← Book details Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 37 OF 71

Sashe 37

Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read

******

Watan mu daya da Haduwa da Engr,Makarantar Haddanmu ta kiramu akan Karban shahada, mu goma Cif zamu karbi shahadar Haddan Qur'ani izifi Sitti,Dole zan koma karofi,Har ga Allah har zuwa Lokacin Abba baisan Halin da ake ciki ba ta bangaran Ishaq ba,ammh sun yi mgana da Engr sosai ta waya akan aurena yace masa ba shi kadai ke da ni ba ina da yan'uwa da iyaye achan karofi zai je ya same su,abunda suka yanke zai Fada masa da haka ma suka rabu.
Sai dai kuma bayan ya samu Inno sun Tattauna itama ta goyo bayan yaje ya samu Goggo da Mallam su tattauna,Ya shirya tafiya ma karofi sai kuma Ishaq ya kirasa da wata mganar data sa ya kasa gane ina aka nufa.
Abunda ya faru shine Mama ta yi ma Ishaq maganar yaushe za'a maida auran..?
Har ga Allah ya ma manta da sai an kara Daura mana aure,ya dauka kawai zan dawo ne ita ta ankar da shi,Sai alokacin ya tuna da sai fa an kara daura wani auran shine Dalilinsa na kiran Abba bayan sun gaisa da Tambayan aiki Ishaq cikin jin nauyi ya yi kasa da Murya cikin Ladabi kafin yace"Abba nace ba..yaushe kuka saka ranar Daurin auran..?
Sai abun ya bama Abba mamaki cikin mamakin yace"Daurin aure kuma..?
Auran wa..?
Ishaq na jin kunya yace"Ko bata fad'a maka ba ne Abba..?
Abba da ya fara hasaso abunda ke faruwa yace da sauri'"Ita wace ce  bata fad'amin ba? kuma me zata fad'amin"
Sai ishaq ya yi tunanin kila Fa'iza bata fad'ama Abba ba tana jin nauyi sai yace"Fa'iza mana Abba.
kan mganar maida auran mu ni da ita"
Sai Abba yaji zufa na ketomai cikin mamaki yace"Topaha..Fa'iza bata fad'amin ba ban ma san da wannan mganar ba"
Ishaq yace"To ban san meyasa bata fada maka ba,ammh ta sanar da yara da Zeey cewa zata dawo har ma ina mata shirin dawowa Abba"
Sai Abba ya jinjina kai kafin yace"Ba shakka. to ka bani Lokaci zan yi mgana da ita abunda muka yanke zan nemeka a waya"
Da haka suka rabu da Abba da ransa ya baci a fili ya furta"Meyasa Fa'iza zata min haka..?domin na bata dama bai kamata tayi wasa da Hankalin mutane haka ba"
Shi kunyarsa Daya Engr ya zai yi da shi..?da tasan tun farko ga inda zata koma meyasa ta amsa masa ai da ta basa Hakuri gabadaya ya shiga Tunani Saboda wlh tallahi yana ganin girman Engr baya so ya yi abunda kuma rai zai zo ya baci ta turo sa sannan kuma ga Ishaq da wata mgana a gefe.
Da bacin ran ya koma gida sai kuma Ammi ta tare shi da mganar Fa'iza zata koma karofi Saboda walimar Saukar su,Da farko ya so ya kirata ne ya tambayeta ammh sai kuma ya Sauya shawara yana so yagani ko zan nemesa da mganar ammh har akayi kwana Biyu bai ji komai daga bangarena ba, sannan Engr ma ya kirasa akan ko yaje karofin yace bai je ba sai weekend sai ya Fahimci shi kan shi bai san abunda ke faruwa ba in ma ni na sani to ban Fad'a masa ba.
Ranar alhamis da Daddare bayan ya Dawo gida yana shirin kirana sai ga shi na shigo Falon,da rana ya Kira Nana Fadila sun yi mgana itama yaji mganar komen a bakinta sai bai nuna mata yaji wani batu ba,Abunda kuma ya kara Dauremai kai da suka yi mgana da Mallam mijin Goggo yace masa zai zo akwai mganar da zasu yi Bude bakin Mallam sai cewa ya yi"Masha Allah Allah ya kaddara da Sauran zama Tsakanin Fa'iza da Yaron nan ai gwara ta koma Saboda ya'yan Dake Tsakani"
Sai ya tabbatar da ba shi kadai yaji wannan mganar ba mutane da Dama sun sani,da ya dawo yau ya tambayi Ammi kan yanayin alakata da Engr Ammi cikin Fara'a ta labartamasa yanayin Farincikin da nake ciki sai ya gano shi Ishaq bai yi mgana dani ba abaki yaran yaji mgana ya hau ya zauna kuma ya yad'a labarin batare da ni na sani ba lalle ko in hakane akwai kura ya zama Dole nasan Halin da ake ciki na kuma yi gaggawan fidda Guda daya in Engr na bama Dama zai bama Ishaq hakuri in kuma Ishaq ne zai san yadda zai lallabi Engr yasan shi da Takwalli da yakana.
Ni daman nazo sanar da Abba ranar asabar zan tafi Karofi ne saboda walimar mu,sai kuma naji yace yana son mgana dani ni yanzu nauyin Abba nake ji saboda Engr,naji Abba na mgana ammh har ga Allah ban ji da kyau ba ina chan ina tunanin hirarmu da Engr na rigiman sai yazo walimarmu har karofi daganan ma sai na nunasa wajen Dangi.
Kamar daga sama naji Abba na ambaton Ishaq da mganar ya kirasa yana tambayansa Lokacin da da suka sanya na auran mu.
Sai na kalli Abba cikin wani yanayi kamar ban ji da kyau ba nace"me kace Abba..?
Sai da Abba ya kara maimaitamin sannan na gane in da aka dosa gabana ya fadi cikin rawan murya nace"Abba..Ni kuma..?
Daman ka ba shi dama ne..?
Abba ya girgiza kai kafin yace"Ke yace kin basa dama kin fad'ama yaran da Antynsu"
Sai na tuna mganar muka yi da Anum,Da mganar mu da Zainab sai naji hankalina ya yi bala'n tashi cikin tashin hankali da rawan murya nace"Ni na fad'a ne wasa nake musu Abba.."
Kai tsaye Abba yace"Zabi naki ne har yanzu Fa'iza ki yi tunani in Ishaq din kika zaba falillahil hamdu sai na sallami Engr, in kuma Engr kika zaba sai na bama Ishaq hakuri ki yanke hukunci daga yanzu zuwa ranar da zan zo Karofi yaushe ne Walimar taku..?
Cikin rawan murya nace"Sati mai zuwa"
Abba ya jinjina kai kafin yace"To kiyi tunani a tsanake kafin lokacin aranar zamu tsaida mgana in sha Allahu.
Tashi ki je, jibin Direba zai kai ki zan barma mamanku Sako ta baki."
Daga haka ya sallameni na mike jikina na wani girgiza zuciyata na rawa.
Allah ne ya kaini d'aki lafiya ko gani bana yi,gabadaya idanuwana sun yi Duhu kamar yadda zuciyata ke cikin Duhu da Sarkakiya.

