← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 53 OF 71

Sashe 53

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da kyar naja jiki na zuwa kan gadon na cigaba da kuka na , shima tunda ya fita a d'aki na yake hawaye dan wani irin kuna yaji zuciyar shi nayi mishi zai iya ratsewa da Allah ba'a tab'a fad'a mishi kalma mai d'aci da k'ona zuciya irin wannan ba.

Da auren nashi akai na har nake iya kallon tsaban idon shi in mishi maganan wani katon banza can, wani wawan naushi ya kaiwa bango kaman shine yayi mishi laifin yana cigaba da hawayen takaici.

A wannan daren babu wanda yayi wani baccin kirki tsakanin mu kowa da abinda yake tunani har gari ya waye.

************************

A b'angaren Baban mu kuwa tunda suka had'a shi da ruwan sanyin nan sukayi tafiyar su suka bar shi cikin azaba tun yana sanin inda hankalin yake har ya suma ya zama bai san a Ina ma yake ba, sai bayan awa daya sannan ruwan ya daina zuba sannan suka kunna wata na'ura Mai feso mishi da zafi, nan da nan d'akin ya kuma d'aukan zafi wanda ya haddasawa Baba farkawa babu shiri.

Sunayan Allah yake ta ambata yana jin shi kaman a cikin wuta yake ya rasa ta inda zafin yake shigowa shi dai bai ga wuta a d'akin ba.

Wata murya yaji ya cika wajan ana " ka shirya gaya mana gaskiya ko har yanzu baka horu ba"

" Wallahi zan fad'a...zan fad'i duk abinda kuke son ji dan girman Allah ku cire daga zafin nan kome kuke so zanyi muku na rantse muku..." Baba ya amsa musu cikin tsananin azaba.

Wani irin dariya yaji an kece dashi sannan kaman da wasa yaji zafin yana raguwa zuwa kaman minti goma yaji zafin ya ragu sosai, haske suka Kara kunnawa yanzu ma daidai wajan shine kad'ai hasken ya tsaya baya iya ganin su sai haske da yake jin yana saka idon shi zugi da rad'ad'i, mutum daya yaga ya ratso ta cikin wani glass sannan ya shigo inda yake amma idon sanye da wani bakin glass hannun shi rike da bakin kyalle yana zuwa kusa da Baba ya d'aure mishi idon sa sannan ya finciko hannun shi ya fara Jan shi suka fara tafiya.

Saida sukayi mai nisa sannan yaji an ingiza shi ya Fad'i kasa daga bays suka kunce mishi idon, farko ma hasken rana ne ya fara dallaro mishi ido yayi sauri ya runtse idon tsawa da yaji an daka mishi yasa ya bud'e ido babu shiri yana rarraba ido duk da yanda yake jin zafin ranan har cikin kwakwalwan shi.

Manyan sojoji ne sun kai su goma zaune akan kujera da wani table a gaban su, gefen su kuwa hagu da dama duk wasu sojojin ne rike da bindigu sunyi layi-layi.

"Ka shirya gaya mana komai Mallam Hassan?" Daya daga cikin mayan sojojin ya tambaya yana kallon Baba da yake durkushe a gaban su kan shi a kasa kaman mai neman gafara, cikin rawan jiki yace " wallahi Allah zan fad'a muku ...Allah zan sanar muku da duk abinda kuke son sani ".

Gyad'a kai sukayi gaba dayan su cike da gamsuwa " yace toh menene shirn ku na gaba?"

Mukut Baba ya had'iye wani bushasshan yawu na fargaba da ya tsaya mishi a makoshi ya bud'i baki yace" Shirin mu na gaba shine........".

Tofa me Baban ZAREEFA yake shirin dad's🤭🤭🤭🤭
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*47&48*

Bai san adadin lokaci da ya b'ata a cikin duhun nan ba yana nan dai zaune ne kawai amma ba zai iya cewa dare ne ko rana ne ba, addu'oi kuwa babu wanda baiyi ba yana son yin sallah amma rashin sanin inda gabar yake da kuma rashin ruwan alwala yasa ya hakura.

Zuwa wani lokaci ya tuna dai ko azahar ba'ayi ba suka kawo shi nan dan haka ya tashi yayi taimama da d'an kasa- kasa daya samu ya kabbara sallah, azahar,la'asar da magarib ya sallata ya sallame saboda tashin hankali da yake ciki ko yunwa baya.

Haushin karnuka da yake jine ya san cewa dare yayi nisa sosai bai tsaya b'ata lokaci ba ya kawo sallah isha'i da 'yan nafilfilu ya raya daren ko gyangyad'i baiyi ba balle bacci, rabon da Baba yayi nafilan dare shi da kan shi ya manta balle Kuma wani.

