← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 71

Sashe 22

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ras yaji gaban shi ya fad'i meya kai shi fad'in haka gashi har an tabo zancen da baya so ayi ta agaban Abba, shima dariyan yayi da son kawar da zancen yace" yauwa Mom abokinaboki na shamsuddeen nan da kike ta yabon shi kullum gobe ne fa auren shi anjima kad'an ma zan je dinnern kuma dasu Sadiq....."

"Aikin kenan zuwa dinnern wasu amma kai baka tab'a tunanin kaima kayi settling down, ko har yanzu kana tsamanin yaro kake komawa?" Abba ya katse musu zancen cikin daure fuska da zaka san ran shi a bace yake.

"Anyway duk ma laifi na ne da na zuba maka ido ina kallon ka da sunan ina jiran ka kawo min matar da kake so da kan ka,but tunda baka fahimta ba let me make my self clear, kwana 3..... Wallahi kwana 3 kacal na baka in baka fito da wacce kake so ba kauye zan je in samo maka mata cikin 'ya'yan dangi, in kuma ka d'auka wasa nake maka ka jira kwana 3 ka gani" Abba yana gama maganan shi ya mike fuuu ya bar musu parlon.

Cikin wata irin murya mai cike da tashin hankali ya rarrafo gaban Mom ya fara magana" Mom pls ki bashi hakuri wallahi ni banida wacce nake so a yanzu dan Allah ya kara min lokaci wallahi zan kawo ta har nan ku gan ta".

"Wannan karon nima babu hannu na a ciki saboda ka kai Abban ka makura sannan ni kaina ina son ganin auren ka ko dan jikoki su cika mana gida, so count me out of this" itama tana gamawa tabi bayan mijin ta suka bar Zafar cikin fargaba da tashin hankali.
[1/26, 7:06 AM] Golden Pen Writer's Assoc: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹

🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*16*

Zafar ya kai kusan 30 mins a zaune wajan sai share gumi yake duk da sanyin A.c dake parlor amma bai hana shi jikewa da gumi ba, ta ina ma shi zai nemo mata cikin kwana 3 kacal, shi fa ya raina 'yan mata 9ija kuma koda yayi karatu abroad bai samu wacce ta kwanta mishi a rai har yace zai iya auren ta ba.

Ringing d'in waya ne ya dawo da shi hayyacin sa amma ya kasa d'aga hannu ya d'auki wayan balle ya amsa,sai da akayi mishi 2 missed calls a na 3 ne ya d'auki wayan ya kai kunne yayi shiru.

"Zafar kana ina ne baka karaso ba, tun d'azu Shamsuddeen ya dame ni da na kira ka wai har an kusan tafiya hall" muryan Sadiq yaji cikin wayan yana magana, bai iya bashi amsa ba ya cire wayan daga kunnen shi ya mike a hankali ya fara tafiya cikin kasaita daya zame mishi jiki.

Part d'in shi ya shiga bai tsaya a parlour ba ya wuce bedroom ya fad'a kan makeken gadon shi da a kalla zai lashe mutane 7 ba tare da wani takura ba, tunani kawai yake tayi dan komai na duniyan ya fice a ran sa bare zuwa bikin nan, bai dad'e da kwanciya ba d'ayan wayan shi ya fara ringing shima kaman ba zai d'aga amma ya daure ba tare da ya lura da sunan mai kiran ba ya amsa wayan, muryan ango Shamsuddeen yaji yana mishi magana.

"Haba Zafar yanzu ka kyauta min kenan, har an fara shagalin biki na baka ciki?"

"No Shams it's...., No just ba zan iya zuwa ba saboda wani dalili nd......"

"Dan Allah mana kada kace haka please ko minti 2 ne Zafar we really need u here ,pls I'm begging..."

"Stop that mana sai ka roke ni ne zan zo bikin ka, aiko saboda Sadiq zan zo ko yanzun ma wani issue ne yake son shige min gaba but gani ni nan zuwa tunda kace ko minti 2 then I will come sai dai ba zan dad'e ba" yana gama fad'in haka ya katse wayan tare da mikewa zuwa bathroom.

Can b'angaren su Ango kuma sadiq yana kallon Shamsuddeen daya gama waya yace" ya zai zo d'in?"

Gyad'a kai shamsuddeen yayi yana murmushi suka cigaba da shirin su.

******"""""*******

Tunda nazo gidan bikin na daure zuciya ta ake ta hidima da ni sai kai komo muke, cikin wannan yanayin ban fasa trying number Yaya na ba sai dai amsar daya ce a kashe har a wayan Maryam na gwada wai ko daga layi na ne a natan ma switch off ake ta maimaita min, bayan munyi sallahn la'asar Maryam ta takura min muka tafi saloon inda akayi mana gyaran gashi lalle sannan aka mana kwalliyan mu.

