Sashe 49
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shirin bacci na nayi bayan na gama kallon, na sha bacci cikin kwanciyar hankali sab'anin Zafar daya kwana cikin wani yanayi da shi kan shi ba zai ce ga inda ya dosa ba shi dai kawai so yake ya zauna kusa da ni ko kuma inda zai samu yayi ta kallo na, tun yana d'aukan abin da sauki har ya fara jin haushin kanshi wai me yasa ya damu da wani lamura nane? in ya kalle ni uban me zan bashi illa ma in b'ata mishi rai da sabon rashin kunya da na samo, bayan wannan ma tun lokacin da ya d'auke ni ya fito dani parlor jiki na da nashi da ya had'u yake kewar d'umin jiki na tare da kamshin jikina mai sanyi da tsayawa a rai sai dai dole ya matse gudun kada raini ya shiga tsakanin mu.
Ya san bakomai yasa ya damu da lamurana ba maybe tausayi na da ya fara jine kawai dan yaji bani da lafiya, " hakane ma" ya furta a sarari yana mai kara bawa kanshi karfin guiwa da kyar dai ya samu bacci yayi nasaran sace shi a wannan daren.
Da washe gari na tashi da sauki dan wannan nauyin da zuciya ta yayi jiya yayi sauki hakan ne ya bani daman fara aiyuka na kaman yanda na saba, bayan na gama share ko ina tass na gyara sannan na shiga wanka ban dad'e ba na fito light make-up nayiwa fuskata na shirya kaina cikin English wears riga da skirt pink color anyi mishi ado da flowers blue hakan yasa na yane kai na da blue vail, kayan bai wani matse ni ba amma ya zauna das a jikina ya min kyau sosai.
Zagewa nayi ina girki sanin cewa Hajara zata iya zuwa at any moment,kayan dad'i nake dafawa dan haka gidan ya cika da kamshi masu dad'in shaka,kamshin nan shi ya fito da Zafar daga d'akin shi sai bud'e hanci yake yana lumshe ido tsohon yunwar shi ta jiya na dawowa sabo fil.
Kofar kitchen d'in yazo ya tsaya yana kallon yanda nake aiki gaba daya hankalina yana kan aiki ban san ma da zuwan shi ba,shi kuma controlling d'in kan shi yake akan abinda zuciyar shi take ingiza shi ya aikata dan ji yake kaman yaje ya rungume ni yaji wannan d'umin jikin nawa da wannan daddadan kamshin mai sanyaya zuciya amma ya daure yayi gyaran murya Wanda ya d'an firgitani na juyo a d'an razane na ganshi tsaye cikin kayan baccin sa farare kal da alamu tashin sa kenan ko wanka baiyi ba.
Kaman ana min dole nace mishi" Ina kwana" saboda ganin babu wasa a fuskar shi, maimakon ya amsa min sai cewa yayi " ki tabbata kinyi da rabon masu aiki tunda kin samu lafiya" sai da na turo baki sannan na bashi amsa da cewa " ni bada su nayi ba dan Hajara zata zone shiyasa nayi girkin".
Kara had'a fuska yayi yace" try anything stupid and see"Yana gama fada ya juya ya fita ba tare da ya jira amsa ta ba, " zaka gani kuwa ai ka daina cin abinci na a gidan nan tunda kai d'an wulakanci ne"nace ina cigaba da aiki na.
Bayan kaman 30 minutes na kammala komai na jera su kan try na fito na wuce parlour na ba tare da nabi ta kan shi da na gan shi zaune a main parlour ba, shirya su nayi anan tsakiyar parlour na tare da kara saka turaren wuta na dawo inda na shirya kayan abincin kenan sai gashi nan ya shigo da fuska kaman an aiko mishi da sakon mutuwa.
"Ina na masu aikin da na gaya miki?"
"Banyi dasu ba na amsa mishi ina kara gyara zamana a gaban warmers d'in, bai saurare ni ba direct kai tsaye ya karasa shigowa da niyyan zai d'auke warmer d'aya, cikin azama na kai hannaye na duka biyu na rungume su a kirjina tare da turo baki ina " ni wallahi ka bar min kayana".
Bai saurare ni ba yana zuwa yasa hannu ya d'agani cid'ak kaman wata karamar yarinya zai ajiye ni a gefe na rike shi gam ina "wallahi ba zaka d'auka min ba ni banyi da rabon ka ai na san cewa kai kake cinyewa ba wasu masu aiki da kake bawa".
