Sashe 11
Ba Sonta Nake Ba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai Inna tayi sannan ta ce," babu abinci Mallam ba muyi girki ba sai...."
"Inna ki bashi nawa da kika ajiye min yaci dan ni nasha ice cream ba zan ci ba". Na katsewa Inna hanzari.
"Yauwa 'yar albarka, Allah sarki yarinya mai tausayin Baban ta" Abba yace cikin jin dad'i yana washe baki.
Inna tsuke fuska tayi tana jin kaman ta kamo ni tayi ta kirb'a sai yau ya san dasu a gidan a baya in ta aika mishi abinci kora ta yake hmmmm sai yau, ba dan taso ba ta tashi ta d'auko mishi hadaddiyar warmer sabuwa da ta sayo mana muke zuba abincin mu a ciki ta ajiye a gaban shi.
Cikin sauri Baba ya bud'e warmer, ba shiri ya lumshe ido saboda kamshi mai dad'i daya bugi hancin sa, yana bud'e ido sai da ya had'iye wani yawu ganin shinkafa da miyar kaza , ko ruwan wanke hannu bai nema ba ya tsoma hannu ya fara aikawa cikin sa hannu baka hannu kwarya.
Ni kuwa duk dad'i ya cika ni yau muma Baban mu ya shigo d'akin mu kaman sauran 'yan gida har yaci abincin mu tsab'anin Inna da duk zaman shi a d'akin namu ya takura ta saboda bata saba ba kuma ta san ba wai matsayin ta da yake kiran ta dashi a baya ba son ta yake bane ya canza a'a sai dan kwad'ayin abin hannun ta wanda ita kuwa ba zata so ya shiga jikin ta b sam..
Yana cikin cin abincin naje inda Inna take ajiye min juices da bobo
na d'auko mishi orange juice na ajiye a gaban shi.
"Ikon Allah shi kuma menene wannan 'yar albarka?" Ya tambaya cikin matukar farinciki.
"Lemon kwali ne Baba" na bashi amsa nima cikin jin dad'in sabon sunan da yake kira na dashi.
Balle murfin yayi ya kafa kai ya fara sha bai sauke ba sai da ya kusan shanyewa sannan ya ajiye yana tsid'e baki ya ce," wai..wai...wai.... Ikon Allah wai lemon kwali kika ce ko?" Ya kara tambaya bayan ya d'auko katon chicken breast a cikin abincin ya fara figa.
Ina dariya na amsa mishi da " eh Baba" Inna dai ko kallon mu batayi ta cika tayi fam jira kawo take ya fita tayi magani na.
Baba bai bar d'akin ba sai da ya gama cinye abincin harda lashe warmer sannan ya mike yana kallo na ya ce," 'yar albarka kada ki manta da Baban ki, ki rinka tunawa dani in kin samu kayan dad'i kinji ko?" Cikin jin dad'i na amsa mishi sannan yayiwa Inna sallama ya fita.
Yana fita muka ji muryan Gwaggo Aisha tana shewa ta ce," ahaiyye nanaye yau me nake gani jama'a kuzo ku tayani duba ko dai ido na ne yake min gizo?"
"Ba gizo idon ki yake miki ba nine nan Mallam Hassan kuma daga d'akin Bintu na fito ko kina da magana ne?" Baba ya b'ata amsa yana cire nama daya mak'ale mishi a hakori.
A yanzu yana dai-dai daya b'ata da kowa a gidan in dai akan Bintu ne, haba yaushe rabon daya ci kaza ko shinkafa da miya ita in banda aukin shinkafa da wake me take bawa mutum ko naira d'ari ko d'ari biyu amma ga Bintu kwanaki bashin dubu biyu ta biya mishi a take,gaskiya dole ne ma ya mak'ale a wajan ta.
Yana gama bata amsa yasa kai ya fice abinsa ya bar Gwaggo Aisha da ihu tana," aikin banza aikin wofi wato ta nan kika biyo dad'in abin kowa ya san dai sunan ki a gidan nan ba sonta nake ba, shine dai sunan ki".
Inna tana jinta bata tanka ba saima kamo ni da tayi zata daka akan abinda nayi Allah ya taimake ni ya jefo Maman Dije ta kwace ni tare da nuna mata kada tayi haka saboda koma ya yake ba'a tab'a canzawa tuwo suna ba, duk abinda zasuyi suyi tsakanin su amma kada ta sakani a ciki.
