tare da na kalle shi ba.
"waya hana ki wucewa?" Yace shima yana wani d'aure fuska " naga ka tare hanya ne"...
Dan matsawa yayi gefe ya bar wani karamin hanya,ta gefen ido na kalle shi naga har yanzu yana rike da malt din a rai na ina mamakin wani irin kurb'a ce yake mata tun dazu ace bai kare ba, sauke ido na nayi cikin sauri nazo zan wuce amma sai yasa hannun shi na dama ya tare hanya.
Dawowa nayi da baya zan koma kitchen d'in nan ma ya jefar da empty tin na malt din ya kara tare min hanya ya zamto ina tsakiya hannayen shi ya zuba min wayan idon shi mai rikitar dani, cikin azama nayi kasa da nawa idon dan ba zan iya jure kallon nashi ba.
"Da kike wani neman guduwa cinye ki zanyi?" Ya tambaya cikin wani irin murya da ban san yana da ita ba, ban iya bashi amsa ba na kara yin kasa da kaina, ina jin yanda zuciya ta take zillo kaman zata fito saboda kusancin namu yayi yawa.
"Hmmm na gane duka gulma ne u just want me to repeat what we did in d morning" yace yana bina da wani irin killer smile.
Cikin zaro ido na d'ago kai na da niyyan yi mishi masifan sharri daya lak'a min amma mukut na had'iye kaya na saima zaro ido da nashiga yi sakamon tattausan bakin shi da naji akan nawa.
Kiciniyar kwace kaina nake amma bai bani daman hakan ba, sai kara manne min yake tun inada karfin kokuwa har karfi na ya kare wani irin kasala na sauko min tare da hawaye kaman an bud'e famfo.
Jin hannuwan shi sun fara min yawo a jiki yasa na tattara sauran courage daya rage min na ture shi ya kuwa tafi da baya har yana bigewa da cabinet din bayan shi ni dai ban juyo ba balle in san halin da yake ciki na fad'a daki tare da rufo kofa na jingina ina maida numfashi.
"Ouch " yace yana rike bayan shi inda ya bugun ya shafawa yana murmushi tare da jin kaman ya bini ,shi dai wannan sabon jaraba daya same shi a kaina bai tab'a shiga irin wannan yanayin ba dan ko lokacin da yake karatu a kasar waje ga dai mata birjik suna yawo half nacked wasu har tallahn kan su suke kawo mishi amma koda wasa bai tab'a jin kwatancin abinda yake ji game dani ba akan su.
"Why! Why her?" Ya furta can kasan makoshi ganin babu mai bashi amsa yasa ya koma cikin parlour ya zauna ya dafe kai yana neman mafita.
Na dad'e jingine da jikin kofan ido na rufe ina wani irin murmushi da yake fitowa daga karkashin zuciya ta, me ya faru tsakanin mu yanzu? Na tambayi kaina.
"He just kissed me" nacewa kaina ina rufe fuskata da tafin hannaye na duka biyu ina kara fad'ad'a murmushin da nake saboda ina ayyanawa a raina cewa yana sona, yes yana sona in ba haka babu abinda zai saka yayi kissing na.
"BA SONKI NAKE BA, ZAN AURE KI NE DAN IN KAUCEWA AUREN DA ABBA NA YAKE SON YI MIN....."
Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.
*Bismillahir Rahmanir Raheem*
*45&46*
A guje Ibrahim ya shigo gida har yana fad'uwa kasa Inna da take tsakar gida ta nufo shi tare da d'aga shi tana karkad'e mishi jiki tace " toh d'an tsokana wa ka tsokano ya biyo ka, ka shigo a guje haka?"
Yana haki irin na alamun ya sha gudu yace yana nuna mata kofan waje " Baba ne..... Baba ne sojoji suka tafi dashi".
"Wani Baban kuma Ibrahim"?" Ta tambaya cikin rashin fahimta.
"Baban mu, Baban mu na gidan nan" ya amsa mata tare da fara kuka.
Salati Inna ta fara tana tafa hannu cikin tashin hankali murya na rawa ta d'aga murya tana " kuna ina matan gidan ku fito dan Allah kuji abinda yaron nan yake fad'a"
Inna Asabe ce ta fito da gudu har tana tuntube bakin ta d'auke da salati itama nan suka kacame dasu da sauran yaran suna ta cacekuce dan sun rasa ta ina zasu fara kasancewar kowa ya san harkan sojoji wuyan sha'ani ne dashi a nan maiduguri.