*Janafty*

*KNKB3013*

*Goron Tula*

*Ingantaccen maganine dake saukarda niimar mace sannan dadin dadawa fruit ne ga dadi abaki zakine dashi chakwai sannan bashi da wata illa yadda kikasan fruit haka yake*
*yana da matukar kyau da tasiri ga ma aurata daga mace harna mijin Kuma munada Syrup nasa da akataceshi sannan aka hada da ingantattun magunguna dasuke temakawa ma aurata kwarai don inganta lafiyarsu dakuma maganin matsalarsu ta auratayya yana saukar da niima sosai yana karawa mace dadi fiye dazatanku sai kingwada zak ibada labari insha Allah*

*Sannan akwai zumar kiba*
*Duk macen dake son ta murmure tayi kyau taciko tatada komad'a sosai shaf dinta yafito sosai da sosai to tasha wannan zumar insha Allah zaki gode min*

*Zumar gyara nono*
*Zasu yi kyau suciko ammanfa bawai su tsaya ba😄 zadai suciko suyi kyau sosai insha Allah*

*Zumar hips*
*Indai kinsha zumar nan to hips dinki zai bude zasu yi kyau suciko sosai zaki godemin nina fadamiki insha Allah*

*Note magungunan mu ingantattune basu da side effects kokad'an anyisu da ingantattun*
*magunguna sosai*
*Location Gombe munaturawa ko ina 08030861857*

*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*
Chapter 37 · 0% Book details