Da wannan nasihan Maman Dije na tsira ba'a jibge ni ba.
Tun daga wannan rana Baba ya maida d'akin mu wajan hiran sa duk da yanda Inna take tsuke fuska baya damun sa in dai zai shigo ya samu abin tab'awa, ni kuwa duk dad'i ya cika ni yanzu Baba na shigo mana kuma ya daina hantara ta saima sabon suna daya lika min wai 'yar albarka.
Inna kuwa duk rawan kafar da yake yi akan mu ba wani burge ta yake ba domin ta san dan abinda yake samu shiyasa har yake ihu da 'yar lelen shi wato Gwaggo Aisha, ta ina ma zata manta abubuwa da yayi mata na shekara da shekaru dad'in bakin sa na lokaci kad'an d'in nan ba zai tab'a goge tabo dake cikin zuciyar ta ba.
Abin takaici ma har yau bai tab'a yunkurin tambayan ina Inna ta ya take samun kud'i da har take wayan nan abubuwan ba, kuma wani ikon Allah bai tab'a had'uwa da Abdulbasit ba dan haka bai san daga inda muke samun kud'i ba.
Tsakani na da Abdulbasit kuwa wani shakuwa ne na ban mamaki ya shiga tsakanin mu ada yana kaiwa sati ko fiye kamin yazo gidan mu amma yanzu baya iyawa dan ana kwana 2 zai zo mu sha hiran mu yana sai dai mafi yawan hiran tsokana ta yake wai ya ganni da saurayi da sauran su ni kuwa insha kuka na in more daga baya kuma mu shirya abin mu ya tafi.
Rayuwa yanzu tayi mana dad'i sosai dan bamu da maraba da masu kud'i tunda duk abinda masu kud'in suke ci suke sha suke sakawa muma haka ni da Inna ta duk mun murmure harda d'an kumatu mukayi.
Gwaggo Aisha da Inna Asabe kuwa duk hankalin su a tashe yake ba ma kaman Gwaggo Aisha dan kiri-kiri ta rasa matsayin ta ya koma kan Inna tayi duk abubuwa da zatayi amma duk a banza dan gwara da yana d'an sauraron ta amma tunda ya shigo d'akin mu ranan ya tarar da Inna tana kirga kud'i sun kai kusan dubu hamsin a hannun ta tun daga wannan rana ya kara haukacewa kasancewar ko shi da yake d'a namiji bai tab'a rike irin wannan kud'i ba.
Ganin duk ya rikice yasa Inna ta bashi dubu biyar a ciki a ranan kaman yayi mata sujada haka ya kwantar da murya yana mata godiya.
Daga wannan ranan mulkin gidan ya koma hannun Inna ta dan Baban mu ya zama kaman wani bawan ta duk abinda tace baya musu balle ya karyata ta cin mutuncin kowa yake a gidan saboda mu.
.
Mun koma makaranta mun shiga jss 2 cikin farincikin sabon uniform da Abdulbasit ya d'inka min dasu sabon jaka da sauran kayan amfani na makaranta, tsab dani na koma kowa ma sai sha'awa ta yake masu tsokana ta da kuma yanzu sune suke bi na wai suna sona da k'awance.
Na biye musu nima duk abinda na kai makaranta na kayan kwalama ina basu ko in sun ce in saya musu wani abu bana kyashin saya musu amma fa ba wai na manta abinda suka min bane sai dai na barwa Allah ne.
A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu muna jss 3 komai na alamun girman 'ya mace duk sun bayyana a tare da ni kyawu na ya fito sosai, shakuwa da yake tsanani na da Yaya na ya rikid'e ya koma zallan soyayya, dan sosai yake nuna min abinda ke cikin zuciyar shi tun ina had'awa da kuruciya har ni da kaina na fahimci na fad'a son Yaya na sosai kullum zai zo mu sha hiran mu da kyar zai daure ya tafi, daya ga hakan ma ba zai wadatar dashi ba ya sayo min dankareriyar waya ta wanda kullum ya kasance muna cikin communicating.
Wannan waya da Yaya na ya saya min gaba d'aya ya d'agawa Gwaggo Aisha da Hajara hankali harda Jameela wacce take ganin sa'anni muke da ita.
