← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 71

Sashe 65

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kuut" yace da karfi harda zaro ido kaman wanda yaga abin tsoro " Amma wannan yarinya kin raina min wayo ki saka ni gadin ki sannan kice Wai in kwanta a kasa ke kuma akan gado? U re not serious" yace yana mikewa a fusace kaman gaske.

Cikin sauri na rike hannun shi idona na cikowa da hawaye nace " kayi hakuri pls kada ka tafi zo ka kwanta toh " wani murmushin gefen.baki ya saki ganin hakar sa na neman cika da ruwa.

"No ba matsala ki kwanta abin ki let me go to my room dan ban fiye son sharing room da mutum ba" yace yana kara tsuke fuska.

Matsawa baya na fara yi da sauri nace "zo ka kwanta pls kada kayi fushi kaji?" Bai ce min kala ba sai dai ya juyo a yangan ce yadawo da baya ya zauna tare da ayyana abubuwa dayawa a ran shi.
[2/23, 8:12 AM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*.

*62&63*

Jan bargon nayi na rufe har kaina ina jin sanyi a raina tunda ina jin motsin mutum kusa dani, shi kuwa a É—osane ya kwanta irin shi a dole alfarma yake min alhalin a zuciyar shi kuwa ji yake kaman ya taka rawa.

Kamshin sa duk ya hana ni sukuni ya cika min hanci sai wani natsuwa yake sauko min na musamman,shima ta b'angaren shi hakan yake kamshin turaruka da nayi amfani dasu masu sanyin duk sun dagula mishi lissafi ji yake kaman ya matso jikina ya rungume ni yayi maganin abinda ke damun sa,wani ɓangaren na zuciyar tayi saurin kwabar sa kan ya bi komai a sannu.

Muna nan kwance shiru kusan awa 1 amma babu wanda yayi bacci a cikin mu kuma babu wanda ya motsa,wata dabara ce ta fad'o mishi a rai nan da nan ya fara sake numfashi da d'an karfi alaman yayi bacci kenan.juyowa nayi a hankali na fuskance shi da yake ya juya min baya bana ganin fuskar shi sai yalwataccen gashin sa baki sidik da yake kwance na zubawa ido ina jin kaman in kai hannu na in shafa.

Dakin nabi da ido ganin ya kashe wuta mai hsken dim light kawai ya bari sai naji duk tsoro ya fara rufe ni, matsowa nayi kusa dashi ina "Zafar! Zafar!! "Cikin murya kasa-kasa ya basar dani yayi kaman da gaske baccin yake harda hadawa da minsharin karya wanda ya kara tsorata ni.

Kusa dashi na matsa sosai kaman zan shige jikin shi har yana jin d'umin numfashi na na sauka a wuyan shi,nan da nan kuwa yaji ya kara rasa natsuwan shi har ya kasa daurewa ya juyo idon shi a rufe amma ya daura min hannun sa na dama a konkoso na ya kara manne ni da jikinsa duk wai a cikin yana bacci yake.

Banyi gigin raba jikina da nashi ba saima kara gyara kwanciya ta da nayi saboda sai yanzu na samu natsuwan yin bacci, aiko ban kai minti goma ba bacci mai dad'in gaske yayi gaba dani na bar Zafar mai baccin karya yana karewa fuskana kallo kaman yau ya fara kallo na.

Tun daga kan giran idona ya fara kallo zuwa hancina haka yayi ta yawo da idn shi akan fuskata mai neman wani abu, da kyar yayi nasaran tsaida idanun nashi kan d'an mitsitsin baki na da yake dauke mishi hankali kullum, fuskar shi ya kawo dab da nawa ya hade goshin mu wuri daya yana goga min hancin sa akan hancina, da sauri ya dauke fuskar shi yayi baya kadan tare da rufe ido ganin nayi motsi ya zata farkawa zanyi.

Murmushi ya sake yana dawo da fuska shi wajan shi na da ganin na cigaba da bacci na cikin kwanciyar hankali, brushing lips d'in shi yayi akan nawa tare da lumshe ido jin taushin labban nawa har kwanyan shi.

Wani irin farinciki ya tsinci kanshi a ciki yana jim inama mu dauwama a haka, kasa hakura yayi saida ya kama lip dina na kasa ya dan tsostsa with his eyes closed.gyara min kwanciya yayi a jikinsa yasa hannayen shi duka 2 ya rungume ni tsam a jikinsa ya lumshe ido with the hope ko bacci zai iya daukan shi saboda yanda yake jin d'umin jikina da Kuma yanda yake jin kirjina ya hadu da nashi duk sai yaji ya shiga da nasani.

