← Book details Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 92

Sashe 61

Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallon sa tayi dai dai lokacin da shima ya juyo da kallon shi akanta, cike da tsaban takaici ta ce

"Haba My lawful yana ga ka dawo damu wannan emergency kodai wani ne aka kwantar ban sani ba?."

Tayi maganar cike da sa ran ya bata amsa ba kalar wanda take tunani ba.

Gimtse kyakyawar fuskar sa ya yi alamar ba wasa kana ya ce

"Wurin Ƴar uwanki muka zo domin tafiya da ita gida."

Ya mutsa fuska tayi cike da alamar tambaya take kallon sa sannan ta ce

"Wacca Ƴar uwata kuma Sailuba ba ko wa?."

Girgiza ma ta kai ya yi alamar a'a kana Yace

"Fito mu shiga zakiga ko wacece ai."

Babu musu ta buɗe motar ta fito shima bayan ya fito suka riƙe Yaran sannan suka nufa ciki Yayin da wasu Nurses ma ta ke bin bayan su da kulolin abincin da suka zo dasu.

Ita dai Rafi'at tafiya take kawai amma gaba É—aya hankalin ta baya a jikin ta tunani take shin ko wurin waye haka Abubakar ya kawo su, ita ko kaÉ—an bata kawo wannan budurwa da suka taimakawa jiya a tunanin ta.

To akan me ma zatayi tunanin ko ita ce bayan cewa taimakon ta kawai suka yi bawai zasu kasance da ita bane.

Har suka ƙariso Ward ɗin bata ankara ba, har sai da taga waɗanan Nurses dake gabansu sun shiga wani Room kana ta fahimci nanne Room ɗin da wacca suka zo wurinta take.

Tura ƙofar Room ɗin Abubakar ya yi ya shiga Bakin sa ɗauke da sallama yayin da ita ma Rafi'at ta take masa baya.

Zaune take a saman gadon marasa lafiya jikinta sanye da kayan asibiti gaban ta kuma tufa ne take ci a hankali, kanta a duƙe tana kallon ƙasa, sai da ta cinye Wanda yake a bakinta sannan ta amsa sallamar da taji anayi a daidai lokacin da ta ɗago da kanta tana kallon mutanen dake shigowa ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallon Rashin sani.

Wani irin bugawa ƙirjin Rafi'at Ya yi ganin kyakyawar fuskar budurwar dake a ɗakin zaune saman bed.

It's unbelievable menene kuma haka me yasa Abubakar ya dawo dasu wurin wannan to su mata Mene?.

Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta sama wuri ta zauna a saman wata farar kujera kusa da mijinta Abubakar da shima ya zauna.

"Sannun ku fa please Mister and Mrs kune kuka taimake ni. In Yesterday?."

Budurwar ta musu tambayar fararen haƙoran ta duka a waje saboda murmushin dake akan kyakyawar fuskar ta.

Har Rafi'at ta buɗe baki zata bata amsa ke nan, likita ya turo ƙofar room ɗin ya shigo yana mai musu sallama.

Shiru Rafi'at tayi kamar mai tunani tana ji lokacin da su Abubakar da wannan budurwa suka amsa masa sallamar amma ita tafasar da zuciyarta take bai bari ta amsa ba.

Bayan wannan likita da Abubakar sun gaisa ne, budurwar ta kuma antayo musu tambayar É—azu.

Murmushi likita ya yi sannan yace

"Kedai Wannan patient nawa kinaso ki gano mutanen da suka taimake ki ko to ai sune waÉ—annan a gaban ki."

Dariya tayi cike Farin ciki ta kalla su Rafi'at da kyawawan Yaran dake a gaban su ta ce

"Barkanku dai."

Amsa ma ta suka yi da faÉ—in

"Yauwa kema barka."

Nan kuma suka shiga gaisawa da ita tana musu godiyar taimakon ta da suka yi.

Rafi'at murmushin yaƙe kawai take bin wannan kyakyawar budurwa dashi amma na ciki na ciki.