Duk hayaniyar nan daya cika gidan mu har makota sun shigo 'yan jin gulma da da masoyan gaske ana ta jajantawa amma gwaggo Aisha bata leko ba balle asan tana gidan ko bata nan a wannan yanayin Baban Dije ya shigo shima hankali tashe amma ganin su Inna a wannan yanayin yasa yayi kokarin boye nashi tashin hankalin ya shiga kwantar musu da hankali kan cewa kada su tada hankalin su su bi komai a sannu insha Allah Baba zai dawo gida tunda ko makiyin sa zai bada shaida akan sa baya aikata wani mummunan abu shi dai bar shi da son kud'i.
Da wannan bayanan ya samu suka d'an natsu kowacce ta koma daki makota kuma suka koma gudajen su da addu'an Allah ya sauwaka.
Hankali tashe Hajara tayi sallama ta shiga cikin gida dan saukowan ta kenan daga napep 'yan suka tare ta da mummunan labarin nan, ganin babu kowa a tsakar gidan yasa ta nufi d'akin su tana kwad'awa Gwaggo Aisha kira kaman zata tsaga gidan amma bata ji muryan ta amsa mata ba, a zaton ta bata gidan ta fita ko sun fita da sauran matan gidan.
Turus tayi fuskarta cike da al'ajabi ganin mahaifiyar nata kishingid'e tana cin gyad'a mai gishiri hankali kwance, d'ago kai tayi ta kalle ta sannan tace meya faru kike ta kwala min kira kaman zaki tsaga gidan nan ko dai yauma kin zo min da labari me dad'i ne?"
Had'iye mamakinta tayi tace umma ni ba dan wannan nake kiran ki ba yanzu ina saukowa a napep naji ana ta kananan maganganu a anguwa wai sojoji har mota 2 sun zo sun tafi da Baban mu?"
Tab'e baki tayi tare da watsa gyad'an hannun ta a baki ta fara taunawa tana hararan ta tace" toh sai akayi me ko ni na aike shi yin mummunan aikin da zasu kama shin, kema kin san Baban ku da shegen son kud'i kinga kuwa wani ta'asan yaje yayi musu, tsuntsun da yaja ruwa shi ruwan zai doka".
Tunda ta fara magana Hajara take kallon ta cike da takaicin abinda take fad'a wai Baban mu ne mayen kud'i, toh ita fa in banda ance laifi tudu ne yanzu bata ganin laifin munanan ayyuka da take sai na Baban mu wanda ta tabbata da wata akasa dan bai aikata abinda mutane suke cewa ba.
"Ke ina tambayan ki kin min shiru, nace dai yauma aikin ya tafi yanda ya kamata ko?" Ta katse ta cikin tsawa.
Gyad'a mata kai kwai tayi dan wani malolon bakinciki ne yazo ya tokare mata wuya, washe hakora tayi cike da farin ciki tana ," Alhamdulillah hankali na ya kwanta amma ya ban ganki da kaya irin na jiya ba, saboda na saka rai zaki kawo mana kayan dad'i ko girki ban daura ba na zauna jiran ki".
Daki kawai ta nufa ta san in ta tsaya takaici ne zai kashe ta, saida ta kusan shiga daki sannan tace mata " mahaifiyar shi ta kira shi ya tafi"
"Uwar shi? Dan uwar shi ta kira sai ya tafi ya bar ki, lalle muna da sauran aiki a gaban mu dole ne mu raba shi da ita in ba haka ba zata kawo mana barazana cikin aikin mu".ta fad'a a masifance ita dai Hajara bata kara kula ta ba ta ida shigewa ta bar ta da kumfan baki.
***************************
Tunda Hajara ta tafi ban kara jin motsin sa ba ina ciki duk haushi ya ishe ni sai kunci nake ni kad'ai, koda naga zaman kuncin ba zai fishe ni ba fitowa nayi na kama dan aikace-aikace na ko zan ragewa kaina damuwa, cikin ikon Allah ko Ina farawa na mance da abinda ya faru.
Kitchen na shiga na had'a kayan da b'ata ina wankewa naji a jiki na alamun ana kallo na da sauri na waiwaya na gan shi tsaye yana karewa baya na kallo, yana ganin na juyo ya basar yayi kaman yanzu ne zuwan shi, karasa shigowa yayi cikin kitchen din ya bud'e fridge ya d'auko malt mai sanyi ya koma bakin kitchen din ya bud'e ya fara sha.
