← Book details Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 47 OF 93

Sashe 47

Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tun seven yagama shiryawa, wayarsa ya ɗauka tare da turawa shugaban makarantar text message, ko 4 minute ba ayiba saiga ƙiran shugaban makarantar ya shigo wayansa.  Fuska yaɗan taɓe sannan ya ɗaga wayar, bayan sun gaisa ne, Principal ɗin yace.
"Naga saƙonka amma banƙi ta taka ba, saidai bakowa muke bawa irin wannan uniform ɗin daka buƙata ba,  mukan bawa ire irenta ne yara da sukayi aure basu kammala school ɗinba, to idan zasu  ci gaba da zuwa shine muke basu, amma tunda haka ka keso babu damuwa"
Ajiyar zuciya ya sauƙe tare da cewa "Nagode, sannan kuma karka manta idan ansamu wani problem ka ƙirani, kamar yanda kaƙirani a wancan time ɗin da aka kaita hospital,  so ba matsala always zaka iya  nemana!" 
"Okay dont mention" Principal  din ya faɗa tare da aje wayan.
Shima wayartasa ya aje tare da ɗaukan cover disigner shoe ɗinsa ya shiga sanyawa, iya kyau kam yayi sa, saidai kuma amma fuskar nan ahaɗe take babu alamar fari'a akanta.  
Zaune suke su duka uku akan dinning ɗin, sanye take da kayan uniform ɗinta na riga da wando,  ahakali take tsakalan chips ɗin dake gabanta, gaba ɗaya batajin daɗin zama acikinsu don haryau ganinta take amatsayinta na bare. Gaba ɗayansu  ƙamshin turarensa ne ya cika hancinsu.    Cikin ƙasaitarsa yake tahowa hannunsa ɗauke da wata ƴar briefcase me kyau,  kujera yaja ya zauna cikin ƙasan maƙoshi yace "Barka da safiya Oummu"    murmushi tayi masa tare da cewa "Barka, hope kunyi waya da commisioner?" 
Kansa ya kaɗa mata alamar "Eh" 

Mood ɗinta ne yaɗan sauya tare da cigaba da cewa "Ya faɗa maka cewa yarannan da suka harbeka sun faɗi wanda ya turosu ko? gaskiya nikam nashiga fargaba da tsoro,  indai har akan aikinka za a iya turowa akasheka, me kenan kake tunanin zai faru anan gaba? zasu iyayin komai!" ta ƙare maganar fuskarta cike da damuwa. 

Kafun Yayi magana Almustapha yace "Nima nayi mamaki ƙwarai da akace wai MR.J.J  ne yaturo ayimaka hakan, wani irin tsananin gabane ke tsakaninka dashi ne wae? Meyake nema dakai ne,  tunfa sanda aka baka BM yakejin haushinka, gaskia yanzu kam baikamata mubarshi ba!"  ya ƙare maganar cikin yanayi naɗan ɓacin rae. 

Aje mug ɗin dake hannunsa yayi tare da cewa "Its Okay, anyi arresting ɗinshi  jiya" yana gama faɗan haka ya miƙe tare da  ɗaukan tissue ya goge bakinsa, briefcase ɗinsa ya ɗauka ya fice, duka suka bishi da kallo, hakanan yake shi koda yaushe baiso ayi magana me tsawo dashi, sai kace marar gaskiya.    

Ture plate ɗin abincin dake gabanta tayi tare da ɗaukan school bag ɗinta dake gefe ta rataya. 