Ban san ko ta yaya abin ya kasance ba sai dai gani nayi itama wani mai mota yana zuwa wajan ta hira, daga ranan da mai motan ya fara zuwa a ranan ta sallami duk sauran samarin ta dan dukan su babu mai mota a cikin su dama lallab'a su take.
Tun daga wannan rana su Gwaggo Aisha suka fara d'aga murya a gidan komin kankantar abinda ya kawo mata sai an fito tsakar gida ana maimaitawa ana yi mana iyayi a gida, mu dai ko a jikin mu amma Inna Asabe duk ta damu dan tana da 'ya Hasiya kuma sa'ar Hajara ce, Allah ya jarabce ta da bakin jini babu wanda ya tab'a zuwa wajan ta .
Yawanci Yaya na in zai zo wajena sai bayan la'asar yake zuwa kuma Baba baya zuwa gida a wannan lokacin amma a yau bayan azahar yazo saboda wai zaiyi tafiya amma ba dad'ewa zaiyi ba gobe zai dawo, muna cikin hira na hango Baba ya nufo gida sai gyara binjimar jikin sa yake, dum naji zuciya ta ta buga dan daga ni har Inna ta bama son Baba ya had'u da yaya na dan zai iya tafka abin kunya dan shi ba damuwar shi bane.
Motan yabi da ido ya gan mu tsaye a gefe kaina a kasa dan bana son yayi min magana amma banyi nasara ba.
Yana gani na ya nufo inda muke cikin sauri yana," a'a 'yar albarka kece anan?"
Kamin in bashi amsa Yaya na ya durkusa har kasa ya fara gaishe shi, cikin washe baki yake amsawa yana bin katuwar motan shi da kallo .
*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/17, 9:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚 🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾
"Inna ki bashi nawa da kika ajiye min yaci dan ni nasha ice cream ba zan ci ba". Na katsewa Inna hanzari.
"Yauwa 'yar albarka, Allah sarki yarinya mai tausayin Baban ta" Abba yace cikin jin dad'i yana washe baki.
Inna tsuke fuska tayi tana jin kaman ta kamo ni tayi ta kirb'a sai yau ya san dasu a gidan a baya in ta aika mishi abinci kora ta yake hmmmm sai yau, ba dan taso ba ta tashi ta d'auko mishi hadaddiyar warmer sabuwa da ta sayo mana muke zuba abincin mu a ciki ta ajiye a gaban shi.
Cikin sauri Baba ya bud'e warmer, ba shiri ya lumshe ido saboda kamshi mai dad'i daya bugi hancin sa, yana bud'e ido sai da ya had'iye wani yawu ganin shinkafa da miyar kaza , ko ruwan wanke hannu bai nema ba ya tsoma hannu ya fara aikawa cikin sa hannu baka hannu kwarya.
Ni kuwa duk dad'i ya cika ni yau muma Baban mu ya shigo d'akin mu kaman sauran 'yan gida har yaci abincin mu tsab'anin Inna da duk zaman shi a d'akin namu ya takura ta saboda bata saba ba kuma ta san ba wai matsayin ta da yake kiran ta dashi a baya ba son ta yake bane ya canza a'a sai dan kwad'ayin abin hannun ta wanda ita kuwa ba zata so ya shiga jikin ta b sam..
Yana cikin cin abincin naje inda Inna take ajiye min juices da bobo
na d'auko mishi orange juice na ajiye a gaban shi.
"Ikon Allah shi kuma menene wannan 'yar albarka?" Ya tambaya cikin matukar farinciki.
"Lemon kwali ne Baba" na bashi amsa nima cikin jin dad'in sabon sunan da yake kira na dashi.
Balle murfin yayi ya kafa kai ya fara sha bai sauke ba sai da ya kusan shanyewa sannan ya ajiye yana tsid'e baki ya ce," wai..wai...wai.... Ikon Allah wai lemon kwali kika ce ko?" Ya kara tambaya bayan ya d'auko katon chicken breast a cikin abincin ya fara figa.
Ina dariya na amsa mishi da " eh Baba" Inna dai ko kallon mu batayi ta cika tayi fam jira kawo take ya fita tayi magani na.
Baba bai bar d'akin ba sai da ya gama cinye abincin harda lashe warmer sannan ya mike yana kallo na ya ce," 'yar albarka kada ki manta da Baban ki, ki rinka tunawa dani in kin samu kayan dad'i kinji ko?" Cikin jin dad'i na amsa mishi sannan yayiwa Inna sallama ya fita.
