← Book details Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 90 OF 92

Sashe 90

Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ae sai kiyi karatu da kyau da kyau ni dai nayi nan."🏃

Kallon Deejarh Afeefah tayi ganin kamar ba ita ba, duk ta nutsu, a Hankali ta kira sunan ta.

"Deejarh."

"Na'am Balarabiyar India."

Ita ma ta amsa, Murmushi tayi sannan ta ce
"Karfa kice zaki sakawa kanki damuwa, domin kuwa da haka aka fara gaba É—aya, ba kanki fa rau ba."

Deejarth ta ce "Amma Balarabiyar India lokacin da kika fara yi, ya kikayi sannan kuma ya kikaji ne dan Allah?."

Deejarh tayi ma Afeefah tambayar tana dariya.

Sai da tayi tambayar kuma tayi saurin rufe baki, mana kallon Amma, dariya Afeefah tayi ta ce

"Ae indai Amma ce batama san kinayi ba, saboda haka saki jikin ki mutumiyar."

Washe baki Deejarh tayi jin abin da Afeefah ta ce sannan ta kuma cewa

"Ya kikaji ke a lokacin kuma kina ina ne?."

Wani murmushin tuno baya Afeefah tayi tana lumshe ido ta ce

"A Lokacin wai. Eh toh a Lokacin muna ƙasar Jamus ne, ni da Zaynerb da kuma Daddyn.
Ae deejarth ina faɗa miki bazan taɓa mantawa da lokacin ba, tsawon rayuwata, wato dai abin da ya faru shi ne.

Wata Ranar Monday na dawo daga school goye da Backpack ɗita, na fito daga cikin Bus na makarantar mu, wacca ta saukeni a ƙofar gate na gidan mu.
Kamar ance na kalla ƙasa, a lokacin kawai na tsinci kaina da durƙusawa ina kallon white socks dake ƙafafuna, aikuwa me zan gani?.👺
Nan fah naga wani abu kamar jini, kamar manja yana ɗigowa duk yabi ya ɓatamin safa ta, ina faɗa miki bansan Lokacin dana rintima a guje ba, ko tsayawa kula Baturen mai gadi, banyi ba, tunda Allah ya bani sa'a na shiga cikin gidan na dangana da Palo, aikuwa anan na sama Daddy yana duba wasu bayanai cikin laptop. Yayin da Zaynerb take daga can gefe tana Assignment cikin littafan ta na school.
Ae Tunda na shigo palon a guje ban tsaya komai ba. Nayi fatali da wannan laptop wacca Daddy yake aiki ciki. Ban tsaya bah, nanfa nan na shiga birgima ina faɗin shikenan kwanana ya ƙare zan mutu nima wajen Haihuwa tunda Jini yana fito min, shikenan nayi ciki a taimake ni.🙈
A lokacin Zaynerb da ta fahimci komai, in banda dariya babu abin da take min. Yayin da shi kuma Daddy kallona kawai Ya tsayi yi, saida kyar aka samu nayi shiru da kyar da ban baki, sannan ne fa, Daddy da Zaynerb suka min bayanin komai, domin kuwa violence highly highly da nake ciki bai bari na fahimci komai ba, duk da dai lokacin ba wani yawau ne dani ba sosai..."🤣

Tunda Afeefah ta fara zuba zance babu abin da Deejarh da Hameeda dake saman 3sieter suke yi banda dariya, Deejarh harda Birgima a ƙasa tana riƙe ciki saboda mugun dariya. Yayin da Hameeda kuwa sai da ta faɗo daga saman 3sieter da take kwance tsaban dariyar ƙeta.

Shiru Afeefah tayi tana kallon yadda suke dariya babu ƙaƙƙautawa, ita ma kawai saita fara dariyar cike da Nishaɗi.😅🤣😂

Su na cikin Haka sai ga Lailah, Zaynerb, Haleesat, Nainarh, Nailah, da gaba É—aya Yaran Uncle Yusuf da kuma Haseeya da Mah'eesha Yaran Uncle sagir suma sun shishshigo gaba É—ayan su, gaisar da granny tasu suka fara yi.

Gaba ɗaya tsayawa suka yi suna kallon yadda su Hameeda suke ɓaɓɓaka dariya cike da kamar zararru, yayin da Amma ta zuba musu ido tana kallon ikon Allah.

