← Book details Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 93

Sashe 48

Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon Oummu Zieyaderh tayi, idanu Oummu ta mata alaman karta cire mayafinta, aikuwa saita yi burus da maganan Inna Ma'u. Wani irin malolon baƙin cikine ya cika zuciyar Inna Ma'u, don sarai ta ga lokacin da Oummu tayiwa Zieyaderh'n idanu.    Aranta tace "Wallahi ko zaku mutune saina laƙaba muku wani sharrin dasai kunbani kuɗi ƴan iska"     

Babu jimawa Malam Garba ya dawo hannunsa ɗauke da ƙwaryan nono, babu wani ƙyama haka Oummu ta zage tasha nonon daganan tace da Malam Garba idan ba damuwa tanaso tayi magana dashi.    "Magana kuma dashi kaɗai?" Inna Ma'u ta tambaya tana zare ido.  Babu wanda ya kulata saima iso da Malam Garba yayiwa Oummu zuwa soro tayanda babu wanda zaiji abun da suka tattauna, cike da fahimtan juna Oummu tayi masa bayanin duk wani abu dake tafe da ita, har acikin ransa yayarda da matar da kuma kamalanta saboda haka atake ya amincewa buƙatarta baƙaramin daɗi Oummu taji ba, nan suka tsaida magana cewar zata turo manya don atsaida magana, inda shikuma yace ko babu wasu manya ya yarda da ita ya bawa Ɗanta Almustapha Auren Ƴarsa Zieyaderh, duk lokacin da suka shirya kawai suzo ayi biki.

(uhhhh guys kushiryafa kuna da biki😝)
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
           
             *SOORAJ!!!*

    *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*
       
            *WATTPAD*
      @fatymasardauna
#romance

*This page is dedicated to you my dear @Zeety delight... heart you dear*

            *Chapter 37*

Da tsananin farinciki ɗauke akan fuskar ko wannensu Oummu da Malam Garba suka shigo cikin gidan, Inna Ma'u na ganin hakan wani ƙaton baƙinciki ya ɗarsu azuciyarta, hakanan taji ajikinta cewa hanyar ƙaruwa suka tattauna, ae kuwa nan ta ƙudura aranta cewa Oummu na tafiya sai tayi maganin Malam Garba, yadae santa ae yakuma san wacece ita.

Kallon Zieyaderh Oummu tayi fuska ɗauke da murmushi tace "Inaga ya kamata ae ace mutafi tun yanzu, kada tafiyan dare ya kamamu"   
Jin abun da Oummu tace yasanya ƙirjinta bugawa, ahankali ta ɗago idanunta tare da ɗan satan  kallon mahaifinnata, cikin rashin sa'a tasamu shiɗinma kallonta yake, da sauri tayi ƙasa da kanta, murmushi yayi tare da cewa "Bakomai kuje Zieyaderh Allah Yakiyaye hanya ya tsare, nima inanan zuwa tunda yanzu nasamu adreshin inda kuke." 
Wani irin sanyi ne Zieyaderh taji na ratsa zuciarta, sam batayi tunanin mahaifinta zai barta ta koma ba. 

"Chab amma kuwa Garba kayi banzan hali, yanzun barinta zakayi ta koma, oh wato kaidai ba ka gaji da jin zagin da mutane ke mana agarinnan ba, karka manta fa duk  akan ɓatanta sunanmu ya ɓaci,  to babu inda zataje tananan tadawo kenan!" Inna Ma'u ta faɗa amasifance, don sam bata tsammaci haka ba.

"Haba Ma'u meyasa ne bazaki sanja ba, dan Allah Kibar yarinyarnan tayi tafiyarta, tafara karatu acan birni, tsayar mata da karatunta bashida wani amfani"  Malam Garba yafaɗi haka cikin ɗan lallashi saboda yasan halin kayansa sarai ba mutumci.

