← Book details Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 67 OF 92

Sashe 67

Sarauniya Kyau Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ashe dama can tana da ciki bata faÉ—awa Abubakar ba, aikuwa koda ya gano haka saiya haÉ—asu gaba É—aya yana kula dasu da cikin jikin su.

This novel Book 2 will be paid book fa, a next post zan faɗi nawa ne payment ɗin_Karku damu sosai zan muku discount_-_😇

*For More Enquires*
08081129487
_-_💓The Nainarh KD💓_-_

___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙

Page *75&76*
_-_Still free page's muke_-_

______**

Rayuwa ta ci gaba da tafiya cike da tarin nasarori sannan kuma ta gefe guda Abubakar yana kula da matan sa duka da cikin jikin su, a lokacin da cikin jikin Hajarah yakai watanni bakwai shima na Rafi'at dai dai lokacin yakai watanni bakwai, ganin haka yasa Abubakar ya samo wata Dattijuwa tana kula dasu gaba É—aya.

A Ranar wata lahadi da Yammaci Hajarah ta fara naƙuda sai dai kuma da yake haihuwar fari ne, batasan kan abin ba, shiru tayi bata faɗawa kowa ba, gashi kuma Abubakar baya ƙasar ya tafi ƙasar jamus a kan harkar kasuwancin sa.

Har gari ya waye ba wanda yasan Hajarah tana naƙuda, sai ita kaɗai wani Abin mamaki kuma a Ranar Rafi'at wuraren ƙarfe sha ɗaya na safe ta santalo jaririyarta da taimakon wannan Dattijuwar mata dake gidan, a lokacin Hajarah tana can ɓangaren ta ita ma tana fama da kanta domin kuwa naƙuda take yi sosai.

Ganin har wuraren sha biyu anyi Haihuwa a gidan har ma Ƴan uwan Rafi'at sun fara zuwa, amma Hajarah bata fito ba yasa Dattijuwar matar,
Hankalin ta ya gaza kwanciya hakan yasa ba shiri ta nufa ɓangaren Hajarah domin ganin ko lafiya, aikuwa tana zuwa ta tarar da Hajarah cikin wani hali na naƙuda wanda ba wacca zatasan Yanayin sai macen da ta taɓa ɗanɗanar haihuwa.

Aikuwa nan wannan Dattijuwar mata ta shiga bawa Hajarah taimakon da ya kamata, a taƙaice dai Hajarah ba ita ta hafe abin da ke cikin ta ba, sai Yammaci wuraren ƙarfe uku na Rana, sannan Ita ma ta santalo jaririyarta mace mai kama da ita Tamkar an tsaga kara, komai irin na ta ne sak, sai lokacin ta fara baccin wahala.

Zuwa dare gaba ɗaya dangi Ƴan uwa da Abokan arziƙi sunji haihuwar da a kayi ma Abubakar duka mata, hatta mutanen France sunji ta hanyar wayar tarho ko washe gari mutanen Jigawa State dana Adamawa dana Mai Duguri Kano gaba ɗaya sun hallara a gidan Abubakar cike da farin ciki, aikuwa nan aka shiga kula da masu jego.

A Ranar da suka cika kwanaki uku da Haihuwa Abubakar ya dura Nigeria aikuwa Ya yi kyakyawar gani a cikin gidan sa.
Gaba ɗaya matan da ya bari haihuwa yau ko gobe su ya tarar ko wacce da kyakyawar Ɗiyar da ta haifa masa, saboda tsananin farin ciki a lokacin rasa mai zayyi ya yi aikuwa ba tare da ɓata lokaci ba ya yi sujadar shukur yana miƙa godiyar sa ga Allah da ya nufe sa da ganin wannan rana.

A lokacin in banda dariya babu abin da su Sakeenah da su Zuwaira suke masa nan ya shiga É—aukar jariran, idan ya É—auki na Hajarah sai ya a je ya É—auki na Rafi'at haka yake ta yi abin gunin burgewa.

Wani ƙarin ikon Allah kuma gaba ɗaya jariran biyu, mugun kama suke da juna tamkar mace ɗaya ce ta haife su, aikuwa nan mutane suka dingi magana a kan wannan abin mamaki.