Kallon kyawawan Yaran tayi cikin shauƙi ta miƙawa Nainarh hannu alamar tazo, aikuwa Yarinyar ta ɓangale baki kana ta ɓanɓare hannunta daga cikin na Rafi'at ta rarrafa da saurinta irin na Yara, ta ƙarisa bakin gadon da budurwar take zaune sannan ta kama gadon tana kici kicin hawa.

Dariya kawai gaba ɗaya suke ma Nainarh wato shi dai Yaro ba Ruwan shi ƙaunar kowa Yake ba abin da ya dame shi.

Da sauri budurwar ta kamo hannun Nainarh tahau da ita saman gadon tana ma ta wasa, aikuwa ganin haka suma Nailah da Abdulmaleek suka ƙarisa wurin da saurin su aikuwa duka ta haɗa tana musu wasa da alama tana ƙaunar Yara sosai obaaaaa.

Kallon Abdulmaleek tayi da yake Babban cikin su sannan ta ce

"My friend please Tell me, what is your name?."

Dariya Yaron ya yi sannan cikin qwarancin sa na yara Yace

"Body."

/Buddy/

Dariya tayi cike da nishaÉ—i ta ce "Okay wato dai 'Buddy' kake so kace ko?."

Girgiza ma ta kai Yaron ya yi alamar "E," yana dariya.

Ta kuma cewa "To ai na gaskiyar nakeso ka faÉ—amin."

ÆŠan shiru ya yi kamar mai tunani sai kuma can Yayi dariya yace "Abdulmaleek naji Aya Aleem iya kiyana."

"Oh suna mai daɗi."🙂

Ta faÉ—a tana dariya.

'Kema Menene sunan ki, ko baki da suna ne?."

Yaron ya antayo ma ta tambayar wacca tasa ta yin murmushi sannan ta bashi amsa da

"Maleek ke nan ai kowa yana da suna a duniya kamar nima dai suna na, suna na...."

Shiru tayi kamar tana tunani sai da kyar ta iya faÉ—i cikin in'ina

"Suna na Ha-Ja-ah..."

Tayi maganar tana dafe qwoqwon kanta da taji kamar zai rabe gida biyu saboda raÉ—aÉ—in da yake ma ta.

"HAJARAH."

Rafi'at ta maimaita sunan cikin ranta tayi murmushi a fili ta ce

"Sunan ki mai daÉ—i kuwa?."

Murmushin ƙarfin hali budurwar mai suna Hajarah tayi tana kuma dafe kanta ta ce da kyar

"Nagode."

"Ah ah kodai kan yana miki ciwo ne, naga kina riƙewa?."

Rafi'at tayi ma Hajarah tambayar a yayin da take ƙarisawa wurin da take zaune saman bed.

"Eh Auntie sosai yake mugun rasamin jina nake kamar bani ba."

Hajarah ta bata amsa tana rumtse idanun ta.

Jin haka yasa likita ya yi ma Abubakar alama da su fita.

Ba musu Abubakar ya miƙe suka fita daga room ɗin, suka bar Rafi'at tana ma ta sannu haɗe karanto ma ta addu'o'i dan ta fahimci kamar hadda jinnu a zancen.

Kai tsaye office na likita suka wuce bayan sun zauna ne, Abubakar da ya gaza jurewa ya kalla likita cikin son jin ƙarin bayani yace

"Please Dr Khasim ko zan iya samun bayanan Rahoton lafiyar Hajarah kuwa?, danna fahimci akwai abin da yake damunta sosai."

Ajiyar zuciya Dr Khasim ya sauke sannan Ya fara magana

"A gaskiya Mister Mai Kyau akwai abin da yake damun wannan patient Hajarah abubuwa da yawa ma ba abu É—aya ba."

"Okay Inajin ka kamar mai da mai ke nan?."

Abubakar ya tambaya yana kuma gyara zaman sa sannan ya mayar da gaba É—aya hankalin sa akan Dr Khasim yana jira yaji abin da zaice.