Yana fita muka ji muryan Gwaggo Aisha tana shewa ta ce," ahaiyye nanaye yau me nake gani jama'a kuzo ku tayani duba ko dai ido na ne yake min gizo?"
"Ba gizo idon ki yake miki ba nine nan Mallam Hassan kuma daga d'akin Bintu na fito ko kina da magana ne?" Baba ya b'ata amsa yana cire nama daya mak'ale mishi a hakori.
A yanzu yana dai-dai daya b'ata da kowa a gidan in dai akan Bintu ne, haba yaushe rabon daya ci kaza ko shinkafa da miya ita in banda aukin shinkafa da wake me take bawa mutum ko naira d'ari ko d'ari biyu amma ga Bintu kwanaki bashin dubu biyu ta biya mishi a take,gaskiya dole ne ma ya mak'ale a wajan ta.
Yana gama bata amsa yasa kai ya fice abinsa ya bar Gwaggo Aisha da ihu tana," aikin banza aikin wofi wato ta nan kika biyo dad'in abin kowa ya san dai sunan ki a gidan nan ba sonta nake ba, shine dai sunan ki".
Inna tana jinta bata tanka ba saima kamo ni da tayi zata daka akan abinda nayi Allah ya taimake ni ya jefo Maman Dije ta kwace ni tare da nuna mata kada tayi haka saboda koma ya yake ba'a tab'a canzawa tuwo suna ba, duk abinda zasuyi suyi tsakanin su amma kada ta sakani a ciki.
Da wannan nasihan Maman Dije na tsira ba'a jibge ni ba.
Tun daga wannan rana Baba ya maida d'akin mu wajan hiran sa duk da yanda Inna take tsuke fuska baya damun sa in dai zai shigo ya samu abin tab'awa, ni kuwa duk dad'i ya cika ni yanzu Baba na shigo mana kuma ya daina hantara ta saima sabon suna daya lika min wai 'yar albarka.
Inna kuwa duk rawan kafar da yake yi akan mu ba wani burge ta yake ba domin ta san dan abinda yake samu shiyasa har yake ihu da 'yar lelen shi wato Gwaggo Aisha, ta ina ma zata manta abubuwa da yayi mata na shekara da shekaru dad'in bakin sa na lokaci kad'an d'in nan ba zai tab'a goge tabo dake cikin zuciyar ta ba.
Abin takaici ma har yau bai tab'a yunkurin tambayan ina Inna ta ya take samun kud'i da har take wayan nan abubuwan ba, kuma wani ikon Allah bai tab'a had'uwa da Abdulbasit ba dan haka bai san daga inda muke samun kud'i ba.
Tsakani na da Abdulbasit kuwa wani shakuwa ne na ban mamaki ya shiga tsakanin mu ada yana kaiwa sati ko fiye kamin yazo gidan mu amma yanzu baya iyawa dan ana kwana 2 zai zo mu sha hiran mu yana sai dai mafi yawan hiran tsokana ta yake wai ya ganni da saurayi da sauran su ni kuwa insha kuka na in more daga baya kuma mu shirya abin mu ya tafi.
Rayuwa yanzu tayi mana dad'i sosai dan bamu da maraba da masu kud'i tunda duk abinda masu kud'in suke ci suke sha suke sakawa muma haka ni da Inna ta duk mun murmure harda d'an kumatu mukayi.
Gwaggo Aisha da Inna Asabe kuwa duk hankalin su a tashe yake ba ma kaman Gwaggo Aisha dan kiri-kiri ta rasa matsayin ta ya koma kan Inna tayi duk abubuwa da zatayi amma duk a banza dan gwara da yana d'an sauraron ta amma tunda ya shigo d'akin mu ranan ya tarar da Inna tana kirga kud'i sun kai kusan dubu hamsin a hannun ta tun daga wannan rana ya kara haukacewa kasancewar ko shi da yake d'a namiji bai tab'a rike irin wannan kud'i ba.
Ganin duk ya rikice yasa Inna ta bashi dubu biyar a ciki a ranan kaman yayi mata sujada haka ya kwantar da murya yana mata godiya.
Daga wannan ranan mulkin gidan ya koma hannun Inna ta dan Baban mu ya zama kaman wani bawan ta duk abinda tace baya musu balle ya karyata ta cin mutuncin kowa yake a gidan saboda mu.
