← Book details Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 1 OF 93

Sashe 1

Sooraj Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

             *SOORAJ*

    *Written By*
Phatymasardauna

*DAn dauko wannan littafi daga shafin www.hausanovels001.com.ng ku ziyarci shafin na www.hausanovels001.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from www.hausanovels001.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this email [email protected] its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__ edicated To My Life (Sardauna)*

*🌈Kainuwa Writers Association*

_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_

*https://www.facebook.com/profile.php?id=61564654192468*

             *WATTPAD*
       @fatymasardauna

*(💗SPECIAL THANKS TO HAJIYA FATIMA MOMYN NIGER💗)*

*BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM*

     
           *CHAPTER 1*

*SOORAJ*

Tsugune yake akan ƙafafunsa, kansa na kallon ƙasa, yayinda  kyawawan idanunsa suke alumshe,  jama'a ne cike awajen, sai hayaniya suke, fuskar kowa ɗauke take da  farinciki, banda wani mutum ɗaya, shima ɗin baƙin ciki  da damuwarsa basu bayyana akan fuskarsa ba, amma tabbas zuciyarsa nacikin matsanancin damuwa.

Sake matse ƴan saffa saffan  idanunsa yayi da ƙarfi, jiyake kansa na juyawa, zuciyarsa nayi masa wani irin tuƙuƙi,  sosai hayaniyar jama'an dake wajen ke hautsina masa ƙwaƙwalwa, sam shiba mutum bane mai son yawan hayaniya, aduk sanda hayaniya yayi yawa awajen da yake, to ciwon kai ne ke kamasa mai tsanani, yanzu haka shikaɗai yasan abunda yakeji, jiyake kamar ya buɗe bakinsa ya kwarara ihu, koda zaiji sauƙin abun da yakeji.

"ALHAMDULILLAH AURE YA ƊAURU YAU ASABAR AN ƊAURA AUREN SOORAJ MAI NASARA DA AMARYARSA AISHATU KABEER MUNA TAYA ANGO MURNA!!!"  abunda wani maroƙi keta faɗa kenan cikin ɗaga murya.

Wannan maganan da maroƙin keyi shiyayi sanadiyar dawo da SOORAJ dake tsugune cikin hayyacinsa,   wani yawu mai ɗaci ya haɗiya, lokaci guda idanunsa suka rikiɗe suka zama jajaye, ƙoƙarin tashi tsaye yasomayi. Da sauri wani kyakkywan matashi dake gefensa yariƙe hanunsa, cikin murya ƙasa ƙasa yace "Please SOORAJ karkayi haka mana, acikin jama'a fa muke, kuma kasan tunda mukazo nan idanun jama'a akan mu yake"

Tsuka wanda aka ƙira da Sooraj yayi, tare da fusge hanunsa daga riƙon da wannan ɗin yayi masa, kallonsa yamayar ga Abbansa, karab idanunsu suka sauƙa akan najuna, da sauri Sooraj yayi ƙasa da kansa. 

A hankali Tururuwan jama'ar da suka taru a ƙofar gidan Alhaji Kabeer suka soma raguwa, kowa na ƙoƙarin kama gabansa,    ganin haka yasa Sooraj miƙewa tsaye yasoma nufar inda motarsa take, ko ɗaga kansa baiyiba balle har wasu daga cikin mutanen da sukayi ragowa su fahimci wani irin yanayi yake ciki.   Hanunsa yaɗaura akan murfin motar zai buɗe, yaji muryar  MAS'UD ta daki dodon kunnensa.

"Inazakaje?" abunda Mas'ud yatambaya kenan.

Juyowa Sooraj yayi ya watsawa Mas'ud harara, ransa amatuƙar ɓace yake, wani irin haushin Mas'ud ɗin yakeji, gani yake komai daya faru hadda sa hanun Mas'ud ɗin aciki,  takaici ne yasake turnuƙe zuciyarsa,  sai kawai yasaki tsuka yabuɗe motarsa yashige, Mas'ud na ƙoƙarin zagayawa gefen mai zaman banza yashiga, Sooraj yayiwa motar key, aguje yafigeta haɗe da turbuɗawa Mas'ud dakuma sauran jama'an dake kusa dasu ƙura.  Hakan yasa kowa yabisa da kallo, ciki kuwa hadda Abbansa dake can gefe suna ganawa da Baban Amarya.

Sheshsheƙan kuka ne ketashi acikin ɗan madaidaicin ɗakin, wata yarinyace rakuɓe ajikin bango, ta takure kanta waje ɗaya, daga yanda take sauƙe ajiyar zuciya akai akai zai tabbatar maka da cewa kuka taci ta ƙoshi son ranta,   idanunta da suka kaɗa sukai jajur ta buɗe haɗe da kai kallonta sama.   "YA ALLAH!" abun da ta ambata kenan cikin wata irin raunanniyar murya, dake cikin halin matsanancin naiman taimako,   tabbas ta yarda cewa idan Ƴa Mace tarasa Uwa to tarasa babban gata aduniya, Uwa itace komai itace ginshiƙin rayuwa, kamar yanda ruwa keda matuƙar amfani aduniya, haka uwa take awajen kowani ƴa/ɗa, ayanda take da ƙananun shekaru, tunaninta da hankalinta basukai ɗaukar wasu matsalolinba, amma saboda halin rayuwa duk tazama wani iri, rayuwarta duhu ne, rayuwarta ƙunci ne, HASKE take nema akoda yaushe, da fata dakuma burin wani wanda zai taimaka mata.

