← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 51 OF 71

Sashe 51

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hannuwana na saka na toshe kunnuwa na dasu saboda yanda nake jin wa'yan nan munanan kalamai suna min amsa kuwwa a kunne na kaman an kawo loudspeaker saitin kunne na ana min magana dashi.

Girgiza kai na na fara yi Ina hawaye kada in yaudari kaina Zafar ba zai tab'a so na ba yasha furta min haka da bakin sa sannan ya tabbatar min da ba zai tab'a sona ba zai sake ni ne in time din alkawarin mu yayi.

Na tabbata yanzun ma haka take kawai ya tsiro da wata dabara ce yanda zai yaudare ni ya gama dani kamin mu rabu , dole ne inyi taka tsantsan domin tsira da mutunci na duk da yanzu ni da Kai na na fahimci na fada son shi ba na wasa ba kuwa.

Bedroom na wuce jiki a mace na zauna bakin gado hawaye na suna kara speed din gudun su inayi ina jin haushin kaina ko meye abin damuwa da wanda bai damu da Kai ba, na kan shiga mummunan tashin hankali in na tuna cewa zai iya rabuwa dani a koda yaushe dan ji nake kaman ba zan iya rayuwa babu shi ba.

Sai da naci kuka na koshi sannan na mike na shiga wanka, na dad'e a sosai ina wankan sannan na fito d'aure da towel wanda ko cinya ta bai ida rufewa ba tsefaffen gashin kaina da na wanke ya kwanto baya na ruwa na tsiyaya, direct mirror na nufa na ja stool na zauna tare da jona hand dryer na fara busar da gashi na.

Sai da ya fara bushewa na ajiye dryer na dauko mayukan gashi na shafa sannan na taje na saka rebon na tufke in pony tail kokarin kunche towel na fara domin inji dad'in shafa mai kaman wani abu yace juya baya ina juyawa muka had'a ido da mutum zaune akan gado na ya tsura min ido kaman zai cinye ni d'anye.

A zabure na mike da gudu zuwa bayi naga shima ya mike zai bini , haba kaman walkiya na shige na mayar da kofa na kulle harda murza key zuciya ta na harbawa da sauri-sauri.

Knocking ya fara yi a hankali yana " pls ki bude Zareefa ba abinda zanyi miki magana nake so muyi kinji?" Naji muryan shi cikin sanyin yana roko na.

Girgiza kai na kawai nake girgizawa kaman yana gani na baki na ya kasa furta komai dan na riga na gano abinda yake nufi ni kuma ba zan tab'a bari yayi min wayo ba haka kawai.

"Zareefa pls listen to me dan Allah ki bud'e kinji?" Nan ma shirun nayi mishi na kasa gaskata kunnuwa na wai yau wannan dan girman kan ne yake roko na harda sassauta murya jin suna na a bakin shi yasa naji kaman in fito inje gare shi saboda ban tab'a jin dad'in sunan nawa ba kaman a bakin shi.

Sai zuciya ta na kara gargadi na akan kar na biye shi duk salon yaudara be, hmmm maza kenan gaskiya sun kware a yaudara ina ma da gaske ya sauko ne muyi zaman mu.

Hakan da na saka a raina naji sabon kuka ya zo min anan na durkushe inayi ina jinsa yana ta min magiya da knocking amma ban amsa mishi ba har ya gaji ya bar wajan.

********************

Baban mu koda suka saka shi a wannan bakar mota sai da suka rufe mishi ido da wani bakin kyalle sannan suka d'auki hanya a cikin motan ma duk da idon shi a rufe yake amma sai rokon su yake yana basu hakuri, bige mishi baki da wani daga cikin sojojin yayi da gindin bindiga yasa Baba yin shiru bai kara yin koda tari ba balle ya Kara gigin magana sai faman tare jinin da yake zuba a bakin shi yake yana jin zugin tsakiyar kan shi.

Sunyi tafiya mai d'an nisa sannnan yaji sun tsaya duk suka fito shima fito dashi sukayi suna Jan shi dan har yanzu basu bud'e mishi idanun nashi ba.

Sunyi tafi mai nisa yana ta jin iface-ifacen mutane da hayaniya kala-kala har yaji sun iso wani waje shiru babu wani motsi balle muryan mutum, nan sun yi tafiya sosai sannan yaji sun tsaya a wani waje yana ji suka bud'e wani kofan karfe suka ingiza shi ciki sannan suka kunce mishi ido kamin ya dawo daidai yaji sun rufe kofan ta waje.