Zieyaderh Oummu taƙira sunanta, "Na'am" ta amsa asanyaye.  "karki manta inkin dawo ki sameni aɗakina kinsan gobene tafiyarmu"  "To" kawai tace sannan ta juya tafice daga cikin falon, tana fitowa compound ɗin gidan shikuma motarsa na fita daga cikin gidan,  mota tashiga ranta duk ba daɗi.
Ko amakaranta yau bata wani sake ba, bayan sundawo break ne aka turo wae principal na ƙiranta, saida gabanta yafaɗi amma haka ta daure taje, wata leda ya bata wanda ke ɗauke da wasu sabbin uniform har kala uku yace mata daga yau su zatana sanyawa. Sosai tayi mamaki amma sai bata nunaba ta amsa kawai ta fice, koda taje aji suka duba kayan, sket ne irin high waist ɗinnan wanda ƙasansa yake da faɗi, sai kuma wata ƴar rigar makaranta fitted da hijab ɗinta wanda idan tasa zai ɗan sauƙo mata kaɗan.   Mamakine ya kashesu su dukansu.  Shukra ce tace "Wannan fa kayan bakowa kesawa a school ɗinnan ba, kodai kinzama house wife ne bamusani ba?"   hararanta Zieyaderh tayi tare da turo baki gaba cikin takaici tace "Ni bawata house wife ɗin dana zama!" dariya suka sanya su dukansu, daga haka sukaci gaba da hiransu, kaɗan kaɗan take sa musu baki.   Har aka tashi sukuku  haka takejin kanta, koda ta koma gida ko falo bata sauƙo ba, haka ta ƙare kwanciyarta aɗaki...  Washegari   Saturday.     Ƙarfe 8 daidai ta kammala shiryawa cikin kayan da Oummu ta bata tace tasanya, riga da sket ne na tsadaddiyar atamfar Vlisco, wacce taji ɗinki, sket ɗin irin pieces ɗinnan ne yayinda rigan takasance fitted, sosai kayan suka amshi jikinta, kasancewar atamfar kalan Maroon gareta hakan yasanya ta sanya maroon hijab ajikinta, sosai tayi kyau duk da cewa batayi wani kwalliya akan fuskarta ba,  flat shoe ɗinta ta sanya tare da  kallon kanta amadubi, ita kanta tasan tayiwa kanta kyau.      Saida suka biya ta wani super market Oummu tayi sayayya sannan suka ɗauki hanyar zuwa KD inda acan ƙauyen su Zieyaderh yake.  Ƙarfe 1 na rana daidai suka iso cikin ƙauyen nasu na Saminaka, tun daga lokacin ƙirjin Zieyaderh ke dukan uku uku,   da ƙyar take iyayiwa Kamalu driver kwatance har suka iso ƙofar wahalallen gidansu,  tun shigowarsu ƙauyen yara kebinsu yayinda manya kuwa ke bin haɗaɗɗiyar motarsu da kallo.    Shawo kwanan Malam Garba kenan hannunsa ɗauke da wani buhu, turus haka yaja ya tsaya yana me bin motar daya gani fake aƙofar gidansa da kallo.  Da sauri ya ƙarasa daidai lokacin kuma su dukansu suka fito daga cikin motar, koda zata shekara ɗari ne batanan bazai taɓa kasa gane jininsa ba, bakinsa abuɗe fuska ɗauke ɗa mamaki yake kallon Zieyaderh, itama kallonsa take lokaci guda hawaye suka wanke mata fuska, ji take kamar taje ta rungume Baban nata, amma kuma tanajin tsoro.  "Ziyada!" yaƙira sunanta muryarsa na rawa.  Kasa amsa masa tayi sai kawai ta fashe da kuka.  Shima hawayene kwance acikin idanunsa. Kamar wadda aka wurgo daga sama haka Inna Ma'u tafito daga cikin gidanta, don tuni labari yakai mata cewa wata haɗaɗɗiyar mota fa faka aƙofar gidanta.  Bakinta awangale taƙarasa gaban yarinyar da take kallonta kamar Zieyaderh, hannu tasa taɗan taɓa fuskar yarinyar dake kuka,   "Laaaaa ha'ila wallahi itace, shegiyar gari kin gama gararanbanki kindawo ko?" Inna Ma'u tafaɗa tana me ƙarewa Zieyaderh kallo, mamaki kuwa aranta kamar zai kasheta.  Ƙasa Zieyaderh tayi da kanta, Malam Garba shine wanda ya kama hannunta tare da duban Oummu dake tsaye yace.
"Hajiya kushigo daga ciki!" Babu musu Oummu ta bi bayansa yayinda yake riƙe da hannun Zieyaderh, aikuwa Inna Ma'u ma rufa musu baya tayi bayan ta tsaya ta gama ƙarewa motar da sukazo da ita kallo, harwani yawu ta haɗiya natsananin kwaɗayi dason abun duniya, musamman ma da ta hango ɗan ragowan lemun fanta dake gaban motar. 

Gudu gudu sauri sauri haka taje ta ɗauko tabarma ta shumfuɗawa Oummu baki har kunne tace "Hajiyan Birni zauna mana!"  Murmushi Oummu tayi tana me kallonta sannan ta zauna aranta tace "Kamar bayanzu tagama zagi ba"  Malam Garba da kansa ya kawo musu ruwa, ita dai Zieyaderh laɓewa tayi abayan Oummu, don har cikin ranta tana jin tsoron abun dazai biyo baya.  