Ban kara juyowa ba amma ji nake kaman na juya nayi ta kallon shi dan ba karamin kyau yayi min ba, kama gulman shi nayi a cikin zuciya ta ina mutum kaman wani aljani ko wani Kaya ya saka sai yayi mishi kyau dubi dai singlet ne da 3 quater a jikin shi amma sai ya zama kaman wani dressing yayi na gani na fad'a ga kamshin sa kuwa duk inda zai je kamin ya isa kamshin ya riga shi isowa haka kuma ko ya tafi zai dad'e a wajan.
Ta kasan ido na kara kallon shi yana tsaye a inda yake bai motsa ba gashi ni kuma na gama wanke-wanken ina son fita amma na rasa yanda zanyi saboda duk ya tare hanya yayi bake-bake babu wajan wucewa ni kuwa bana son yi mishi magana dan har yanzu haushin shi nake ji.
Wasu ayyukan na shiga kirkira wai ko zai gaji ya bar hanyan amma saima gani nayi ya gyra tsayuwar shi ya jingina da kitchen cabinet din ya cigaba da kurb'an malt din yana kara tsare ni da ido, gajiya nayi da kirkire kirkiren nayi shahada na nufo kofan wai ko in yaga nayi niyyan fitan zai bani hanya amma ga mamakina ko motsawa baiyi ba balle ya matsa.
"Zan wuce" nace ba tare da na kalle shi ba.
"waya hana ki wucewa?" Yace shima yana wani d'aure fuska " naga ka tare hanya ne"...
Dan matsawa yayi gefe ya bar wani karamin hanya,ta gefen ido na kalle shi naga har yanzu yana rike da malt din a rai na ina mamakin wani irin kurb'a ce yake mata tun dazu ace bai kare ba, sauke ido na nayi cikin sauri nazo zan wuce amma sai yasa hannun shi na dama ya tare hanya.
Dawowa nayi da baya zan koma kitchen d'in nan ma ya jefar da empty tin na malt din ya kara tare min hanya ya zamto ina tsakiya hannayen shi ya zuba min wayan idon shi mai rikitar dani, cikin azama nayi kasa da nawa idon dan ba zan iya jure kallon nashi ba.
"Da kike wani neman guduwa cinye ki zanyi?" Ya tambaya cikin wani irin murya da ban san yana da ita ba, ban iya bashi amsa ba na kara yin kasa da kaina, ina jin yanda zuciya ta take zillo kaman zata fito saboda kusancin namu yayi yawa.
"Hmmm na gane duka gulma ne u just want me to repeat what we did in d morning" yace yana bina da wani irin killer smile.
Cikin zaro ido na d'ago kai na da niyyan yi mishi masifan sharri daya lak'a min amma mukut na had'iye kaya na saima zaro ido da nashiga yi sakamon tattausan bakin shi da naji akan nawa.
Kiciniyar kwace kaina nake amma bai bani daman hakan ba, sai kara manne min yake tun inada karfin kokuwa har karfi na ya kare wani irin kasala na sauko min tare da hawaye kaman an bud'e famfo.
Jin hannuwan shi sun fara min yawo a jiki yasa na tattara sauran courage daya rage min na ture shi ya kuwa tafi da baya har yana bigewa da cabinet din bayan shi ni dai ban juyo ba balle in san halin da yake ciki na fad'a daki tare da rufo kofa na jingina ina maida numfashi.
"Ouch " yace yana rike bayan shi inda ya bugun ya shafawa yana murmushi tare da jin kaman ya bini ,shi dai wannan sabon jaraba daya same shi a kaina bai tab'a shiga irin wannan yanayin ba dan ko lokacin da yake karatu a kasar waje ga dai mata birjik suna yawo half nacked wasu har tallahn kan su suke kawo mishi amma koda wasa bai tab'a jin kwatancin abinda yake ji game dani ba akan su.
"Why! Why her?" Ya furta can kasan makoshi ganin babu mai bashi amsa yasa ya koma cikin parlour ya zauna ya dafe kai yana neman mafita.
Na dad'e jingine da jikin kofan ido na rufe ina wani irin murmushi da yake fitowa daga karkashin zuciya ta, me ya faru tsakanin mu yanzu? Na tambayi kaina.
"He just kissed me" nacewa kaina ina rufe fuskata da tafin hannaye na duka biyu ina kara fad'ad'a murmushin da nake saboda ina ayyanawa a raina cewa yana sona, yes yana sona in ba haka babu abinda zai saka yayi kissing na.
"BA SONKI NAKE BA, ZAN AURE KI NE DAN IN KAUCEWA AUREN DA ABBA NA YAKE SON YI MIN....."