Cike da kumfar baki Inna Ma'u tace "Dole kace haka mana saboda ƴar kace, ai dama ninasan banice na haifeta ba, kuma zaman birni kam wannan algungumar ƴar taka ta gama yinshi....." Bata gama rufe bakinta ba taji sauƙar wani abu me ɗan nauyi akan cinyarta,   idanu ta zaro lokaci guda tare da haɗiye maganan dake bakinta, take yanayin fuskarta ya sauya daga ɓacin rai zuwa murmushi. "To Alhamdulillah, irin wanga farare bugun can babban birni, Hajiyan Birni Allah ya ƙara arziki!" Inna Ma'u tafaɗa bakinta har kunne,   kuɗine masu yawa Oummu ta aje mata don rufe bakinta, ai kuwa lokaci guda sai ga bakinnata ya rufu .    cike da nishaɗi tace.
"To yanzu sai yaushe zaku kuma dawowa?"    yanayin yanda tayi maganan tana me ƙoƙarin cusa kuɗin cikin lalitantane yabasu daria amma sai suka gimtse, ɗauke da ɗan murmushi Oummu tace.
"Nan bada jimawa ba Insha Allah, Nangaba kaÉ—an kema nasan zaki kaimana ziyara!"

"Sosaima kuwa, kice  ziyarori ma ba iyaka ziyara kaɗai ba, don fa basau ɗaya zanzo ba!!" Inna Ma'u tafaɗa cikin jin daɗi, dama ita abun duniya shine kanta.

Har wajen mota suka rakasu,  bayan motar  Oummu ta buɗe wanda ke shaƙe da kaya, Kamalu driver tasanya ya shiga ciro kayan yana kaiwa cikin gidansu Zieyaderh, kayan abincine kala kala da kuma wata leda dake ɗauke da kayan sawa, atamfofi da shadda irin na maza, godiya kam ba irin wanda baban Zieyaderh baiyi mata ba, duk da yanuna mata cewa kayan sunyi yawa, amma saitace masa ba komai,  koda ta bashi kuɗi ƙin amsa yayi babu yanda batayi dashi ba amma haka yaƙi amsa, Inna Ma'u kuwa daɗine ya isheta, musamman ma ganin ana shigar da kayan abinci cikin gidanta.  Haka su Zieyaderh suka baro cikin ƙauyen zuciarta cike da kewan babanta.    Har bacci tayi a hanya kafun su iso, gaba ɗaya zaman mota ba daɗi ji take duk jikinta yayi mata wani iri.

Suna isa gida kowa ɗakinsa ya wuce, don gaba ɗayansu agajiye suke,  da ruwan zafi tayi wanka kana tabi lafiyar gado.

Sunday. 
Yawanci duk ranan weekend atare suke cin abinci akan dinning,  tun 8 tatashi tayi wanka,  riga da sket na 1million stones tasanya wanda suka amshi jikinta sosai, tayi kyau.  Wani ɗan madaidaicin mayafi ta sanya ta rufe jikinta, a kitchine ta samu Oummu cike da ladabi ta gaida ta,  fuska ɗauke da fari'a Oummu ta amsa mata,  yauma kamar koda yaushe itace ta shirya gaba ɗaya abincin akan dinning.   Ƙamshin turaren Almustapha daya shiga hancinta shi yasanyata ɗago da kai ta ɗan kalleshi, ƙasa tayi da kanta tare da gaidashi,   amsa mata yayi yana me jan kujera ya zauna, sosai yau ɗin tayi masa kyau acikin shigarta,  duk da cewa bai taɓa ganin kwalliya akan fuskarta ba amma gaskiya tana da kyau sosai.  

Oummu da Almustapha ne suke taɓa hira kaɗan kaɗan yayinda ita kuma take serving ɗinsu,   tunaninsa ne kwance aƙasan zuciyartaz hakanan taji wani iri da bataga ya fito ba, tunaninta ne ya katse sakamakon  wani daddaɗan sanyin da taji yana ratsa jikinta, gefe guda kuma ni'imtaccen ƙamshinsa dake zautar da'ita ne yashiga cakuɗa da numfashinta. 
Sanye yake da blue crazy jeans and Blue t-shirt mai kyau da tsada ƙiran company'n D&G,  sosai yayi kyau kwarjininsa yasake bayyana, yayinda gashin kansa kuwa sai shinning yake, kujera yaja ya zauna, dakansa yayi serving kansa, wajen haɗa tea, ahankali yake sipping tea ɗin yayinda kansa ke ƙasa, yau babu waya ahannunsa amma duk da haka yi yake kamar hankalinsa baya garesu,   gaba ɗaya wajen ya ɗauki shiru,  kowa abincinsa yakeci yayinda akabar mutane biyu daga cikinsu da saƙar zancen zuci,  gaba ɗaya hankalinta yana garesa, so take ta ɗago idanunta ta kallesa amma fargaba ya hanata.
Tissue Oummu ta ɗauka ta goge bakinta tare da dubansu su dukansu, cikin nutsuwa tace  "Ina da buƙatar hankulanku  agareni dukanku!"  Almustapha ne ya fara aje cokalin dake hannunsa tare da duban Oummu, itama Zieyaderh ɗago kanta tayi ahankali tana me kallon Oummu'n, shikam ko motsawa baiyiba, kana bai kuma daina shan tea ɗinsa ba.

