Sashe 61
Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
kuma Yaya Ishaq ne cikin Jallabiya mai ruwan madara. Zainab na ganin mu ta saki mirmishi nima sai na sakar mata ta fara taku zuwa garemu muma sai muka fara takawa Hannuna gam cikin na Engr. muna tafe jiki na gugan jikin juna. Idanuwana Zainab suke kallo ammh bansan ta yadda akayi ba idanuwana suka sauka kan Yaya ishaq ba,ido hudu muka hada da shi,Mirmishi nayi masa sai yayi kasa da idonsa ammh bai dauke ba gabadaya,shi kuma ni yake kallo tare da kallon hannuna cikin na Engr dake Sarke da juna. Gabana ya yi wani ras!har sai da takalmin kafata ya turgud'eni zan fad'i Engr ya yi saurin rikoni yana kallona nima shi na kallah cikin sanyin muryansa yace"Are u ok..? Da kai na amsa masa sannan ya sakeni ammh bai yarda ya saki hannuna ba. Sai da muka kariso gabda juna sannan ya sakeni ganin kuma Zainab ta bude hannuwanta bakinta kamar Gonar Auduga tana fadin"Oyoyo Oyoyo ga maman Amir" Nima sai na bude hannayena muka Tarbi juna cikin fara'a muka rungume juna. Kafin mu saki juna muna bin juna da kallo cikin fara'ar da taki barin fuskokin mu dani da ita. Yaya Ishaq ko hannu ya mikama Engr cikin jin nauyi suka yi musabaha tare da gaisawa Engr ko a fuska bai nuna masa da wani abu ba. shima ya tarbesa cikin Fara'a kamar wani abu bai taba shiga tsakaninsu ba Zainab ta rike hannuna tana gaishe da Engr ya amsa mata cikin fara'a da Tambayan yara. Tace duk suna lafiya tana kamkame da Hannuna tace"Bismillah mu shiga ciki" Sai muka yi gaba,ni da ita su kuma suka bi bayan mu duk sai naji na takura na kalli Ishaq ta gefen idanuwana sai da gabana ya fadi da ganin irin ramar da yayi kamar wanda ya shekara yana jinya. Shima duk da ban sani ba ya kalleni sannan nasan yana mamakin sauyawata. Zainab ke min mgana kasa kasa da cewa"Kin ganki kuwa maman Amir..?ko dai an samo mana bby Honeymoon ne? Dariya nayi ban yi mgana,ita ta shiga gaba tana janye da hannuna har cikin Falon,yaran duk suna falon Har da Mama da Shema'u. Zainab na kan gaba ta kareni tace"Anum.." Anum dake zaune kan kujera tana duba littafan makarantar ta yan SS1 ce,First time,musty na zaune a kasan Cafet ya na zanensa na fama Ahmad Kuma na gaban Tv shi da Farhan suna kallon Mbc3,Amir kuma na daga chan gefen Mama wani Novel din Turanci ne a hannunsa yana karantawa Fadil na kan jikinsa ya lafe kamar mara lafiya. Kiran sunan Anum da Zainab tayi yasa duka yaran suka dago suna kallonta Batayi mgana ba illah kaucewa da tayi na bayyana afalon. ina saka yarana a ganina naji idanuwana sun cika da kwallar Farinciki da wani irin kewa da ban taba ji ba. Gabadayan su suka mike har da Amir kuwa da naga ya kara zama wani Zabgege ga tsawo ga jiki irin na Ubansa Dukkansu bakin su ya kasa motsi mamakin ganina suke yi,Ahmad ne ya bude murya kafin yace"UMMAA..! Sai na gyada mai kai sai hawaye sharr na Farinciki suka zobomin na zube gwiwoyiyina a kasa na bude hannayena ina fadin"Umma ce Ahmad di'n Umma" Ai da gudu ya rugo ya fada jikina sai ya fashe da kuka Musty ma ganin haka ya watsar da Abun da yake yi ya iso gareni yana fadin"Umma..! Sai