Sashe 42
Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"In Allah ya yarda."
Ta faɗa hakan a lokacin da Madam Miracle ta miƙa ma ta box ɗin, harta juya zata koma, Madam Miracle ta ce
"Baki ji ba,"
Juyowa Jiddarh tayi tana kallon ta, murmushi Madam Miracle ta kumayi sannan ta miƙawa Jiddarh wani haɗaɗɗen Diamond Ring ta ce "Wannan dagani ne, na baki kyauta saboda kyanki kawai." 😃
Ihun mutane da sowa gurin ya kuma É—auka kamar kamar mene.
Dariya kawai Jiddarh takeyi a lokacin da Madam Miracle ta kammala zura ma ta Diamond ring a yatsarta na Ƙarshen hannun damar ta, godiya tayiwa Madam sannan ta juya tana nunawa mutane gift ɗinta da kuma tsadadden Diamond ring ɗin bayan komai ya lafa ta koma ta tsaya a gurin ta.
Haka aka ci gaba da kiran sunayen Æ´an matan Gasa har aka zo kan ta uku, aka bata kyautarta sannan ta dawo kusa dasu Jiddarh da budurwar da tayi ta biyu ta tsaya.
Madam Miracle ta ci gaba da jawabi cike da qwarewa da sanin takan abin, ana cikin haka ana shirin tufe taron kenan wata kyakyawar matashiyar budurwa daga cikin sauran Æ´an matan Gasan bakwai ta zube a gurin a sume.
Da sauri wata kyakyawar budurwa daga cikin ƴan kallo ta hau saman gurin tana kiran sunan budurwar da ta suma da alama budurwar Ƴar uwanta ce, duk yadda akaso wannan budurwa ta farka daga suman da tayi abu ya cutura, haka aka kwasheta ranga ranga zuwa asibiti.
Daga haka kuma taron dai ya tashi jikin kowa yayi sanyi laqwas.
Da gudu Jiddarh ta ƙarisa wajen su Humaira da suke tsaye curko curko a harabar Hall ɗin taron, bata damu da tarin mutanen dake kallonta da ɗaukar Video da kuma hotunan ta ba.
Rungumo Humaira da Auntie tayi a tare tana dariya.
"Oh Allah wai ke Jiddarh bakya girma ne?, ai wannan sai ki karyani fa." Cewar Auntie tana dariya.
Dariya Jiddarh takeyi ta ce "Auntie na ina farin ciki da murna yau, kawai dan ma abin da ya faru yanzu ya É—an sanyaya min jiki ne, don da alama yarinyar ta gaza jure rashin nasara ne shiyasa harta suma ko?."
Humaira ta ce "E, gaskiya abin akwai taɓa zuciya wata ƙila tayiwa Gasar dogon buri ne, sai kuma Allah yasa ba ita zata sama Nasara ba, sai ita kuma ta saka jure hakan ta sume."
"Koma miye matsalar ta can taje taji dashi ba damuwar ku bane, kuji da abin da yake a gaban ku yarana."
Cewar Auntie tana ya mutsa fuska. Da tsananin mamaki su biyun suke kallon ta jin abin da ta ce Jiddarh mamaki ya hanata magana, sai Humaira ce tayi ƙarfin halin cewa.
"Auntie wai mane naji kina faÉ—ane?, mutum ce fa ita, kuma mace dole zataji babu daÉ—i kinsan zuciyoyin mu ma ta akwai rauni."
Ɗan dafe goshi Auntie tayi tana cizan harshenta ganin tayi sakin layi a gabansu.😳
"Auntie dake fa nakeyi, kin min shiru?." Humaira ta faɗa a hasale tana fitar da numfar fashin ɓacin rai.
Gane yanayin da Humaira ta shiga ne yasa Auntie saurin kamo hannunta tana faÉ—in.
"Am so sorry my Dear, it's all my fault, na yadda bai kamata nayi wannan maganar ba. Amma ki yafeni kuskuren baki ne."
Da ƙarfi Humaira ta qwace hannunta daga cikin na Auntie, ta buɗe mota a fusace ta shiga ciki.