Yanayin yanda na cukuikuye shi na rike sai ya haifar mishi da kasala kuma dama abinda tun jiya zuciyar shi ta kwad'aitu da shi kenan,da gangan yayi fara kiciniyan kwace kan shi ni kuma ina kara rike shi akan ba zai d'auka ba kan kace me kokuwa ya kaure tsakanin mu anan yayi amfani da wannan daman hannayen sa babu inda basu je ba a jiki na, ni kuma a hauka na ban kawo komai a raina ba na zata duk cikin kokarin kwace kan shi yake a hannu na.
Sallaman Hajara ne yasaka shi saki na cikin sauri ya tashi itama Hajara cikin sauri tayi hanyan parlour dan tunanin ta wani abu daban ya bata, murmushin mugunta shimfid'e a fuskar shi yace " ga tsaraba nan kin tari yayar ki dashi,sai ki san bayanin da zaki mata "sai a lokacin na fahimci abinda ya faru duk sai naji kunya ya rufe ni me ko zan cewa Hajara ai babu abinda zan fada in wanke kaina,dafe kaina nayi cike da takaicin abinda ya faru tare da dana sanin me yasa na biye shi dana sani da barin shi nayi ya d'auki abinda yake so.
Plate ya d'auka ya bud'e warmers d'in ya d'ebi abinda yake so ya fita abin shi ba tare da na sani ba domin nayi nisa cikin tunani,ita kuma Hajara bata tsaya a main parlour ba direct fita tayi ta zauna a inda ta zauna jiya tare da dafe kai duk Gwaggo Aisha taja mata wannan abin kunyan asuban fari ta taso ta kan ta shirya tazo kada ya fita aikin su ya koma baya.
Hankalin shi kwance yaci abincin sa yana ta sakin murmushi shi kad'ai kaman wani sabon kamu,he really enjoys what happened between us now, fitowa nayi main parlour ganin zaman ba zai fice ni ba .
Wani tukikin bakin ciki ne naji ya tokare min wuya ganin yana ci min abinci,duddubawa nayi ko zanga Hajara amma ko alamarta ban gani ba.
Komawa nayi cikin Ina ta kumbura saboda haushi na san kila ta koma gida shikenan ya rusa mana budget ina ta murna yau ma zamu yini muna shan hiran mu sai gashi ko gaisawa bamuyi ba ya kore ta.
Zaman ta kaman da 15 minutes sai ga Amadu yazo yin aikin sa, maimakon yayi aikin suka bige da hirar su cike da son junan su har Zafar yazo ya wuce da mota bai gama aikin ba ganin sa ne yasa ya maida hankali kan aikin sa,tana zaune ya kammala itama ta mike tace zata koma gida tare suka fito ya rako ta har gida sannan suka rabu cike da kewan juna.
Baba Yana zaune a majalisar shi tare da 'yan maula daya samu yana d'an miko musu da na cefane,daga nesa suka hango motocin sojoji har guda 2 sun nufo su, Baba Yana ganin su cikin sa ya murd'a ya mike jiki na b'ari yace "yau kuma me ya kawo wa'yan nan azzaluman cikin anguwan nan" yana magana ne yana nufan hanyan gida amma ko ten step baiyi ba motocin suka karaso tun kamin motan ya tsaya suka fara durowa daga ciki tare d'aga musu tsawa "kada wanda ya motsa daga nan".
Cak Baba ya tsaya yana tsiyayen gumi duk ya firgice.
"Waye Mallam Hassan a cikin ku?" Suka tambaya.
A tare mutanen wajan suka nuna baban mu da yake tsaye yana karkarwa.
"Kai ne Mallam Hassan ?" Kai kawai Baba ya iya gyad'a musu.
" Common my friend oya! oya! shiga mota mu tafi"wani daga cikin motan ya fad'a, wasu guda hud'u nufo shi fuska a murtuke babu alaman sun tab'a koda murmushi balle dariya, hannu Baba ya shimfid'a yana kokarin rokon su tare da basu hakuri , d'ayan ya d'aga katon bindigan hannun shi yace yana musu gardama wallahi zasu harbe shi a wajan su wuce kuma sun harbe banza.
Gudu-gudu Baba ya nufi wata bakar mota da sai yanzu ya lura da ita suka hankad'a shi ciki babu b'ata lokaci suka fice daga anguwan da matukar gudu.
" Allah ya kiyaye mu da basu d'ubi kowa daga cikin mu ba sai shi kad'ai suka nema" inji wani dattajo cikin 'yan zaaman majalisan.
"Ni dama wannan kud'i na Mallam Hassan akwai ayar tambaya ace mutum yayi kud'i lokaci d'aya"? Wani ma ya kara nashi.