Da washe gari yana zaune makoshin shi duk ya bushe saboda kishi yaji an dallaro mishi fitila a ido wanda ya haddasa mishi rintse idanun nashi babu shiri har wani radadi yaji idon na mishi ko dan ya kwana a cikin duhun ne oho.

"Oga he don wake up" yaji wani kakkausar murya daga wajan ana magana,tafiya ya fara ji na mutane da bai san adadin su ba sun nufo inda yake a tsorace ya mike tsaye jikin sa na karkarwa yana jiran yaga ta ina zasu bullo dan har yanzu bakin shi da suka buge yana nan a kumbure har fuskan shi.

Cak yaji kafan ya d'auke lokaci daya amma baya iya ganin su kasancewar har yanzu hasken daidai fuskan shi yake wajan su kuma duhu.

"Kai ne Mallam Hassan ko?" Yaji an daka mishi tsawa, jikin shi na cigaba da bari ya gyad'a musu kai.

"Open ur mouth and answer me my friend, nace kaine Mallam Hassan?"

Duk da bai fahimci turancin da akayi mishi ba amma cikin sauri ya amsa da " nine...nine Mallam Hassan ranka ya dad'e".

" Good bana son gardama ko taurin kai ka gaya mana menene next target d'in ku me kuke shirin aikatawa a gaba?" Yaji wani murya daban ya tambaye shi cikin gurb'ataccen hausar shi.

Cikin rashi fahimta yake kallon inda yake jiwo muryan su duk da baya iya ganin su dan kwata-kwata bai gane inda zancen nasu ya dosa ba.

"Ka bamu amsa ba wai ka tsaya zare Mana ido ko kuma kana so mubi da kai yanda muka bi da partner ka" wani cikin su ya kara daka mishi tsawa, Baba duk ya rud'e ya rasa inda zai saka ran shi yaji dad'i sannan ko kad'an bai fahimci tambayan nasu balle ya basu amsa kaman yanda suka bukata illah jikin shi da yayi ta b'ari kaman an jona mishi shocking.

"Dole yayi mana taurin kai oga saboda babu wani criminal da za'a kawo ya amsa laifin shi cikin sauki but zamu bi dashi yanda muka bi da sauran.

Step 1" yaji wani murya daban har yana amsa kuwwa, kalle-kalle ya fara yi a matukar tsorace kamin ya ankara yaji ruwan sanyi harda kankara suna zubowa daga sama daga inda yake tsaye nan da nan yaji wani irin sanyi da tunda yake bai taba jin irin shi ba ya rufe shi a take ya fara rawan sanyi hakoran shi na had'uwa da juna.

"Ka huta cikin sanyin ka in ka shirya mana bayani zamu dawo" wani yace suka juya suka bar Baba cikin rawan sanyi yana son tsaida su amma ya gagara bud'e baki balle magana ya fito, yana ji yana gani suka tafi tun yana jin sawun kafan su har ya daina ji.

******************

A gidan mu kuwa babu wanda yayi baccin kirki saboda tashin hankali domin ganin har dare babu Baba babu labarin shi, masu nafila nayi masu addu'oi nayi in ka cire gwaggo Aisha da tasha baccin ta harda minshari, koda gari ya waye Baban Dije da wasu 'yan uwan Baban mu suka fita bin baracks ko Allah zai sa su dace su sami inda aka kai Baba.

Bayan tafiyan su babban tukunya Inna ta daura a tsakar gida na abincin sadaka da tayi niyya tun cikin dare sanin cewa sadaka yana maganin masifa, Inna Asabe tana gani ta fito ta kama mata suka fara aikin tare. A can dakin Gwaggo Aisha kuma drama ce ta kaure tsakanin su ita da Hajara kan cewa wai lalle sai ta fita tazo gidana sun kammala aikin su da suka fara ita Kuma Hajara tace babu inda zata je ta bar ta taji da tashin hankali na rashin Baban mu.

"Ke me yasa baki da wayo a rayuwar ki ne, ban san yaushe zakiyi hankali ba Hajara wani uban ne har kike kumfan baki akan sa, tunda aka haife ki meya tab'a tsinanana miki a matsayin sa na uba a gare ki , ina ni din nan da kika raina nice nake fad'i tashi har kuka taso.

Wannan aikin da nake dan waye nake yin shi dan ke da 'yan uwan kine ku samu rayuwa mai kyau koda bayan raina amma kike shirin watsa min kasa a ido, waye wata Bintu da za'a ce ita ce mai abu a gidan nan tazo tana d'aga mana hanci, hanyan da tabi ta hau muma shi zamu bi mu hau domin kowa ya san asiri sukayi har wannan d'an masu kud'in nan ya aure ta, in zaki farka daga wannan baccin naki ki farka ki kalli abinda duniya take ciki ba wai ki tsaya yin shirme ba"
Chapter 53 · 0% Book details