Ajiyar zuciya kawai Auntie take saukewa cike da tsaban tsoro, kamo hannunta Jiddarh tayi idanunta sun cicciko tab da qwalla ta ce "Dan Allah Auntie karki saka wannan abun a ranki, saboda ke mahaifiyarta ce kinsan dai ba halinta bane raini, bata cikin hayyacinta ne shiyasa.
Ɗan murmushi Auntie tayi sannan ta ce "Ba komai Jiddarh na sani gaskiyarta ne duka laifina ne, da banyi wannan maganar ba, da ranta bai ɓaci ba, har waɗannan mutanen su leƙo kuma a fusace."
Magana Auntie takeyi tana leƙen motar da Jumaira take ciki.
Hakan da tayi da kuma maganar da tayi duka ba ƙaramin dariya taso ta ba Jiddarh ba. Amma ta danne ta ce "Auntie wai ina su Sister Ni'ima ne suzo mutafi gida, lokaci yana ƙurewa fa, naji da wannan ɗaukar Video da hotunan da ake min."
Murmushi Auntie tayi ta ce "Su Ni'ima akwai gurin da zasu biya, ki shiga mota kawai mu tafi gida zamu haÉ—u dasu acan.
"To" Jiddarh ta ce sannan ta nufa motar da Humaira take ciki. Da sauri Auntie ta ce "A'a Jiddarh inaga kizo wannan motar da nake mu tafi tare naga kamar mutanen basu koma ba."
Qumshe dariya Jiddarh tayi tana rufe baki ta ce "A'a Auntie barni na shiga wannan kawai, ai sun sanni Abokai nane, babh abin da zasumin fa domin mun saba."
Tayi maganar tana buÉ—e motar zata shiga, Auntie ta ce
"Ni dai ba ruwa na, Jiddarh tunda kince wannan motar zaki shiga su waÉ—annan mutanen ba ruwan su da wata Abota ko Æ´an uwan taka uban mutum zasuci da gayya." ðŸ˜
Dariya Jiddarh tayi sannan ta shige motar ta zauna gefan Humaira dake waya abin ta. Daga ɓangaren hannun hagu ta zauna sannan driver yaja suka fita daga gate ɗin gurin motocin nasu guda huɗu rass, sannan suka ɗauki hanyar gida ɗoɗar.
A hanya Jiddarh ta ɗan kalla Humaira sai kuma da sauri ta kauda kanta tana karanto duk addu'ar da tazo bakinta, ƙara kallon Humaira tayi a zuciyarta ta ce "Wata ƙila sun koma."
Ɗan taɓo kafaɗun Humaira tayi cike da tsoro, wani irin juyowa Humaira tayi gaba ɗayanta tana kallon Jiddarh da idanunta waɗanda suka canza kala izuwa dark maroon.
Wani irin fitsarin tsoro ne yazo ma Jiddarh amma ta maƙale shi tana zare ido, so take tayi ihu koda driver zaiji ya tsayar da Motar kota samu ta tsere, amma ta kasa daga ta buɗe baki sai taji kamar an mayar dashi da ƙarfi an rufe. Ba abin da takeyi sai zufa ƙoƙari take tayi hawaye koda zasuji tausayinta. amma mandaƙas idanunta suke ko ɗan qwalla babu.
Matsawa jikin murfin mota take yayinda Humaira take biyota kamar wata 😘.
Wata dabara ce ya faÉ—o ma ta da sauri ta lalubo wayarta, a cikin jakarta dake a hannunta, cikin rawar hannu ta lalubo lambar Humaira ta danna kira.
Kai tsaye kiran ya shigo wayar Humaira dake saman cinyarta sautin zazzaƙar muryar Ahmad Sulaiman yana karanto suratul Ma'ida ya karaɗe motar.
Firgigit Humaira ta dawo hayyacinta, wata wawiyar ajiyar zuciya Jiddarh ta sauke sannan tayi rejected kiran, kallon Humaira tayi tana murmushin yaƙe ta ce "Uhm sannu Humaira kin farka daga baccin kenan.?"
Ya mutsa fuska Humaira tayi tana faɗin "Wai ya akayi ma na ganni a mota ba'a tsaye muke ba munajiran ƙarisowar Ni'ima.?"