Wajen baki kirin take ko tafin hannun shi baya iya gani balle ya san a ina yake, shiru yayi ya zauna cikin wani yanayi mai wuyan fassara shi dai ya san shida fita a cikin wannan duhun sai ta Allah.
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*49&50*

Yawo ya dinga yi a motan nashi yaki komawa gida saboda shine zaman lafiyan shi gashi bai san waye kuma zai tunkara da maganan nan yaji sauki ba shi Sadeeq da ya san sirrin shi ma bai bashi goyon baya ba to ina zai je?

A wani karamin masallaci daya gani ya tsaya yayi sallahn mariba da aka kira bai tashi ba yana nan yana kai kukan shi ga Allah kan yaye mishi wannan sabon al'amari da yake ji game da ni, gashi a dalilin baya iya controlling kan shi har raini ya fara shiga tsakanin mu, ji yanda d'azu na tsaya ina mishi tsawa for god sake this village girl? Yace cikin ran shi.

Jiki a mace ya fito daga masallacin tare da addu'an Allah ya amsa mishi addu'oin da yayi, mota ya shiga maimakon yayi hanyan gidan shi direct hanyan main house d'in su ya mika horn d'aya kawai yayi mai gadi yazo ya bud'e mishi gate ya kutsa kai cikin gidan nasu.

Abba da Mom suna zaune a tsakiyar parlour da alamu basu dad'e da gama cin abinci ba domin ya tarar Mom sai aikin had'a kayan da suka b'ata take, kusa da Abba ya zauna tare da daura kan shi akan kafadan Abba sannan ya fara gaishe su.

Mom ma dakatawa tayi da aikin da take ta amsa mishi cikin kulawa sannan ta kwashi kayan tayi hanyan kitchen, Abba na ganin Mom ta bar wajan ya juyo ga tilon dan nashi da kyau yana shafa kan shi yace " ya akayi ne son naga duk yanayin ka ya canza?"

Salon da Abba yayi amfani dashi yayi mishi magana yasa yaji hawaye na taruwa a idon shi amma ya shanye tare da kakaro murmushi ya daura kan fuskar shi yace" bakomai Abba"

"Ni mahaifin ka ne Zafar na san yanayin kana cikin damuwa da kuma na farinciki, ba zan tilasta maka sai naji abinda yake damunka ba but ka sani in aka ce maka kana da iyali dole sai kayi hakuri da kai zuciya nesa domin mata da kake gani akwai su da rauni manzon Allah yace da kashin hakarkari aka hallice su, kaga kuwa a lankwashe suke in kace zaka mikar da karfin tsiya sai dai ka karya so kabi komai a sannu. Kaji ko?" Abba ya karasa yana shafa gashin kan shi.

Murmushi yayi yana gyadawa Abba kai dan ya san Abba bai san matsalar da take damun shi bane, yanda ya fahimci abin daban ne, a haka Mom ta dawo ta same su ta zauna akan kujeran dake opposite da inda suke zaune idonta akan su tace" me Baba da yaro suke tattaunawa ne?"

" Shagwab'a ke damun yaron naki, kin riga da kin shagwab'a shi tun farko gashi ya girma harda iyali bai san ya girma ba" Abba ya amsa mata yana dungure kan Zafar.

Hannu ta mika mishi tana " come here my boy ai yaro baya girma a gaban maman shi" da rarrafe ya karasa wajan kafan ta ya zauna tare da daura kan shi akan guiwar ta.

"Yi shagwab'ar ka yanda kake so d'ana ko akwai wani abu da kake bukata ne?" Rungume kafaun nata yayi ya girgiza mata kai, dariya ta saka tana "lalle yau yan shagwab'an na kusa kuwa".

Abba ma dariyan yayi suka fara consoling d'in d'an nasu tare da yi mishi hira mai dad'i har ya wassake ya fara dariya harda kyakyatawa, damuwan dake ran shi kusan kashi 70 ya ragu sai kusan karfe tara sannan yace zai tafi gida yayi musu sallama ya fito ya shiga motan shi ya nufi gida.

Yana nufo gida damuwar shi da yaji ya d'an ragu yaji ya dawo sabo , ji yayi kaman ya fasa shiga gidan ya koma amma haka nan ya daure ya shiga saboda ya san rashin shigan ba shine mafita ba, koda yayi parking ya d'an dad'e zaune a cikin motan tare da daura kan shi jikin staryn yana neman mafita.

Ya jima a haka sannan ya hakura ya mike jiki ba kwari ya nufi cikin gida.
Chapter 51 · 0% Book details