kuka shima nima kukan nake yi,Farhan ma ya kariso yana kallona yace'Umma..' Kamar yana tamtama sai na jawosa jikina na hada da su Ahmad na Rumgume ina fadin"Farhan din Umma ina Fadil..! Sai kawai naji an chakumeni ta baya ashe Fadil ne bakina yaki Rufuwa ina kuka ina Hawaye ina Dariya Lokaci daya ina fadin"Fadil..Fadil d'in Umma" Yana Dariya yace"Umma umma..Ina kika tafi bana ganin ki? Ya fad'a yana shafa Fuskata kamar yana Tantamar ni ce ko ba ni ba ce. Ni ko kuka ya hanani mgana Duka na hadasu na rumgume ina Hawaye ina Dariyan jin dadi raina nake jin wani salama da kwanciyar Hankali suna shigata Amir da Anum sun kariso gabana ammh sun kasa bin ayarin yaran,sai da na ji Anum na fadin"Umma mu kin manta damu..? Tafad'a idanuwanta taf da kwallah sai na mika mata hannuna Daya ta kama ina Hawaye nace"Ina ni ina mantawa da Anum din Umma" Amir dake gefe yace"Umma ita Kadai..Ita k'adai..kika gani" Yafada muryansa tana wani irin rawa,da kuma wani kewa a cikinta. Na dago ido na ina kallonsa sai na mika masa Dayan hannun ina fad'in"Babana bazan manta dakai ba kaima zo. kuzo wajen Umma" Gabadayansu suka taho atare suka Duka suka bi bayan kannensu a tare Amir da Anum suka fashe da kuka nima kukan nake yi kasa kasa har yana bayyana ammh na farinciki. Mama dake gefe ta Dauke kwallarta tana mirmishi,Dazu taga Zainab tazo ta kira Ishaq kila zuwan Fa'izan ta shaida masa Allah sarki Uwa. ita uwa tana da girma girman da Ubangijine kadai yasan iyakarsa. shema'u ta kalli Mama kafin tace"Maman Innar su Anum ce..? Mama ta gyada kai batayi mgana ba Ranta ya cika da wani nauyi da ta rasa ko na menene tasan dai na kunya da nauyin Fa'iza ne sannan da Tausayin yaran nan. Ba ita kadai ta share kwallah ba Hatta Ishaq sai da ya juya baya yana goge kwallar da suka cika kwarmin Idanuwansa. Engr na kallonsa sai ya nuna kamar bai gani ba. yana Daga baya ya sagale hannayensa a bayansa yana kallona ni da ya'yana wani irin kauna da soyayya da baisan yana yi min yaji ya kara sarkeshi, ya tabbata ba karamin kaddara bace ta fidda ni daga gidan mijina sannan ya kara Godema kaddara data kaddara auran mu. Zainab ma sai da ji kwalla sun kawo mata,sai daga baya baya ne aka samu sauki ammh ko da yaushe yaran cikin kiran Umma suke Fa'iza ba a iya Rayuwar ya'yanta take da tasiri ba har a rayuwar su Farhan domin mai kulawa dakai baya bace maka aranka har abada. Zainab ce ta matso tana Fadin"To ku saki Umman naku ta zauna ta Huta mana" Jin haka yasa su Amir suka tashi da Musty Ammh Ahmad da Fadil makalemin sukayi kamar zan gudu haka na mike suna rike da hannayensu Ahmad bakinsa ya bude fadi kawai yake yi"Umma nan zaki kwana..? Fadil kuma"Umma ni zan biki gidan ki" Ina Dariya nace"Yaran Umma duk sun kara girma" Na fada ina kara ganin girman Ahmad da Musty Farhan da Fadil har mamakin girman yaran nake yi mutsy fa ya kamo tsawo na Amir ko in muka jera sai ace yayana ne ni daman gani ba Tsawo kuma ba wani jiki ba yar Firit don ma na kara kumari da a baya ne kila sai dai ace nice karamar su sai ko in anga Fuskar ta manya. Engr ne yayi gyaran murya kafin yace"Umma kad'ai