Haka yayi ta fama da kyar ya samu bacci ya dauke shi wuraren asuba. da washe gari a makare muka tashi ni dad'in bacci ya hana ni farkawa da wuri yayin da shi kuma rashin baccin da wuri yasa ya makara. 6:20am shi ya fara farkawa cike da farincikin we slept together,ya tsaya kallon innocent face dina da nake bacci na peacefully sai yaga kaman nafi kyau a haka.

Light kiss ya manna min a goshi yana murmushi sannan ya had'a fuska ya fara magana kaman gaske" ke Zareefa!! Ya haka? Daga taimako ga yanda kika wani kanainaye ni kika haye min jiki, amma da nine nayi miki haka sai kice da wata manufa nayi miki ko?"

Shiru nayi naki in motsa balle in bashi amsa duk kunya ya lullube ni dan gaba daya a jikin sa nake kwance, dariya kawai yayi ya cire ni a jikinsa yayi hanyan fita yana " in kin gama likimon sai ki tashi kiyi sallah, kin sa mun makara har na rasa sallah jam'i " ina jin shi amma ban tanka ba har sai da na tabbatar da ya fita sannan na mike na shiga bathroom domin yin alwala.

************************

Gidan mu yanzu ya zama kaman bashi ba ko ina shiru hatta da yaran gida sun canza kasancewar canjin da baba yazo dashi gidan, kullum da safe ya kan tara su Inna a parlour shi ya nemi gafaran su akan yanda suka zauna ada na yanda bai damu da sauke nauyin da Allah ya daura mishi ba sannan ya kanyi alkawarin canji a zamanta kewar su Kuma yana bukatan hadin kan su domin babu abinda zai tafi daidai sai sun bashi hadin kai .

Inna ta da Inna Assbe su kanyi mishi alkawarin bashi dukkan hadin kai da yake bukata yayin da ita kuma Gwaggo Aisha takan tabe baki ta dauke kai saboda ita wannan tsarin kwata kwata bai mata ba, tafi jin dad'in rayuwar gidan mu na da yanda kowa yake kara zube kayi duk abinda kake so babu mai hana ka musamman ita da take taka duk wanda take son takawa a gidan ta kwana lafiya.

Kananan yaran gida duk yasa an saka su a islamiya da boko cikin ikon Allah sun natsu tare da maida hankalin su ga karatu, maganan tallah Kuma babu shi dan ya dade da soke ta wanda hakan sam Bai yiwa Gwaggo Aisha dad'i ba.

Da farko taso tada masifa a tsakar gida kaman yanda ta saba yi shekara da shekaru, sai dai nan da nan Baba ya taka mata biriki ta hanyan da bata tab'a tsammani ba.

Kiran su yayi parlour shi ya zaunar dasu sannan ya fara magana;

"Ina son ku bani hankalin ku gaba dayan ku kuma ku fahimce ni Dan daga rana irin ta yau bana son inga kun daurawa ko wani yaro tallah a gidan nan,ina son ku bani hadin kai su samu tarbiya da karatu da suka rasa a baya.a kullum sai naji kaman in zubda hawaye in na tuna yanda gidan yake a baya sannan bana gajiya da naiman yafiya ku akan...."

"A'a dakata mallam akan me zaka ce ba zamu daurawa yara abin sana'a ba sai dai mu zauna kara zube babu sana'a, kana wai su je boko da isamiya ko menene?" Gwaggo Aisha ta katse shi a hasale tana kumbure kumbure cikin fushi shi kuwa ido ya zuba mata ganin hakan kuwa yasa ta cigaba da masifarta.

"Ni dama na rasa gane kan ka tunda ka dawo daga barikin sojojin nan duk ka canza ka zama sabon mutum, da farko ina tantaman abinda zuciyata take raya min game da hakan amma yanzu na gaskata tabbas Mallam wajan dukan nan da sukayi maka sun daki kan ka har ya jawo maka tabin hankali. Toh wallahi ni dai ba zan dauka ba tun wuri ka canza shawaran na fad'a maka ehe" ta karasa cikin fushi.

Baba kuwa murmushi kawai yayi ya a kada kai ya tabbata da ace a can baya ne ta fad'a mishi wannan kalmar ta tabin hankali, da ya nuna mata haukan amma a yanzu kam yafi karfin wannan.

Cikin natsuwa da ta fara zama jikin shi yace" ba shawara nake baku ba Aisha wannan umarni ne a matsayina na uban yaran kuma miji a gare ku".

"Hmmmm su miji manya ni dai na gaya maka wannan umarnin naka ka bawa saunayen matan naka amma banda ni domin babu abinda zai hana ni yin sana'a" Gwaggo Aisha ta mayar mishi da martani cikin gadara.
Chapter 65 · 0% Book details