Gyara zama Oummu tayi tare da cewa.
"Sooraj da Almustapha inaso nayi maganannan ne agabanku saboda ko ba komai kamar yayye kuke awajenta, sannan awajenta zataji maganar  amatsayin sabuwace, saɓanin ku da kuka taɓa jinta"   ɗan numfasawa tayi kana tace..
"Zieyaderh!"

Tun kafun ta kammala maganganun nata ƙirjin zieyaderh ke bugawa, asanyaye tace.   "Na'am!"

Tashi Oummu tayi daga inda take zaune, tare da jawo wata kujera ta zauna gab da Zieyaderh'n, hannayen Zieyaderh Oummu ta kamo cike da son gamsar da ita tace.
"Haƙiƙa kowacce uwa tanaso ɗanta ko ƴarta su samu abokan zama na gari, burin kowacce uwa adunia shine ƴarta mace ta dace da mijin aure, haka ma kuma ɗanta namiji ya dace da macen aure,  tamkar ƴa haka na ɗaukeki Zieyaderh,  bazan taɓa son wani abu dazai cutar dake ba,  bazan miki dole ba, saboda kema kina da ra'ayi kamar kowa, halayyanki da kuma irin nutsuwarki yasanya naji ina kwaɗayin da ki ƙara zama acikin zuri'ata, duk da cewa munatare dake ayanzu, amma anan gaba ba lallaine mukasance tare ba, dole watarana aure zai ɗaukeki ya nesantaki damu, bazanyi baƙinciki ba idan kika samu adalin miji daga wani waje na daban, amma zanfi so ace daga cikin zuri'ata kika samu wannan adalin mijin, ba daga wani waje daban ba,  kamar yanda nace bazan miki dole ba, ba kuma umarni nake baki ba, saidai  ganin ya cancanta yasanya ni yin tunanin  haɗaki  aure da ɗana Almustapha!"

Dummmmmm tamkar ankwaɗa mata  katuwar guduma akan ƙirjinta haka taji, yayinda agefe guda kuwa  taji sauƙan kalaman Oummu acikin kunnuwanta tamkar almara, wani irin abune taji ya sarƙemata maƙoshi, take tasoma tari har  saida manya manyan  idanunta suka rikiɗe daga farare zuwa jajaye, da sauri Oummu ta ɗauko ruwa ta bata, cikin ikon Allah tanasha tarin ya ɗan lafa,  jingina bayanta tayi da jikin kujera tare dayin ƙasa da kanta, me Oummu ke faɗane? Kodai kunnuwanta ne basuji mata da kyau ba? Aure kuma da Almustapha? Waƴannan tambayoyin sune cike aranta, ganin komai take kamar ba da gaske ba.   Dafa shoulder ɗinta Oummu tayi cike da kulawa tace "Karki taɓa cutar da kanki Zieyaderh,  idan har kinaga hakan zai sa ki cutu to karki ɓoye ki sanardani, bazan taɓa miki dole ba, nayi hakanne kuma badon na cutar dake ba saidon ina kwaɗayin ganinki cikin zuri'ata, duk da nasan cewa banice na haifi Almustapha ba, amma inayi masa son da nake yiwa ɗana SOORAJ, kuma ina masa kwaɗayin zamowarki mata a garesa!!"

Hawayene suka cika idanun Zieyaderh, har takai ga sun soma sauƙa akan hannunta, wani irin bugawa zuciyarta keyi,  ita kanta batasan awani irin hali take ciki ayanzun ba, gaba ɗaya kalaman Oummu sunzama tamkar wani sinadari na bayyanar da raunin zuciyarta.
Chapter 48 · 0% Book details