"Dan Ubanki wai maikikeyi acikin ɗakinnan ne? baƙar munafuƙa, Allah dai yayi wadaranki ZIYADA natsani waƴannan halayyartaki, muguwa mai baƙar zuciya, zaki fitone kosai nashigo cikin ɗakin nayi ƙasa ƙasa dake!?"   faɗan wata mata dake tsaye abakin ƙofar ɗakin da yarinyar ke ciki, matar tacika fam sai jijjiga ƙugu take.

Jinmuryan Inna Ma'u acikin dodon kunnuwanta baƙaramin tsoritata yayiba, jikinta na rawa tanufi hanyar fita daga ɗakin.

Tana fitowa Inna Ma'u ta bita da wani irin kallo. 
  "Wallahi natsaneki Ziyada, natsani koda jin sunanki ne, adole nake rayuwa dake acikin gidannan, keda uwarki kun riga da kunzamemin JARABA, ƴan iska masu fararen fuska!" Inna Ma'u tafaɗi haka cike da takaicin Ziyada.

Itadai Yarinyar da ake ƙira da sunan ZIYADA shiru tayi tare da sunne kanta ƙasa,  ƙirjinta kuwa jitake kamar zaiyo tsalle yafito waje sarai tasan wacece Inna Ma'u, yanzu zata kuma sake jibganta fiye da wanda tayi mata ɗazu.  

"Ungo wannan naira ishirin ɗin kije maza ki ɗauko min niƙa na, kuma wallahi idan kika sake baki dawo da wuri ba, yau saina ƙona wannan ɗan iskan fuskan naki, mai zubin mayu"  Inna Ma'u tafaɗi haka tana mai sanya hanunta ta  mangare Ziyada harsai dakanta ya bugu da bango,  sosai taji zafin bugewa dakuma mangareta da Inna Ma'u tayi, amma babu halin tayi kuka, naira ishirin ɗin ta amsa, cikin yanayinta mai sanyi tanufi hanyar ficewa daga gidan.
Tana ficewa Inna Ma'u tayi ƙwafa haɗe da cewa.
"Wallahi bazaki ƙara min cikakken sati biyu agidannan ba, ko kasheki ne ma gwamma nayi na huta, komai na mayyar uwarki kin kwashe"....

Gudu sosai yake tsalawa akan babban titin, saida yayi tafiya mai nisa kafun yayi parking motar agefen titi, hanunsa yasanya ya bugi steering motar, tare da furzar da iska daga bakinsa,  wata drawer dake jikin motar yajawo haɗe da ciro goran ruwa, ɓalle murfin goran yayi haɗe da kafa goran abakinsa, saida yasha ruwan fiye da rabin goran kafun ya ɗauke bakin goran daga kan nasa bakin,   numfashi yake fitarwa ahankali, jiyayi ƙirjinsa yayi masa nauyi,   ɗaga kansa yayi ya kalli madubin dake cikin motar, da sauri ya kauda kansa gefe, wani irin tsananin tausayin kansa ne ya kamasa, jiyayi zuciyarsa tayi wani irin karyewa,    kifa kansa yayi ajikin steering motar, baisan yazaiyi da rayuwarsa ba, baikuma san taya zai fahimtar da iyayensa lalura da damuwarsa ba, akodayaushe su kansu kawai suka sani, koda sau ɗayane basu bashi dama yasanar dasu matsalarsa ba, ako da yaushe basu da wata magana saita Aure, burinsu ɗaya shine yayi aure, baruwansu su basu wani damu da sanin shiɗin yayakeba,   ɗago kansa yayi daga jikin steering motar, idanunsa ne suka sakeyin ja, kamar anwatsamusu garin barkono,   bayajin cewa zai iya zama da kowace mace aduniyarnan, yanaji ajikinsa cewa shi ba'ayisa don yayi aure ba,  rayuwarsa cike take da DUHU baisan wani HASKE ba,   "Sai yaushene zasu fahimci hakan?" yatambayi kansa.  Shiru yayi naɗan wasu mintuna kafun yatada motarsa, yanzu kam ahankali yake tuƙin motar bakamar ɗazu ba, saidai kuma zuciyarsa cike take da tarin tunani kala kala lallai dolene zaiyi abun da ya saba, duk da yasan hakan ba daidai bane kuma ALLAH Ma bayaso, amma baida wani zaɓi da ya wuce haka...

*(Sunan labarinnan SOORAJ shima ƙirƙiransa nayi kamar yanda na ƙirƙiri sauran, kamar yanda kukasani labarina ina ginashine akan mutum biyu, to wannan labarin ma hakanne, domin akan SOORAJ da kuma ZIYADA na ginashi, kamar yanda nagina SHU'UMIN NAMIJI akan ZAID da ZAHRAH,  nakan tsayawa nayi komaina akan daidai, ina iyaka ƙoƙarina wajen ganin nabaku nishaɗi, nasamu ƙalubale sosai akan Labarin dana gama wato SHU'UMIN NAMIJI duk da nasan matakin nasara yana tarene da ƙalubale, amma wasu sunta faɗamin maganganu son ransu so please kuna kiyayewa, bakowacce magana yakamata ace wasunku na furtawa ba, karku manta magana mai daɗi sadaka ce.)*

*VOTE and COMMENT yawan vote da comment yawan typing...😝*     *Friday/13 March/2020*
    
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*SOORAJ*

   *Written By*
Phatymasardauna

*Dedicated To My Life (Sardauna)*

*🌈Kainuwa Writers Association*

_{United we stand and succeed; Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}_

https://www.facebook.com/profile.php?id=61564654192468

*WATTPAD*
@fatymasardauna

*CHAPTER 2*
Chapter 1 · 0% Book details