Da sauri cikin sarƙewar murya Jieddarh ta ce "E, e mana kwarai, ai a tsaye muke sai kikace muzo mu tafi gida bacci kikeji, wannan ne abin da ya faru fa."
Qura ma ta ido Humaira tayi tana kallonta sannan ta ce "Ya naga kina inda inda kodai ƙishi kikeji ne.?"
Da sauri Jiddarh ta fara tari kamar da gaske tana faÉ—in "Ruwa, a bani ruwa please, dai dai lokacin da driver ya shiga da motar gidan.
Fitowa tayi daga motar tana riƙe baki kamar mai jin ƙishin da gaske da sauri Auntie ta ƙariso gurin tana tambayar ba'asi.
Cike da damuwa Humaira ta ce "Wai ƙishi takeji shiyasa take tari fa."
Kallon Jiddarh Auntie tayi zatayi magana Jiddarh ta kashe ma ta ido É—aya, tuni Auntie ta ramfo abin da take nufi. Dan haka kallon Humaira tayi ta ce "mu shiga ciki ko."
Da gudu Jiddarh ta taye sama bayan sun shiga palon saboda sauri in twin's take taka staircases É—in hannunta na rawa tasa key ta buÉ—e Bedroom É—in ta.
Da ido Auntie da Humaira suka bita da kallo Sannan Auntie ta dawo da kallonta kan Humaira cike da tuhuma ta ce "Menene ya faru a mota naga kamar bata cikin nutsuwar ta.?"
Fuskarta da alamar Rashin jindaɗi Humaira ta ce "Nima dai bansan abin da ya faru ba, farkawa kawai nayi na tsinci kaina a cikin mota driver yana tuƙi ga Jiddarh a gefena, shi ne na tambaye ta abin da ya faru tahau inda inda, bayan na tambaye ta ko qishi takeji sai ta hau tari ba ƙaƙƙautawa."
Humaira tayi maganar tana zama a two sieter.
"To Allah ya kyauta gaba."
Cewar Auntie a lokacin da tayi picking call É—in da ya shigo wayarta, sannan tayi hanyar kitchen tana magana.
Da ido Humaira ta bita sai kuma ta taɓe baki tana gyara kwanciyar a saman kujerar da take akai.
Jiddarh kuwa tana shiga haÉ—aÉ—É—en palon ta wanda ya gaji da haÉ—uwa, jifa tayi da handbag É—inta saman kujera sannan ta É—auki ruwan roba a fridge tasha, kana ta dawo ta zauna akan kujera tana kici kicin rage kayan jikinta.
Sai da ta kammala cire doguwar gown ɗin jikinta sannan ta miƙe ta shige Bedroom a saman bed ta aje gown ɗin sannan ta shiga bathroom.
Sai da ta kwashe mintuna Ashirin tana wanka kana ta fito É—aure da towel White color a chest É—inta.
Gaban Dress Mirror ta tsaya tana kallon kanta tayi murmushi afili ta ce "Saini Jiddarth ɗiyar Ahalin Komai Naga, yau na cinye Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha saura na ƙasa, ina fatan kamar yadda na lashe wannan shima na lashe shi." 😎
Sai tayi shiru da sauri ta ɗauki red jam baki ta buɗe, sannan ta zizara a saman jajayen laɓɓanta kana ta mayar da jam bakin saman Dress Mirror.
Kallon kanta ta kuma a madubi washe baki tayi a fili ta kuma cewa "Amazing Masha Allah sai ni Jiddarh kuma fa wallahi ina da kyau sosai. Ya Allah wannan baiwar ta ka Jiddarh tana godiya da wannan hallitar da aka ma ta bada wayonta ko dabara ba."
Kwance Ribbons É—in da ta É—aure dogon gashin kanta tayi aikuwa gashin ya zubo ta gabanta da bayanta duk yabi ya rufe ma ta fuska.
Gefe ta matsa da gashin da ya rufe ma ta fuska, kallon kanta ta kumayi a madubi ta ce "Wash sai ni Jiddarh SARAUNIYAR KYAU a garin kano, wannan kyau haka aiko Larabawa da Turawa saina cinyesu a Gasa bansani ba."