"Ikon Allah sai Look, toh mu dugu ko kuwa mu tsaya?, domin naga kamar Babu Lafiya anan fa."
Cewar Yasira tana zare idanu.

Ido cike taf da qwalla saboda tsaban dariya Hameeda ta kalle su cikin É—an dariya take faÉ—in

"Please ku tsaya, ku zazzauna."

"Ah taya ya zamu zauna bayan kuma kuna dariya sai kace waɗanda suka sama taɓin kwakwalwa. Ni tafiya ma zanyi dama nazo nayi ma Amma sallama ne." cewar Nailah tana shirin fita.

Ganin Haka Yasa duk suka yi tsit Afeefah ta ce
"Please Auntie Nailah zoki zauna, ae mun gama dariyar, jin Haka yasa gaba ɗaya Ƴan matan suka zazzauna a tsakiyar palon, gaba ɗaya suka gagaisa da Amma ɗin tasu sannan.

Lailah ta ce
"Mu fah har Yanzu Bamu ji abin da Yasa kuke wannan dariyar da muka shigo muka samu kuna yi ba, sai kace waÉ—anda suka shaqa Laughing gas."

Hameeda da dariyar bai ishe ta ba take faÉ—in

"Kedai Lailah bari kawai. Wani Labari mukaji wanda ya sakamu nishaÉ—i."

Wannan kuma wani Labari ne haka, a gaskiya muma a bamu Musha, Zaynerb ta faÉ—a tana gyara zamanta saman tattausar carpet na Palon.

Hameeda ta ce
"Ae kinma san Labarin, sai dai kuwa idan kin manta."

"Mu dai bamu sani ba, saboda haka a bamu musha."

Wannan karon Yasira ta kuma maganar.

Satar kallon Amma Hameeda tayi sai taga hankalin ta baya kansu, saboda haka kallon su ita ma tayi cikin Dariya ta ce
"Dama kawai Afeefah ta bamu labarin first Period nata fa."

Aikuwa jin abin da ta faÉ—a gaba É—aya suka gyara zama sunji gossip.

Yasmin ta ce
"Please Auntie Hameeda bamu Labarin daga ji Abin zai bada jitta highly higher highest ma."

Aikuwa nan bada ɓata lokaci ba, ita ma Hameeda da take sarkin surutu obaa, ta basu labarin da Afeefah ta basu wurin da tayi mistake Afeefah ta gyara ma ta, babu ko kunya.

Habba ae nan gaba ɗaya ƴan matan wurin suka kwashe da dariya. 😅🤣😂

Mah'eesha ta ce, Bayan sunyi shiru.

"Allah sarki Rayuwa, Auntie Hameeda da kika bada wannan Labari sai naji na tuna Baya, lokacin muna Boarding school nima haka nayi fama, first period nawa lokacin yazo min ana cikin tsakiyar Assembly, ae lokacin naci wuya ba kaɗan ba, abin ku da babu yawo sosai. Haka na dingi kuka, sai yanzu da naji wannan Labari sai naji na tuna Baya, sai naji dama ace baya zata dawo, habba ae kawai Abin Ba'a magana domin kuwa Rayuwar ƙuruciya tayi wallahi, Barin ma dai ace muku school Life, habba hummm." 🔥

Mah'eesha tayi maganar tana lumshe kyawawan idanun ta. Alamar dai tayi missing Baya highly highly.

Yasira ta chafe zancen da cewa
"Ke dai Mah'eesha Bari kawai. Abin cike yake da nishaÉ—i obaa."

Habba nanfa suka buÉ—e sabuwar fira tsakanin su.
Yayin da kowa sai ya bada Labarin shirmen da ya tafka a lokacin ƙuruciya, Especially ma Lokacin suna school kuma ace J.s.s.😘

Kowa bada labari yake a cikin su cike da Nishaɗi harda Haleesat da take miskilar gaske, ae ita ma tuni ta a je miskilanci a gefe aka shiga fira da bada Labari da ita. 😛

"Kun kammala kuwa?, nace kun kammala fitsarar taku Ja'iran Yaran zamani kawai, wato Babu kunya kunzo kun sakani, ni kakarku mahaifiyar ubannin ku a tsakiya, wato kowacce taji da farar fuska, sai kace zabiya, kuna bada Labarai koh?.
Wato ga marasa kunya har Gida, zakuci ƙaniyar ku domin kuwa da Babannin ku zan haɗaku duka."🙄

Gaba ɗaya tsit shiru suka yi suna jin Yadda kakartasu take ƙare musu tsiya.