" Ai ko yanda suka ciko motoci saboda shi kad'ai kuma kun san abin azimun ne"
" Kunga yanzu ba lokacin wannan bane mu watse kamin su canza ra'ayi su dawo su had'a da mu"
fad'an hakan ke da wuya duk suka watse cikin abinda bai fi kiftawar ido ba, nan da nan labari ya cika anguwa cewa sojoji sun kama Baba sun tafi dashi.
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
✠*✠G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* âœâœ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*
Ya san bakomai yasa ya damu da lamurana ba maybe tausayi na da ya fara jine kawai dan yaji bani da lafiya, " hakane ma" ya furta a sarari yana mai kara bawa kanshi karfin guiwa da kyar dai ya samu bacci yayi nasaran sace shi a wannan daren.
Da washe gari na tashi da sauki dan wannan nauyin da zuciya ta yayi jiya yayi sauki hakan ne ya bani daman fara aiyuka na kaman yanda na saba, bayan na gama share ko ina tass na gyara sannan na shiga wanka ban dad'e ba na fito light make-up nayiwa fuskata na shirya kaina cikin English wears riga da skirt pink color anyi mishi ado da flowers blue hakan yasa na yane kai na da blue vail, kayan bai wani matse ni ba amma ya zauna das a jikina ya min kyau sosai.
Zagewa nayi ina girki sanin cewa Hajara zata iya zuwa at any moment,kayan dad'i nake dafawa dan haka gidan ya cika da kamshi masu dad'in shaka,kamshin nan shi ya fito da Zafar daga d'akin shi sai bud'e hanci yake yana lumshe ido tsohon yunwar shi ta jiya na dawowa sabo fil.
Kofar kitchen d'in yazo ya tsaya yana kallon yanda nake aiki gaba daya hankalina yana kan aiki ban san ma da zuwan shi ba,shi kuma controlling d'in kan shi yake akan abinda zuciyar shi take ingiza shi ya aikata dan ji yake kaman yaje ya rungume ni yaji wannan d'umin jikin nawa da wannan daddadan kamshin mai sanyaya zuciya amma ya daure yayi gyaran murya Wanda ya d'an firgitani na juyo a d'an razane na ganshi tsaye cikin kayan baccin sa farare kal da alamu tashin sa kenan ko wanka baiyi ba.
Kaman ana min dole nace mishi" Ina kwana" saboda ganin babu wasa a fuskar shi, maimakon ya amsa min sai cewa yayi " ki tabbata kinyi da rabon masu aiki tunda kin samu lafiya" sai da na turo baki sannan na bashi amsa da cewa " ni bada su nayi ba dan Hajara zata zone shiyasa nayi girkin".
Kara had'a fuska yayi yace" try anything stupid and see"Yana gama fada ya juya ya fita ba tare da ya jira amsa ta ba, " zaka gani kuwa ai ka daina cin abinci na a gidan nan tunda kai d'an wulakanci ne"nace ina cigaba da aiki na.
Bayan kaman 30 minutes na kammala komai na jera su kan try na fito na wuce parlour na ba tare da nabi ta kan shi da na gan shi zaune a main parlour ba, shirya su nayi anan tsakiyar parlour na tare da kara saka turaren wuta na dawo inda na shirya kayan abincin kenan sai gashi nan ya shigo da fuska kaman an aiko mishi da sakon mutuwa.
"Ina na masu aikin da na gaya miki?"
"Banyi dasu ba na amsa mishi ina kara gyara zamana a gaban warmers d'in, bai saurare ni ba direct kai tsaye ya karasa shigowa da niyyan zai d'auke warmer d'aya, cikin azama na kai hannaye na duka biyu na rungume su a kirjina tare da turo baki ina " ni wallahi ka bar min kayana".
Bai saurare ni ba yana zuwa yasa hannu ya d'agani cid'ak kaman wata karamar yarinya zai ajiye ni a gefe na rike shi gam ina "wallahi ba zaka d'auka min ba ni banyi da rabon ka ai na san cewa kai kake cinyewa ba wasu masu aiki da kake bawa".
Yanayin yanda na cukuikuye shi na rike sai ya haifar mishi da kasala kuma dama abinda tun jiya zuciyar shi ta kwad'aitu da shi kenan,da gangan yayi fara kiciniyan kwace kan shi ni kuma ina kara rike shi akan ba zai d'auka ba kan kace me kokuwa ya kaure tsakanin mu anan yayi amfani da wannan daman hannayen sa babu inda basu je ba a jiki na, ni kuma a hauka na ban kawo komai a raina ba na zata duk cikin kokarin kwace kan shi yake a hannu na.