Ranar suna kuwa ɗiyar Hajarah taci suna Zaynerb a Yayin da Ɗiyar Rafi'at taci suna Haleesat, wato dai har lokacin Abubakar bai manta da Haleesat Rashid Rayyan ba masoyin gaskiya ke nan, Allah sarki Rayuwa a lokacin har da yawa sun manta da ita.😞

Ba ƙaramin daɗin wannan sunan da Abubakar ya sakawa ɗiyarsa dangin Rafi'at suka ji ba, a lokacin wasu daga ciki har sai da suka yi kuka na tunawa da maragayya Haleesat Rashid Rayyan mutumiyar kirki.

Ita ma dai Hajarah sai lokacin take sanin wacece Haleesat Rashid Rayyan a wurin Abubakar.

Rayuwa ta ci gaba da antayewa yayin da Abubakar yake kula da matan sa duka domin kuwa ƙin bari ya yi su Hajiya Harirah su ɗauki Hajarah wankan gida, a lokacin sai dai Hajiya Harirah ce tazo ta zauna dasu tana kula da Hajarah, yayin da ita kuma Rafi'at wannan Dattijuwar mata da ta amsa haihuwar su take kula da ita.

---**

Wani Abun mamaki da ya taɓa faruwa Wanda gaba ɗaya Ahalin Alhaji Sameer Lamiɗo ba zasu taɓa mantawa dashi ba shi ne.

A wata Ranar Alhamis da safe lokacin Rafi'at da Hajarah suka cika watanni uku da Haihuwa, Ranar Abubakar bai fita Company ba.
Wuraren goma na safe suna zaune a palon gidan shida Rafi'at da Hajiya Harirah da kuma sauran Yaran gidan suna taɓa fira sama sama.

Sai ga Hajarah ta shigo tamkar an jefo ta, sai faman goge gumi take ga fuskar ta ɗauke da matsanancin Farin ciki saboda tsananin saurin da take yi har Ƴarta Zaynerb dake hannunta ta kusa faɗi ƙasa, ta taro ta.

_-_Mgnr Payment da nace. Tabbas Book 2 is paid fa_-_

_Duk Wanda Ya shirya ayi tafiyar da shi, kuma ya shirya Payment_

_-_Just Pay With This Details_

_-_-_-_-_-_
*The Phone Number*
*08081129487*
*The Acct Number*
*8081129487*
*The Bank Name*
*Palmpay Bank*
*The Acct Name*
*Khadeejarth Sabi'u Yahyah*

___*💋 SARAUNIYAR KYAU 💋*_________ƚαƙυɳ ϝαɾƙσ__________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉. 𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖. 𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆
💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙

☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

Page *77&78*

Qarisowa tayi sannan ta tsaya a tsakiyar palon tana faman sauke ajiyar zuciya game da haki, ganin yadda ta shigo a hargitse kamar wani ya biyo ta yasasu gaba É—aya tashi suna tambayar abin da ke faruwa.

A hankali ta buÉ—e kyakyawan idanunta waÉ—anda saboda tsananin farin cikin da take ciki yasa suka kawo ruwa, ta kallesu dasu sannan ta fara magana.

"Ina cikin farin ciki wanda tunda nake a Rayuwata ban taɓa shiga ciki ba. Yau kuma a dai dai wannan lokaci na tuna WACECE NI, Yau bayan shafe tsawon shekaru ɗaya da wata biyar da kwanaki biyar da mintuna goma sha biyar da sakanni, a Yau ni 'Hajarah Haleed Mai Waje: na tuna Asalina na tuna Ahalina na tuna sunan State nawa, na tuna komai da komai duka...'

Tayi maganar ne a Yayin da wasu siraran Hawayen Farin ciki suka wanke ma ta fuska.

Gaba ɗayansu jama'ar dake a palon kabbara suka saka cike da tsantsan farin ciki, shikuwa Abubakar gaza jurewa ya yi har sai da ya yi sujadar shukur yana kuma miƙa godiyar sa ga Allah wato dai maganar bahaushe ce da yake cewa INDA RAI DA RABO ikon Allah, gashi dai daga ƙarshen ƙarshe, Hajarah zata kuma haɗuwa da Ahalinta a karo na biyu, Allah ke nan buwayi gagara misali.

Da gudu Rafi'at ta ƙarisa wurin Hajarah ta Rungumo ta gaba ɗayanta a jiki tana faɗin

"Na tayaki murna sosai sosai Abokiyar."