Yayin da Lailah da Yasira da kuma Mah'eesha Waɗanda sune nan Ja'iran ciki sai faman tiƙa dariya suke yi.

"Eh dariya koh? Kuyi dariya da kyau, ke Lailah ɗiyar Abubakar kar kiga Sunanki Lailah, kiyi Tunanin zanji tsoron ki, dan kina Lailah, a'a Lailah kike ba dare bah."🌚
Ke kuma, ta nuna Deejarh wacca Tayi tsuru tsuru saboda yadda taji mararta ta ɗauki ƙugi.

Na dawo kanki wato kece wacca take al'adar ko kuwa ba ke ce ba, naga kinyi tsit kina kallona?."

Tayi maganar tana kallon Deejarh.

Cike da jin raÉ—aÉ—in ciwo Deejarh ta amsa da

"Eh Ni ce,"

Amma ta ci gaba da cewa abin da nakeso dake kije ki sama Ruwan zafi a gora ki É—aura a saman cikin ki, sannan kuma ki dinga yawan shan ruwan zafi akai akai harki kammala kinji?."

Da toh kawai Deejarh ta amsa.

Miƙewa Afeefah tayi sannan ta kalla Deejarh ta ce

"Taho muje na rakaki domin ki fara tun Yanzu."

Aikuwa da sauri Deejarh ɗin ta miƙe sannan tabi bayan Afeefah suka fita.

A hanya kafin su ƙarisa ɓangaren Auntie Suwaiba ba, suna tafiya duk da ciwon da Deejarh take ji bai hanata kallon Afeefah ba, sannan ta ce

"Balarabiyar India wai dama fassarar sunan Lailah Yana Nufin Dare ne?. To ke, Kuma Menene fassarar Sunanki?."

Afeefah tana tafiya batare da ta juyo ba ta ce

"Eh Haka Lailah Yana Nufin Dare. Yayin da Afeefah kuma Yake Nufi 'TAGARI.''

"Aikuwa dai Sunan ya cancanta dake it's really deserved to you highly."

Cewar Deejarh cikin murmushi, Buɗe ƙofar palon Afeefah tayi Bayan sun ƙarisa sannan suka shiga ciki domin aiwatar da umarnin Amma ɗin.

**

Da Marece wuraren ƙarfe _-_05:00pm_-_ gaba ɗaya Ahalin Uncle Yusuf suka yi sallama da mutanen Gidan har dasu, Afeefah sannan suka tafi Airport domin komawa BORNO STATE.

Tare da Rakiyar wasu daga ƴan Gidan, Yayin da ita ma Nailah ta bisu Airport ɗin zatayi jiran awa ɗaya a Airport ɗin domin komawa Lagos Birnin da take Aure ita ma da yake akwai wata ƙawarta wacca take ma'aikaciya ce anan Airport ɗin.
Yayin da ita kuma Nainarh sai zuwa gobe idan Allah ya nufa zata bi Jirgi ita ma domin komawa ƙasar Auren ta wato Eritrea.

*ABUJA*
*NIG£RIA*

Misalin Ƙarfe Tara Na Dare _-_09:00pm_-_

Zaune yake saman ɗaya daga cikin Royal sofa's waɗanda aka ƙawata qaton palon nashi dasu.

Hannu sa kuwa tsadaddiyar wayar sa ce yana latsawa, a zahiri zaka yi tunanin tsadaddiyar wayar hannun sa yake kallo.
Yayin da kuma cikin zuciyar sa tunani yake yi shin ya kira ta ne, ko kuwa dai ya barshi kawai.😀

Haka kawai yaji yana buƙatar jin daddaɗar muryarta cikin daren nan, ko da suna Yara yafi shiri da ita sama da kowa cikin Yaran Uncle's nasa da kuma Mamy's ɗin sa.

Shiga Contacts na wayar nasa ya yi sannan ya lalubo lambarta wanda Ya yi saving da, mí afortunado polola { My lucky girlfriend} daga yakai hannu zai danna call, sai kuma ya fasa, daga yakai hannu zai danna call sai kuma fasa, Haka ya shigayi yana maimaita wa, aikuwa cikin mistakenly ya danna kira.
Chapter 90 · 0% Book details