Ta faɗa hakan a lokacin da Madam Miracle ta miƙa ma ta box ɗin, harta juya zata koma, Madam Miracle ta ce
"Baki ji ba,"
Juyowa Jiddarh tayi tana kallon ta, murmushi Madam Miracle ta kumayi sannan ta miƙawa Jiddarh wani haɗaɗɗen Diamond Ring ta ce "Wannan dagani ne, na baki kyauta saboda kyanki kawai." 😃
Ihun mutane da sowa gurin ya kuma É—auka kamar kamar mene.
Dariya kawai Jiddarh takeyi a lokacin da Madam Miracle ta kammala zura ma ta Diamond ring a yatsarta na Ƙarshen hannun damar ta, godiya tayiwa Madam sannan ta juya tana nunawa mutane gift ɗinta da kuma tsadadden Diamond ring ɗin bayan komai ya lafa ta koma ta tsaya a gurin ta.
Haka aka ci gaba da kiran sunayen Æ´an matan Gasa har aka zo kan ta uku, aka bata kyautarta sannan ta dawo kusa dasu Jiddarh da budurwar da tayi ta biyu ta tsaya.
Madam Miracle ta ci gaba da jawabi cike da qwarewa da sanin takan abin, ana cikin haka ana shirin tufe taron kenan wata kyakyawar matashiyar budurwa daga cikin sauran Æ´an matan Gasan bakwai ta zube a gurin a sume.
Da sauri wata kyakyawar budurwa daga cikin ƴan kallo ta hau saman gurin tana kiran sunan budurwar da ta suma da alama budurwar Ƴar uwanta ce, duk yadda akaso wannan budurwa ta farka daga suman da tayi abu ya cutura, haka aka kwasheta ranga ranga zuwa asibiti.
Daga haka kuma taron dai ya tashi jikin kowa yayi sanyi laqwas.
Da gudu Jiddarh ta ƙarisa wajen su Humaira da suke tsaye curko curko a harabar Hall ɗin taron, bata damu da tarin mutanen dake kallonta da ɗaukar Video da kuma hotunan ta ba.
Rungumo Humaira da Auntie tayi a tare tana dariya.
"Oh Allah wai ke Jiddarh bakya girma ne?, ai wannan sai ki karyani fa." Cewar Auntie tana dariya.
Dariya Jiddarh takeyi ta ce "Auntie na ina farin ciki da murna yau, kawai dan ma abin da ya faru yanzu ya É—an sanyaya min jiki ne, don da alama yarinyar ta gaza jure rashin nasara ne shiyasa harta suma ko?."
Humaira ta ce "E, gaskiya abin akwai taɓa zuciya wata ƙila tayiwa Gasar dogon buri ne, sai kuma Allah yasa ba ita zata sama Nasara ba, sai ita kuma ta saka jure hakan ta sume."
"Koma miye matsalar ta can taje taji dashi ba damuwar ku bane, kuji da abin da yake a gaban ku yarana."
Cewar Auntie tana ya mutsa fuska. Da tsananin mamaki su biyun suke kallon ta jin abin da ta ce Jiddarh mamaki ya hanata magana, sai Humaira ce tayi ƙarfin halin cewa.
"Auntie wai mane naji kina faÉ—ane?, mutum ce fa ita, kuma mace dole zataji babu daÉ—i kinsan zuciyoyin mu ma ta akwai rauni."
Ɗan dafe goshi Auntie tayi tana cizan harshenta ganin tayi sakin layi a gabansu.😳
"Auntie dake fa nakeyi, kin min shiru?." Humaira ta faɗa a hasale tana fitar da numfar fashin ɓacin rai.
Gane yanayin da Humaira ta shiga ne yasa Auntie saurin kamo hannunta tana faÉ—in.
"Am so sorry my Dear, it's all my fault, na yadda bai kamata nayi wannan maganar ba. Amma ki yafeni kuskuren baki ne."
Da ƙarfi Humaira ta qwace hannunta daga cikin na Auntie, ta buɗe mota a fusace ta shiga ciki.