Da yake haka suke kiran juna, murmushi Hajarah tayi tana kuma damƙe hannun Rafi'at dake cikin nata Sannan ta ce

"Nagode sosai Abokiyar, Allah ya bar ƙauna."

Hajiya Harirah kuwa tun ɗazu fuskar ta ɗauke take da matsanancin Farin ciki, saboda haka sai ta kasa magana, kawai tana binsu da kallo, ƙari sowa wurin ta Hajarah tayi Bayanta miƙawa Abubakar Zaynerb kana ta Rungumo Hajiya Harirah faɗi take

"Hajiyar mu kita yani murna da farin ciki Yau ina cikin nishaÉ—i obaaaaa..."

Sai da gaba É—aya suka sama nutsuwa suka zazzauna sannan kuma Abubakar ya É—auki waya yana kiran gaba É—aya dangi yana faÉ—a musu Abin farin cikin da suka wayi gari da shi.

Aikuwa nan aka dingi tayasu murna barinma dai su Zuwaira, Jawaheer, Jummai Sakeenah waɗanda suka ɗauki Hajarah matsayin Ƴar uwa ba matar ɗan uwansu ba, ai nan mutanen Jigawa State suka ce gasunan ƙarisowa Abujan ayi farin ciki tare dasu.

A Ranar gaba É—aya Ahalin sun wuni ne cike da farin ciki mara misaltuwa.

Misalin ƙarfe bakwai na Yammaci mutanen Jigawa State tun daga kan Alhaji Sameer Lamiɗo Dr_Raheemah Hajiya Zuwairiya, Zuwaira, Jawaheer, Jummai hatta Sakeenah dake Aure a Adamawa State sai da ta hallara a garin Abuja gaba ɗayansu sun ƙariso.

Wuraren ƙarfe Takwas da Rabi na dare gaba ɗaya sun hallara a Babban palon gidan, suna fira cike da nishaɗi bayan komai ya lafa ne Alhaji Sameer Lamiɗo ya kalla Hajarah cike da kulawa Yake faɗin

"ÆŠiyata Hajarah gaba É—aya nida Ahalina muna tayaki murnar tuno Rayuwar ki da Ahalin ki da kikayi.."

Murmushi tayi cike da jindaÉ—i ta amsa da

"Ina godiya sosai Abbhee..."

"Tohm ni dai har Yanzu banji sunan State É—in namu ba."

Cewar Jawaheer cike da zoyala, murmushi Hajarah take saboda farin cikin da take ciki ma haƙoranta sunƙi rufuwa gyara zama tayi kana ta fara magana kamar haka.

"Da Farko dai kamar Yadda kuka sani sunana Hajarah sunan mahaifina kuma Alhaji Haleed Mai Waje, ni ɗin cikakkiyar Ƴar Garin KADUNA STATE ce dake a nan AREWA cikin Nigeria Yankin Africa."🌍

"Alhamdullilah.

Masha Allah..

Hakan akeso..."

Haka kawai gaba ɗaya mutanen da ke zazzaune a palon suke faɗa nan kuma aka ƙara tayata murna daga nan kuma Sabuwar fira ta ɓalle a tsakani daga ƙarshe sun yanke shawarar cewa gobe tun daga kan Alhaji Sameer Lamiɗo da matansa da kuma Zuwaira da Abubakar sai kuma ita Hajarah ɗin zasu wuce Kaduna Garin Gwamna domin haɗuwa da Ahalin Hajarah, daga haka kuma taron ya watse dama lokacin dare Ya yi sai kowa ya sama makwanci, dama kuma Hajarah ita keda girki sai kawai tabi mijinta tura karsa.🤭

*WASH£-GARI*

Wuraren ƙarfe goma sha ɗaya na safe gaba ɗayansu Ahalin tsaye suke a filin ajiye motoci na gidan. Yayin da waɗanda zasuyi tafiyar suna shirye tsaf, Yayin da kuma waɗanda ba da su za'a tafi ba, suka tsaya daga gefe suna musu ban kwana cike da Fatan Nasara.

Bayan sun gama ban kwana É—in ne gaba É—aya suka shiga motoci da yake motocin ba kalar na wannan zamanin bane, shiyasa sai da suka yi mota uku sannan gaba É—aya suka shiga ciki.

*SAIDAI KUMA ME?.*
Chapter 67 · 0% Book details