Muna dawowa daga saloon muka saka ankon mu na material Les dark blue da tie milk color sosai kayan suka zauna a jiki na, nayi wani kyau ina haske sai ka zata nice ma Amaryan , Maryam itama tayi kyau sosai abinta,

Lokaci yanayi mutane suka fara tafiya ga motoci birjik sai wanda ka zaba zaka shiga wasu kuma a nasu suke tafiya, duk yanda Maryam tayi min nasiha kan in saki raina cikin jama'a in kwantar da hankalin na Yaya na yana lafiya amma na kasa.

Ko da muka isa ma banyi wani abu ba na nemi waje na zauna kan wani table da babu kowa saboda ina bukatan kad'aici na fad'a duniyar tunani anya Yaya na lafiyan shi kuwa Allah yasa haka Allah ya kare min shi duk inda yake Ameen.

Haka na cigaba da tunanin shi ina yi mishi addu'a Allah ya kare shi yasa yana cikin koshin lafiya tare da kokuwa da hawaye cikin ido na da suke ta bara zanan zasu fito ina maida su ciki.

****************

A hankali yake takun sa cikin natsuwa da kasaita ya nufi wata bakar latest Honda wanda zai fita dashi, tsab yake kaman wani basarake yayi matukar kyau cikin half jamfa na wani arnanen voile milk color mai duhu wanda ya kara haska farar fatan sa, bai saka hula ba,gashin kan shi da sajen shi sun sha gyara sun kwanta lub sai sheki suke sai kamshin tsaddaun perfumes d'in shi yake, bai yiwa iyayen nashi sallama ba ya fad'a motan shi yaja ya tafi.

Sowan abokan sa sosai ke tashi a lokacin da ya iso na murnan zuwan nashi dan wasu sun fidda ran cewa zai zo, bai biye musu ba hannu kawai ya d'aga musu ya wuce ya samu waje ya zauna yana auna maganan Abban shi wai shi zai had'a shi aure da 'yar kauye shida na birnin ma basa burge shi in aka aura mishi ita ko Ina zai kai ta, oho.

Yana cikin zancen zuci yaji an dafa mishi kafad'a a dan razane ya d'ago yaga Sadiq ne tsaye a kan shi yana mishi murmushi yace " lafiya kake kuwa tun d'azu ina tsaye s kan ka ina maka magana baka ji ba har sai da na tab'a ka, kuma baka je kun gaisa da Shams din ba kazo ka zauna kai kad'ai".

Zafar kallon shi kawai yayi ya d'auke kai ba tare da yace mishi ci kan ka ba kuma bashi da niyyan tankawan.

A zuciye Sadiq ya mike zai bar wajan yana fad'in " d'an rainin hankali kada Allah yasa kayi maganan ai dama ka saba wulakanta mutane...".

Caraf yaji Zafar ya riko hannun shi ta baya tare da dawo da shi baya fuska a had'e yace" seat"

Ba musu Sadiq ya koma ya zauna yana mai nazarin yanayin Zafar d'in ,duk da bai cika faran-faram da mutane ba amma yaga tarin damuwa da tashin hankali a tare da shi kasancewar shine mafi kusanci dashi bayan iyayen shi.

"Wats wrong u look so disturbed?" Sadiq ya tambaya cikin kulawa.

Hannun shi duka 2 ya d'aura a goshi yana murzawa kaman ba zai amsa ba can kuma yace" ina cikin damuwa Sadiq kasan yau Abba ya dawo da naje...."

"But naga kayi aski ai ko an bashi labarin kaje wani party ne?" Sadiq ya tambaya yana dariya.

"Shut up just shut up it'ss not a joke ina gaya maka damuwa na nd u e making fun of me" Zafar ya katse shi a hasale.

"I'm sorry sorry pls I don't mean it naga kawai shine matsalan ka da Abba most time" cikin rarrashi da kwanantar da murya Sadiq yake magana yaga da gaske abokin nashi ya fusata.

"In wannan ne da sauki kaima kasan ba zai dame ni ba cos I'm used to it " sai da ya sarara yana had'iyen zuciya alaman abinda zai fad'a ya mishi zafi yace "can u imagine abba ya bani 3 days wai in kawo matar da zan aura ko ya had'a ni da 'yar kauye".

Dariya Sadiq ya kwashe da shi harda rike ciki yace" kai nagodewa Abba yayi min maganin ka Wallahi ba ka raina 'yan matan Nigeria gaba d'aya ba, shikenan anyi maka mai kankat waya ga Zafar da village girl.

Kasan me on ur wedding day ko kuma on ur dinner with d village girl nine zan....."
Chapter 22 · 0% Book details