Gyara zama Oummu tayi tare da ɗagawa baban Zieyaderh gaisuwa, amutumce ya amsa, kafun tasake wata magana Inna Ma'u tayi saurin cewa. "Mutanen Binni Sannu marabanki da zuwa Hajiya!"  Still murmushi Oummu  tayi tare da jinjina kanta alaman yauwa.   Batare da ta bari kowa acikinsu yace wani abuba tace "Lallaima Zieyaderh wato dakika gudu kaina kikeso na aurawa tsoho ɗan dashen? ko kuwa kina tsammanin nida ubanki muna da kuɗin da zamu biyasa abun daya kashe ne, wallahi mudai kin cucemu akan guduwarki saida duk wani ɗan abun dana mallaka ya ƙare saboda ɗan dashe cewa yayi sai mun biyasa kudin daya kashe,  kin cuceni kin cuci mahaifinki wallahi!!" Imma Ma'u tafaɗi haka tana me matse wasu munafukan hawayen ƙarya data ƙaƙalosu da ƙyar.    Sake cewa tayi "Amma Allah ne zai mana sakayya, koda yake ma ai yanzu nasan kintara kuɗi sosai ko bakomai zan fanshe asarata" tana murmushi ta ƙare maganar.   Oummu kam mamaki al'ajabi haɗi da tsoro al'amarin matar ya bata, wato dai ita ko agaban wayene bazata iya ɓoye maitanta ba.  Cikin sauri taɓuɗi baki zata sake cewa wani Abu, da sauri Malam Garba yace "Ya isa haka Ma'u, dafari ya kamatane mufara sanin ina taje bawai irin waƴannan kalaman yakamata ayi mata ba" afusace Inna Ma'u tajuya zata faɗa masa baƙar magana sai kuma tatuna da wani abu tafasa. Saita fara yaƙen ƙarya tana me ƙarewa komai dake jikin Zieyaderh kallo. 

Murmushin takaici Oummu tayi tare da kai dubanta ga Baban Zieyaderh, sannu ahankali tayi masa bayani akan cewa ɗantane ya tsinci Zieyaderh bawai yawon iskanci ta tafi ba.   Ajiyar zuciya me ƙarfi Malam Garba ya sauƙe tare dayiwa Allah godiya daya sanya ƴarsa ta faɗa hannu na gari.  Itakuwa Inna Ma'u afakaice take hararan Oummu aranta kuwa cewa tayi "Kuji ƙaryan banza, yo koma gaskiya ne wayasan abunda sukeyi dashi ɗannaki, kai banma yarda ba yanda yarinyarnan tayi ɓul ɓul da ita akwai abun da take aikatawa wata ƙilama cikine da ita"   tana gama ƙimtsa zancen zucinta tayiwa Zieyaderh ƙuri, ba inda take kallo kamar cikinta, wai adole saita gano ko cikine da ita, burinta bai wuce taga tumbinnata yaɗan taso ba ta tabbatar da zarginta.   

Godiya sosai Malam Garba ya shiga yiwa Oummu na irin riƙon amanar da tayiwa ƴarsa, don har acikin ransa yana me nadamar irin rashin kulawan daya nuna mata abaya, sannan kuma yana ƙaunar ƴarsa sosai, dan itace kaɗai jininsa aduniya, amma yazaiyi da sharri da kuma tsoron Inna Ma'u da yake, duk itace ummul aba'isin faruwar komai.   Miƙewa yayi yace zaije ya samo musu fura.   Aikuwa yana fita Inna Ma'u tace "Hajiyan birni ince dai ɗannaki daya tsinceta gidanki ya kawota ba gidansa ba?" 

Mamakine ya kama Oummu cike da mamakin tambayar tace "Mekike nufi?"  da sauri Inna Ma'u ta washe baki tare da cewa "A'a babu abun danake nufi kawai dai tambaya ne,  ke Zieyaderh cire lufayan mana kisha iska" Tafaɗa cike da zaƙuwan son ganin yanda cikar halittan Zieyaderh'n ya koma, tayi rantsuwa matuƙar taga cikin Ziryaderh yaɗan tasa to wallahi saita cucesu maƙudan kuɗaɗe.  (Chaii guys Inna Ma'u fa ta tsananta😆) 
Chapter 47 · 0% Book details