"To kamar dai Yadda kaji na faÉ—a Malama Hajarah tana fama da matsaloli daban daban na Farko dai shi ne....

A binkciken da muka gunadanar akan kwakwalwarta shi ne na farko ta manta da gaba É—aya Ahalin ta da kuma ainihin State da take, sai dai abu É—aya da ya ba kowa mamaki shi ne....."

Katse sa Abubakar ya yi yana goge zufar da ta karyo masa kana cikin wata kalar murya yake faÉ—in

"Bangane ba Dr Khasim ban fahimci abin da kake nufi ba kwata kwata wai kana so kace min mutum zai iya mantawa da Ahalin sa ne a dalilin wani hatsari ko kuma taɓin kwakwalwa?."

Murmushi Dr Khasim ya yi sannan ya amsa da

"Of course wannan mai sauƙi ne, amma ka fara dakatawa kaji sauran abubuwan da suke damunta kafin kayi wasu tambayoyin."

Jin haka yasa Abubakar nutsuwa amma zuciyar sa bata bar bugu ba.

Dr khasim ya ci gaba da cewa

"Kamar yadda kaji ne, tabbas ta mance gaba ɗaya memory nata da ya taɓa faruwa a tsakaninta da Ahalinta, sannan kuma ta manta da sunan State da take gaba ɗaya a Brain nata...
Sai dai abu ɗaya shi ne bata manta ko wacece ita ba, ma'ana dai shi ne bata manta sunan ta ba, ko kuma karatun ta ko kuma wani burin ta bata manta dasu ba, sai dai kuma ɓangaren Ahalin ta dai...
A bisa binkciken da muka gabatar shi ne zata iya tunawa da Ahalinta da kuma sunan State nata kamar nanda shekara É—aya ko fi ye da haka a bisa hasashen wasu manyan likitocin duniya...
Amma idan shekara ɗaya tazo ta wuce wata shekarar ta zagayo bata tuna komai ba, tofah sai dai ayi haƙuri domin kuwa har abada ba zata taɓa tuna komai ba...."

Ido waje wannan karon Abubakar yake kallon Dr Khasim saboda tsananin mamaki ma kasa cewa komai ya yi kawai yana tauna maganganun Dr Khasim ne.

Sun É—auki tsawon lokaci a haka ba Wanda ya iya cewa komai, sai can bayan kamar mintuna biyar.
Abubakar ya nisa sannan yace

"Dr Khasim ina da wata tambaya É—aya fa."

Murmushi Dr Khasim ya yi kana Yace

"Okay Go ahead Inajin ka."

Abubakar Yace "To wai dama can an taɓa samun kalar wannan matsalar ne, mutum ya manta memory nasa da ya taɓa faruwa a tsakanin sa da Ahalin sa a dalilin hatsari ko wani Abun?."

"Eh an taɓa samu a ƙasar China Babban Birnin ƙasar wani mutum ya yi hatsarin mota sai gaba ɗaya ya manta da Ahalin sa da sunan garin sa abin da bai manta ba kawai shi ne shiɗin ɗan kasuwa ne, sannan kuma ƙarin abin mamakin bai manta da harkokin kasuwancin sa ba."

___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*___________________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

Page *67&68*

"A ƙasar India an taɓa samun irin haka ba iya nan ba a wasu ƙasashen ma anyi ta samu, amma ni dai a Nigeria wannan ne karo na farko dana tsinci wannan al'amari."

Nan dai Dr Khasim ya ci gaba da yima Abubakar bayani akan matsalolin da suke damun Hajarah.

A taƙaice dai su Abubakar basu suka bar wannan Asibitin ba sai wuraren ƙarfe ɗaya na rana.
Washe gari ma haka suka sake dawowa wurin Hajarah sannan Abubakar ya kuma komawa wurin Dr Khasim ya masa ƙarin bayani akan lafiyar Hajarah.
Chapter 61 · 0% Book details