.
Mun koma makaranta mun shiga jss 2 cikin farincikin sabon uniform da Abdulbasit ya d'inka min dasu sabon jaka da sauran kayan amfani na makaranta, tsab dani na koma kowa ma sai sha'awa ta yake masu tsokana ta da kuma yanzu sune suke bi na wai suna sona da k'awance.
Na biye musu nima duk abinda na kai makaranta na kayan kwalama ina basu ko in sun ce in saya musu wani abu bana kyashin saya musu amma fa ba wai na manta abinda suka min bane sai dai na barwa Allah ne.
A kwana a tashi ba wuya a wajan Allah dan yanzu muna jss 3 komai na alamun girman 'ya mace duk sun bayyana a tare da ni kyawu na ya fito sosai, shakuwa da yake tsanani na da Yaya na ya rikid'e ya koma zallan soyayya, dan sosai yake nuna min abinda ke cikin zuciyar shi tun ina had'awa da kuruciya har ni da kaina na fahimci na fad'a son Yaya na sosai kullum zai zo mu sha hiran mu da kyar zai daure ya tafi, daya ga hakan ma ba zai wadatar dashi ba ya sayo min dankareriyar waya ta wanda kullum ya kasance muna cikin communicating.
Wannan waya da Yaya na ya saya min gaba d'aya ya d'agawa Gwaggo Aisha da Hajara hankali harda Jameela wacce take ganin sa'anni muke da ita.
Ban san ko ta yaya abin ya kasance ba sai dai gani nayi itama wani mai mota yana zuwa wajan ta hira, daga ranan da mai motan ya fara zuwa a ranan ta sallami duk sauran samarin ta dan dukan su babu mai mota a cikin su dama lallab'a su take.
Tun daga wannan rana su Gwaggo Aisha suka fara d'aga murya a gidan komin kankantar abinda ya kawo mata sai an fito tsakar gida ana maimaitawa ana yi mana iyayi a gida, mu dai ko a jikin mu amma Inna Asabe duk ta damu dan tana da 'ya Hasiya kuma sa'ar Hajara ce, Allah ya jarabce ta da bakin jini babu wanda ya tab'a zuwa wajan ta .
Yawanci Yaya na in zai zo wajena sai bayan la'asar yake zuwa kuma Baba baya zuwa gida a wannan lokacin amma a yau bayan azahar yazo saboda wai zaiyi tafiya amma ba dad'ewa zaiyi ba gobe zai dawo, muna cikin hira na hango Baba ya nufo gida sai gyara binjimar jikin sa yake, dum naji zuciya ta ta buga dan daga ni har Inna ta bama son Baba ya had'u da yaya na dan zai iya tafka abin kunya dan shi ba damuwar shi bane.
Motan yabi da ido ya gan mu tsaye a gefe kaina a kasa dan bana son yayi min magana amma banyi nasara ba.
Yana gani na ya nufo inda muke cikin sauri yana," a'a 'yar albarka kece anan?"
Kamin in bashi amsa Yaya na ya durkusa har kasa ya fara gaishe shi, cikin washe baki yake amsawa yana bin katuwar motan shi da kallo .
*Albishirinku mata masu son kamshi da gyara ga dama ta samu zamu fara classes na koyar da turaren wuta kala-kala humra shima in different colors dilke gyaran amarya man gashi nd lots more kada ko yarda a baki labarai akan 300 kacal zaki zama pro na kan ki, duk mai bukata ta tuntubi wannan no 08172724281 sai mun ji ku*.
[9/17, 9:01 PM] Ummee Yusuf: 🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚 🦚🌹
🦚
*BA SONTA NAkE BA*
🦚
🦚🌹
🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹
🦚🌹🦚🌹🦚🌹🦚🌹
_A story about love and sacrifice._
_Written by_ *UMMEE YUSUF*
_(Maman Yusuf)_
_*From The Fantastic Writer of*_
```FARHAT```
```KAMACE```
```UKUBAR KISHIYATA```
```UMMU~SALMA```
```UWANI```
*_And now_*
*_BA SONTA NAKE BA_*
*âœâœ G̾O̾L̾D̾E̾N̾ P̾E̾N̾ W̾R̾I̾T̾E̾R̾S̾ A̾S̾S̾O̾C̾I̾A̾T̾I̾