Sallaman Hajara ne yasaka shi saki na cikin sauri ya tashi itama Hajara cikin sauri tayi hanyan parlour dan tunanin ta wani abu daban ya bata, murmushin mugunta shimfid'e a fuskar shi yace " ga tsaraba nan kin tari yayar ki dashi,sai ki san bayanin da zaki mata "sai a lokacin na fahimci abinda ya faru duk sai naji kunya ya rufe ni me ko zan cewa Hajara ai babu abinda zan fada in wanke kaina,dafe kaina nayi cike da takaicin abinda ya faru tare da dana sanin me yasa na biye shi dana sani da barin shi nayi ya d'auki abinda yake so.
Plate ya d'auka ya bud'e warmers d'in ya d'ebi abinda yake so ya fita abin shi ba tare da na sani ba domin nayi nisa cikin tunani,ita kuma Hajara bata tsaya a main parlour ba direct fita tayi ta zauna a inda ta zauna jiya tare da dafe kai duk Gwaggo Aisha taja mata wannan abin kunyan asuban fari ta taso ta kan ta shirya tazo kada ya fita aikin su ya koma baya.
Hankalin shi kwance yaci abincin sa yana ta sakin murmushi shi kad'ai kaman wani sabon kamu,he really enjoys what happened between us now, fitowa nayi main parlour ganin zaman ba zai fice ni ba .
Wani tukikin bakin ciki ne naji ya tokare min wuya ganin yana ci min abinci,duddubawa nayi ko zanga Hajara amma ko alamarta ban gani ba.
Komawa nayi cikin Ina ta kumbura saboda haushi na san kila ta koma gida shikenan ya rusa mana budget ina ta murna yau ma zamu yini muna shan hiran mu sai gashi ko gaisawa bamuyi ba ya kore ta.
Zaman ta kaman da 15 minutes sai ga Amadu yazo yin aikin sa, maimakon yayi aikin suka bige da hirar su cike da son junan su har Zafar yazo ya wuce da mota bai gama aikin ba ganin sa ne yasa ya maida hankali kan aikin sa,tana zaune ya kammala itama ta mike tace zata koma gida tare suka fito ya rako ta har gida sannan suka rabu cike da kewan juna.
Baba Yana zaune a majalisar shi tare da 'yan maula daya samu yana d'an miko musu da na cefane,daga nesa suka hango motocin sojoji har guda 2 sun nufo su, Baba Yana ganin su cikin sa ya murd'a ya mike jiki na b'ari yace "yau kuma me ya kawo wa'yan nan azzaluman cikin anguwan nan" yana magana ne yana nufan hanyan gida amma ko ten step baiyi ba motocin suka karaso tun kamin motan ya tsaya suka fara durowa daga ciki tare d'aga musu tsawa "kada wanda ya motsa daga nan".
Cak Baba ya tsaya yana tsiyayen gumi duk ya firgice.
"Waye Mallam Hassan a cikin ku?" Suka tambaya.
A tare mutanen wajan suka nuna baban mu da yake tsaye yana karkarwa.
"Kai ne Mallam Hassan ?" Kai kawai Baba ya iya gyad'a musu.
" Common my friend oya! oya! shiga mota mu tafi"wani daga cikin motan ya fad'a, wasu guda hud'u nufo shi fuska a murtuke babu alaman sun tab'a koda murmushi balle dariya, hannu Baba ya shimfid'a yana kokarin rokon su tare da basu hakuri , d'ayan ya d'aga katon bindigan hannun shi yace yana musu gardama wallahi zasu harbe shi a wajan su wuce kuma sun harbe banza.
Gudu-gudu Baba ya nufi wata bakar mota da sai yanzu ya lura da ita suka hankad'a shi ciki babu b'ata lokaci suka fice daga anguwan da matukar gudu.
" Allah ya kiyaye mu da basu d'ubi kowa daga cikin mu ba sai shi kad'ai suka nema" inji wani dattajo cikin 'yan zaaman majalisan.
"Ni dama wannan kud'i na Mallam Hassan akwai ayar tambaya ace mutum yayi kud'i lokaci d'aya"? Wani ma ya kara nashi.
" Ai ko yanda suka ciko motoci saboda shi kad'ai kuma kun san abin azimun ne"
" Kunga yanzu ba lokacin wannan bane mu watse kamin su canza ra'ayi su dawo su had'a da mu"
fad'an hakan ke da wuya duk suka watse cikin abinda bai fi kiftawar ido ba, nan da nan labari ya cika anguwa cewa sojoji sun kama Baba sun tafi dashi.
[12/14/2021, 7:54 AM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
✠*✠G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* âœâœ
https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/
*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶Ãt̶̶є αs̶̶s̶̶Ãd̶̶Ãσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єÃv̶̶є n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶Ãc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶Ãv̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✠*,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ Ãt̶̶ w̶̶Ãl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αÃn̶̶.*
*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*
Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.
*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*
*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*