← Book details Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 71

Sashe 48

Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ke kuwa ai zaki fimu sanin halin da take ciki tunda ke macece, yau ta tashi bata da lafiya wai tana fama da jiri da ciwon kai kinga alamun ciki sun bayyana a tare da ita amma fa a nawa hasasshen kenan ko kunje asibiti?" Abba ya amsa mata da wadatattacen murmushi saman fuskar shi yana kallon Zafar daya duke kai shima yana murmushin tare da girgizawa Abba kan shi.

"Ja'iri ji wani murmushi dan Allah Hajiya yaran yanzu da shegen son 'ya'ya suke" ya karasa yana dungure mishi Kai.

Mom da tayi suman zaune ko jin abinda yake fad'a ba tayi ba har yayi musu sallama ya fita ya bar ta baki bud'e.

Anan Kuma nida 'yar uwata sai hira muke zubawa yanda tun daga kofar shigowa zaka ji hayaniyar mu ba dan komai ba sai na labarin sabon saurayi da tayi na gidan mu take tana yayi mata amma tana gudun kada yaji ta tab'a aure da haihuwa ya guje ta...

Ni kuwa ina kara karfafa mata giwan cewa babu wanda zai kalle ta yace ta tab'a aure balle har ace ta haihu, muna cikin haka Zafar ya dawo gidan jiki a sanyaye amma tunda ya fara jiyo murya ta cike da nishadi muna hira yasa ya shigo da karfin shi, sallama yayi ya tsaya daga bakin kofa fuskar shi d'auke da tsantsan farincikin samu na a haka da yayi, bude min hannuwa yayi alamun inzo gare shi har zan watsa masa harara na tuna cewa ashe fa in a gaban mutane ne drama muke yi hakan yasa banyi musu ba na taso cikin wani yauki da ban san na iya shi ba na nufe shi tare da kashe da wani sexy smile.

Kafe ni yayi da ido ko kiftawa ba yayi yi har na iso gaban shi kaman zan shiga jikin shi sai na zille ina dariya nace" ga Yaya ta nan ku gaisa"

Shafa suman kan shi yayi da hannnu daya dayan hannun kuma yasa ya rike min hannu sannan ya kai duban shi ga Hajara da duk kunyan abinda ke faruwa ya rufe ta yace " babbar Yaya barka da zuwa" har da d'an risinawa kaman da gaske, cikin jin nauyi Hajara ta amsa suka gaisa duk yana rike da hannu na.

"Zo muje ki had'a min ruwan wanka wifey" yace yana kokarin jan hannu na zuwa parlor, tirjewa na fara kokarin yi tare da nuna mishi nayi bakuwa zan zauna wajan ta ya tafi kawai banyi aune ba naji ya d'aga ni cak in a bridal style yayi waje dani.

" Naji dadi sosai da nazo na same ki cikin koshin lafiya" yace yana bin ko ina na jiki na da kallo ,muna karasa fitowa parlorn na watsa mishi harara tare da kokarin sauka a jikin shi nace " Mallam kana over acting fa sauke ni dan Allah sai kace da wanda yake ganin mu a nan".

Cikin wani yanayi na sanyin jiki ya sauke ni kamin yace min wani abu na bar shi nan tsaye na shige kitchen nemawa Yaya ta abinda zata ci da rana , jiki a mace ya koma ya zauna tare da dafa kan shi tsakanin jiya da yau din nan bai san me yake damun shi he feels a different person.
[6/16, 9:22 PM] Golden Pen Writers Associ: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹

_A story about love and sacrifice._

_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_

_*From The Fantastic Writer of*_

```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```

*_And now_*

*_BA SONTA NAKE BA_*

✍ *✍ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾O̾N̾* ✍✍

https://www.facebook.com/Golden-Pen-Writers-Association-102095951667849/

*w̶̶є αr̶̶є вєαr̶̶єr̶̶'s̶̶ σf̶̶ s̶̶σ g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶*
*w̶̶є w̶̶r̶̶ít̶̶є αs̶̶s̶̶íd̶̶íσu̶̶s̶̶l̶̶ч p̶̶єr̶̶c̶̶єív̶̶є n̶̶σ p̶̶αín̶̶,*
*s̶̶σ m̶̶αg̶̶íc̶̶αl̶̶ σu̶̶r̶̶ c̶̶r̶̶єαt̶̶ív̶̶є g̶̶σl̶̶d̶̶єn̶̶ p̶̶єn̶̶* ✍ *,вєh̶̶σl̶̶d̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶.α p̶̶r̶̶σd̶̶u̶̶c̶̶t̶̶ σf̶̶ σu̶̶r̶̶ p̶̶єn̶*̶ *,s̶̶αv̶̶σu̶̶r̶̶ σu̶̶r̶̶ w̶̶σr̶̶d̶̶s̶̶, f̶̶σr̶̶ ít̶̶ w̶̶íl̶̶l̶̶* *c̶̶αu̶̶s̶̶є чσu̶̶ n̶̶σ p̶̶αín̶̶.*

*Yadda Annabi, Tsira Da Amincin Allah Su Tabbata A gareshi, Yake Kirga Tasbihinsa.*

Daga Abdullahi bn Amr, Allah ya yarda da shi, yace; Na ga Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi, yana kirga tasbihi da (yatsun) hannun damansa.

*INA MASOYAN LITATTAFAN ƘUNGIYAR GOLDEN PEN?*

*NESA TA ZO KUSA, TUNANIN RASHIN SAMUN NEXT PAGE YA ƘARE!.*

Kasance mutum na farko da zai fara karanta sabbin littattafan marubutan mu, a duk lokacin da muka yi typing. Kina/Kana iya samu, ta wannan damar ce kawai idan ka bi wannan links tare danna *LIKE* a shafin mu na Facebook zaka/zaki iya samun cigaba ko kuma ki samu duk littafin da kike buƙata namu daga farko.

Sai kun zo, kar ku manta a koda yaushe comments da sharhin ku yana ƙara mana ƙarfin gwiwa a wajen rubutu mai yawa.

*Bismillahir Rahmanir Raheem*

*43&44*

A wannan rana a nan parlourn ya yini kaman an dasa shi yana zaune sai kurb'an ruwa yake duk inda zan wuce kuwa sai yayi ta bina da ido kaman ya samu tv, ni dai ko kallo bai ishe ni ba dan yau wani tashen rashin mutunci nake ji dashi.

Sallah azahar kad'ai naga ya fita yayi a masallaci ya dawo a lokacin ni Kuma fitowa ta kenan daga kitchen hannu na d'auke da wani tray mai d'an girma da na d'aura kayan dad'i dana girkawa 'yar uwata, wuce shi nayi zuwa parlona inda na bar Hajara zaune tana kallo,nan tsakiyar parlour na ajiye na fita na had'o drinks masu sanyi a fridge na kara wucewa ta.

Ya d'an jima zaune wai ko zan dawo in kawo mishi rabon shi yaji shiru, murmushi yayi kawai tare da kad'a kai ya d'auki makullin mota ya fita ba jimawa sai gashi nan ya dawo da kaya niki-niki a hannu leda d'aya tak ya ajiye a parlorn ya wuce da sauran parlona ya same mu mun fara cin abincin muna hiran mu, ajiye kayan hannun sa yayi ya d'an kalle ni yace " pls ga kada ki manta da drugs d'in ki in kin gama cin abincin ki sha sannan ga fruits suma ki sha zaki ji dad'in bakin ki" gyad'a mishi kai kawai nayi ya juya ya fita yana waiwaye na.

"Zareefa gaskiya kinyi dacen miji nagari a wannan zamani da maza ba abinda suka iya sai wulakanta matan auren su, amma ki ga yanda yake tarairayen ki" cewar Hajara kenan, murmushi kawai nayi mata ba tere da na bata amsa ba na fara bud'e ledan fruits d'in a raina ina baki san waye shi bane har kike yabon sa.

A can main parlour kuwa Zafar zaune ya saka fried rice nd chicken daya sayo dan yaci amma ya kasa kwata-kwata bai fi spoon 3 yayi ba yaji abincin ya fita ran shi, tsaki yaja yana hararan inda muke bai san ya akayi haka ta faru ba daya saba da cin abinci na har baya iya cin wani abincin wani.

Kara kallon abincin yayi gashi dai so color full ya sha veggies amma sam bai ji wani taste ba a bakin shi,tattre su yayi ya ajiye a gefe ya sha fruits d'in daga baya duk ya kwashe su ya mikawa Baba mai gadi.

Har kusan la'asar muna tare da Hajara sannan tace zata koma amma zatayi kwana 2 a jere tana zuwa saboda akwai wani waje da Gwaggo Aisha take Aiken ta ita kuma bata son zuwa shiyasa zata rinka zuwa nan as ta tafi inda ta aike ta, ni kuwa cikin murna da jin dad'in zan samu mai taya ni hira har na kwana 2 na amsa mata da ina jiranta tazo da wuri.

Duk sauran kayan ciye-ciye da Zafar ya kawo ita na tarawa nace ta kaiwa su Ibrahim, ta amsa tana ta godiya na rako ta har bakin kofan main parlorn ta tafi.

Tana zuwa gida ta tarar da Gwaggo Aisha a tsakar gida tana jiran ta, ganin ta da manyan ledoji yasa ta fara washe baki domin taga alamun nasara a aikin bokan ta.

"Ya kika dad'e haka Hajara, kin gan ni nan tun d'azu nake zaman jiran ki" ta fad'a cikin d'aga murya yanda sauran 'yan gidan zasu ji.

Cikin kara fad'ad'a farar ta ta karaso gaban ta tare da ajiye kayan hannun ta murya kasa-kasa tace" gashi nan yace in kawo gida yana gaishe ki".

Wani irin shewa Gwaggo Aisha ta saka tana dariya tace" wannan duka yace ki kawo min lalle sirkin nawa ba wasa" murmushi kawai Hajara tayi ta shige ciki ta bar ta a nan sai bud'e su take d'aya bayan d'aya tana kara bud'a murya tana yabon kayan tare da yad'a habaici.

Dare nayi suna zaune suna hira da Gwaggo Aishan wayan ta ya fara ringing ganin number sabon saurayin ta ne yasa ta d'aga tana murmushi bayan sun gaisa yake ce mata bata ma tambayi sunan shi ba, nan itama tace ai ba sai ta tambaya ba shi ya kamata ya fad'a mata nan yace mata sunan shi Amadu.

Tashi tayi zuwa bedroom d'in su ganin Gwaggo Aisha ta ishe ta da waye ya kira ko Zafar ne? Da kai kawai ta amsa mata ta karasa shigewa daki ta barta tana ta murna.

*****************************

Da daddarem ma kin girkin girka komai nayi na kwanta Ina kallon wani series da nake matukar so a zee world ya shigo min da sallama na amsa mishi ciki-ciki kaman yanda shima ya min, tsaye yayi kaman me son cewa wani abu ko me neman wani abu ni dai bance mishi kala ba na mayar da hankali na kan tv.

"Ya jikin naki?" Naji muryan sa kaman daga sama.

" Na warke" na bashi amsa ba tare da na kalli inda yake ba.

Bai kara cewa komai ba ya fita nabi bayan shi da harara, a raina ina wa zai kara kula ka kaci zalin shi ko ka mishi mugunta da ka saba.
Chapter 48 · 0% Book details