Ajiyar zuciya kawai Auntie take saukewa cike da tsaban tsoro, kamo hannunta Jiddarh tayi idanunta sun cicciko tab da qwalla ta ce "Dan Allah Auntie karki saka wannan abun a ranki, saboda ke mahaifiyarta ce kinsan dai ba halinta bane raini, bata cikin hayyacinta ne shiyasa.
Ɗan murmushi Auntie tayi sannan ta ce "Ba komai Jiddarh na sani gaskiyarta ne duka laifina ne, da banyi wannan maganar ba, da ranta bai ɓaci ba, har waɗannan mutanen su leƙo kuma a fusace."
Magana Auntie takeyi tana leƙen motar da Jumaira take ciki.
Hakan da tayi da kuma maganar da tayi duka ba ƙaramin dariya taso ta ba Jiddarh ba. Amma ta danne ta ce "Auntie wai ina su Sister Ni'ima ne suzo mutafi gida, lokaci yana ƙurewa fa, naji da wannan ɗaukar Video da hotunan da ake min."
Murmushi Auntie tayi ta ce "Su Ni'ima akwai gurin da zasu biya, ki shiga mota kawai mu tafi gida zamu haÉ—u dasu acan.
"To" Jiddarh ta ce sannan ta nufa motar da Humaira take ciki. Da sauri Auntie ta ce "A'a Jiddarh inaga kizo wannan motar da nake mu tafi tare naga kamar mutanen basu koma ba."
Qumshe dariya Jiddarh tayi tana rufe baki ta ce "A'a Auntie barni na shiga wannan kawai, ai sun sanni Abokai nane, babh abin da zasumin fa domin mun saba."
Tayi maganar tana buÉ—e motar zata shiga, Auntie ta ce
"Ni dai ba ruwa na, Jiddarh tunda kince wannan motar zaki shiga su waÉ—annan mutanen ba ruwan su da wata Abota ko Æ´an uwan taka uban mutum zasuci da gayya." ðŸ˜
Dariya Jiddarh tayi sannan ta shige motar ta zauna gefan Humaira dake waya abin ta. Daga ɓangaren hannun hagu ta zauna sannan driver yaja suka fita daga gate ɗin gurin motocin nasu guda huɗu rass, sannan suka ɗauki hanyar gida ɗoɗar.
A hanya Jiddarh ta ɗan kalla Humaira sai kuma da sauri ta kauda kanta tana karanto duk addu'ar da tazo bakinta, ƙara kallon Humaira tayi a zuciyarta ta ce "Wata ƙila sun koma."
Ɗan taɓo kafaɗun Humaira tayi cike da tsoro, wani irin juyowa Humaira tayi gaba ɗayanta tana kallon Jiddarh da idanunta waɗanda suka canza kala izuwa dark maroon.
Wani irin fitsarin tsoro ne yazo ma Jiddarh amma ta maƙale shi tana zare ido, so take tayi ihu koda driver zaiji ya tsayar da Motar kota samu ta tsere, amma ta kasa daga ta buɗe baki sai taji kamar an mayar dashi da ƙarfi an rufe. Ba abin da takeyi sai zufa ƙoƙari take tayi hawaye koda zasuji tausayinta. amma mandaƙas idanunta suke ko ɗan qwalla babu.
Matsawa jikin murfin mota take yayinda Humaira take biyota kamar wata 😘.
Wata dabara ce ya faÉ—o ma ta da sauri ta lalubo wayarta, a cikin jakarta dake a hannunta, cikin rawar hannu ta lalubo lambar Humaira ta danna kira.
Kai tsaye kiran ya shigo wayar Humaira dake saman cinyarta sautin zazzaƙar muryar Ahmad Sulaiman yana karanto suratul Ma'ida ya karaɗe motar.
Firgigit Humaira ta dawo hayyacinta, wata wawiyar ajiyar zuciya Jiddarh ta sauke sannan tayi rejected kiran, kallon Humaira tayi tana murmushin yaƙe ta ce "Uhm sannu Humaira kin farka daga baccin kenan.?"
Ya mutsa fuska Humaira tayi tana faɗin "Wai ya akayi ma na ganni a mota ba'a tsaye muke ba munajiran ƙarisowar Ni'ima.?"