kuka sani ko..? Sai alokacin su Amir suka gansu kunya ta kama Anum baki bude tace"Laaa Baba.." Amir ma yace"Baaba.." Sai su Ahmad suka tsaya suna kallon su,Amir yace"Sannu da zuwa Baba.." Makale kafad'a ya yi kamar yaro kafin yace"No..Oya nima hug irin wanda kuka bama Umman ku" Sai suka tafi a tare suka fada jikinsu ya Rungumesu cikin Fara'a. Ahmad da Musty suka kalleni sai nayi mirmishi na gyada musu kai ganin suma yana mika musu hannu. Sakin su Amir yayi ya rumgumosu yana Fadin"Yauwa ya'yan Umma da Baaba.." Harda su Farhan daya bayan Daya ya dinga dagasu yana kuma kiran sunayen su mamaki ya cika su Musty yace"Kai ya sunan ka tunda mu kasan sunan mu.? Yana dariya yace"Ni sunana Baaba baka ji su Amir sun kirani da Baaba ba..? Musty ya kallesa ya kara kallonsa kafin yace"Baaba..? Cikin alamun tambaya ni ya kallah alamun hakane..? Ina shirin nayi mgana sai kawai muka hada ido da Yaya Ishaq ya kureni da ido sai na kasa mgana na maida kaina kasa. Ahmad ne ya yi karaf yace"Sunan ka da mamanka ta saka maka" Engr ya kwashe da dariya,irin Dariyan da yake yi in yana jin Nishadi. kafin yaja kumatun Ahmad yace"Sunana da mamana ta sakamin Abdulbasit ne." Zai kara mgana Anum tayi saurin cewa"Ahmad shima Baban mu ne kamar Daada.." Sai ya washe baki yana Fadin"Baaba..Sai su Farhan suka Dauka shi kuma yana ta amswa da Fara'a ina ganin Fara'ar take fuskarsa ta kaunan yara acikin idanuwansa. Zainab ta ce mu karisa ciki muna Tsaye sanda ya mike Dauke da Farhan da Fadil lokaci daya yana rike da Hannun Ahmad,Su Anum suka bi bayansa kallona yake yi da alamun nagode Fa'iza kin ga ma bani komai. Tunda kika saka na zama Uban ya'yanki nima. Sai da muka kariso falon naga Mama ita tafara gaisheni sai na sauko daga kan kujera na duka ina gaisheta har Gaban Abada Mama uwa ce agareni bazan taba kin darajata ba ta amsa cikin Fara'a da nauyi. Engr ma yadda nayi haka yayi sai naga Mama na kauda kai tana sharan kwallah fadi take yi'"Allah ya baku zaman lafiya Allah ya kad'e Fitina" Ba kunya Engr ya rika amsawa da Ameen Ameen. Sai alokacin na iya dagowa na gaida Yaya Ishaq ya amsa fusakarsa cikin yanayin da ban gane ba. Zainab Shema'u ta saka ta kawo mana ruwa da lemu,yaran kuma suna tare da Engr duk tambayan da suka yi masa sai ya basu amsa shi fa yadda yake iya zama da manya haka yake iya zama da yara kafin wani Lokaci su Ahmad sun saki jiki da shi. Ishaq na gefe kamar mutum mutumi sai dai mirmishi kad'ai yake yi. Allah kadai yasan Halin da zuciyarsa take ciki alokacin,Wlh tallahi bai taba sanin haka yake tsananin son Fa'iza ba sai da ta auri waninsa. A yadda yayi fama da zuciyarsa akan soyayyar Fa'iza ya tabbata ko Zainab da take zabinsa bai sota haka ba. Ya shiga jarabawar rayuwa da baya Fatan wani ya shiga irinsa Son matar da ba Muharaminsa ba,tunda Zainab ta fad'amasa zuwan Fa'iza da Engr ya rasa natsuwarsa sai yaji abunda ya Binne na soyayyar Fa'iza na neman taso masa, ganinta da yadda ta sauya sai ya kara Saranda ya tabbatar ma kansa Fa'iza ta samu wanda ya fisa komai da komai sannan ganin irin kaunar dake idanuwan Engr ya tabbatar masa da cewa in