Da sauri cikin sarƙewar murya Jieddarh ta ce "E, e mana kwarai, ai a tsaye muke sai kikace muzo mu tafi gida bacci kikeji, wannan ne abin da ya faru fa."
Qura ma ta ido Humaira tayi tana kallonta sannan ta ce "Ya naga kina inda inda kodai ƙishi kikeji ne.?"
Da sauri Jiddarh ta fara tari kamar da gaske tana faÉ—in "Ruwa, a bani ruwa please, dai dai lokacin da driver ya shiga da motar gidan.
Fitowa tayi daga motar tana riƙe baki kamar mai jin ƙishin da gaske da sauri Auntie ta ƙariso gurin tana tambayar ba'asi.
Cike da damuwa Humaira ta ce "Wai ƙishi takeji shiyasa take tari fa."
Kallon Jiddarh Auntie tayi zatayi magana Jiddarh ta kashe ma ta ido É—aya, tuni Auntie ta ramfo abin da take nufi. Dan haka kallon Humaira tayi ta ce "mu shiga ciki ko."
Da gudu Jiddarh ta taye sama bayan sun shiga palon saboda sauri in twin's take taka staircases É—in hannunta na rawa tasa key ta buÉ—e Bedroom É—in ta.
Da ido Auntie da Humaira suka bita da kallo Sannan Auntie ta dawo da kallonta kan Humaira cike da tuhuma ta ce "Menene ya faru a mota naga kamar bata cikin nutsuwar ta.?"
Fuskarta da alamar Rashin jindaɗi Humaira ta ce "Nima dai bansan abin da ya faru ba, farkawa kawai nayi na tsinci kaina a cikin mota driver yana tuƙi ga Jiddarh a gefena, shi ne na tambaye ta abin da ya faru tahau inda inda, bayan na tambaye ta ko qishi takeji sai ta hau tari ba ƙaƙƙautawa."
Humaira tayi maganar tana zama a two sieter.
"To Allah ya kyauta gaba."
Cewar Auntie a lokacin da tayi picking call É—in da ya shigo wayarta, sannan tayi hanyar kitchen tana magana.
Da ido Humaira ta bita sai kuma ta taɓe baki tana gyara kwanciyar a saman kujerar da take akai.
Jiddarh kuwa tana shiga haÉ—aÉ—É—en palon ta wanda ya gaji da haÉ—uwa, jifa tayi da handbag É—inta saman kujera sannan ta É—auki ruwan roba a fridge tasha, kana ta dawo ta zauna akan kujera tana kici kicin rage kayan jikinta.
Sai da ta kammala cire doguwar gown ɗin jikinta sannan ta miƙe ta shige Bedroom a saman bed ta aje gown ɗin sannan ta shiga bathroom.
Sai da ta kwashe mintuna Ashirin tana wanka kana ta fito É—aure da towel White color a chest É—inta.
Gaban Dress Mirror ta tsaya tana kallon kanta tayi murmushi afili ta ce "Saini Jiddarth ɗiyar Ahalin Komai Naga, yau na cinye Gasar SARAUNIYAR KYAU matakin jaha saura na ƙasa, ina fatan kamar yadda na lashe wannan shima na lashe shi." 😎
Sai tayi shiru da sauri ta ɗauki red jam baki ta buɗe, sannan ta zizara a saman jajayen laɓɓanta kana ta mayar da jam bakin saman Dress Mirror.
Kallon kanta ta kuma a madubi washe baki tayi a fili ta kuma cewa "Amazing Masha Allah sai ni Jiddarh kuma fa wallahi ina da kyau sosai. Ya Allah wannan baiwar ta ka Jiddarh tana godiya da wannan hallitar da aka ma ta bada wayonta ko dabara ba."
Kwance Ribbons É—in da ta É—aure dogon gashin kanta tayi aikuwa gashin ya zubo ta gabanta da bayanta duk yabi ya rufe ma ta fuska.
Gefe ta matsa da gashin da ya rufe ma ta fuska, kallon kanta ta kumayi a madubi ta ce "Wash sai ni Jiddarh SARAUNIYAR KYAU a garin kano, wannan kyau haka aiko Larabawa da Turawa saina cinyesu a Gasa bansani ba."