Sashe 19
Kana Naka Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kimanin Sati biyu ina cikin Iddata zuwa Lokacin tuni Labari ya bazu a ko'ina wanda ma ba'ayi Tunani ba duk sun samu Labari,su Nana Fatima bakin Ammi sukaji duka sun kirani suna min nasiha sai na nuna musu ba komai,Anty Binta ko kunya kirana tayi a waya tana cemin yanzu sai da na kashe wannan auran..?ni kuma sai na bata amsa da cewa daman Tuntuni ya kamata ya mutu Bai mutu bane Daganan bata kara mgana ba Yaya Asiya kuma duk sai jikinta ya yi sanyi tace"Fa'iza zawarci ba Dadi"
Kai Tsaye nace"Ni ba zawarci zan yi ba makaranta zan koma, na karo ilimi sannan zan bunkasa kasuwancina ke dai kiyi min fatan alheri"
Jin haka yasa sai ta bini da addu'a kawai ganin Nima ban damu ba.
Hankalina kwance abuna har yar kiba nayi ina mgana da su Anum ta wayar Zainab tunda itama ta kirani tana Fadin"Yanzu shikenan mamam Amir..?ina mirmishi nace"Ba shikenan ba Maman Fadil zumunci Allah ne ya had'a sannan akwai ya'ya tsakani ke ce kuma uwar su ko Auran su ya tashi ni yar kallo ce"
Ban bata Damar da zata rokeni ba na cikata da mgana sai ta kasa mgana Sannan yaran kuma ko da yaushe sukace Umma yaushe zaki zo..?Sai nace ina nan zuwa to sun ma Fahimci ina Fade ne kawai sun daina Damuna ammh ban yi wasa ba duk sanda mukayi waya zan ce su kula da salla da Azkar ban da kawayen banza su taimaki kannensu sannan na roki Anty Fadila dom Allah ga amanar ya'ya na nan ne tace Haba kada na Damu kamar suna gidanta ne tunda nan suke weekend.
Har Badariya sai da ta kirani tana jimami nace mata tayi min Fatan alheri a bakinta nake jin Hajiyar Dala nata Fad'an wai da na kashe aurena ina da wanda yafi Ishaq din ne.?taga mai kwasata wato ina Takama muna da Uba mai arziki.
Ban ce komai ba sai mirmishi kawai da nayi, na jima da sanin Hajiyar Dala bata kaunarmu kuma bazata taba ba shiyasa nima na shata mata Layi,ranar da Badariya ta Fad'amin ta kira Goggo tana fad'a ta kuma ce a bani waya ta maimaita min abunda Badariya tafad'amin ni ko ban yi mata shuru ba nace"Bani da shi Goggo,kuma bana Fatan samu ma. saboda sha'awan aure da Namiji dalilin ishaq yasa ya fita a raina"
Sai mgana ta yasa jikinta yayi sanyi bata kara mgana ba sai cewa tayi"To su yaran fa wa kika bar ma su.?
Nace Mata Allah sai ta kashe wayarta a raina naji Fes,duk da Ishaq din na Damuna da kira ban taba Dauka ba. Text din ban hakuri safe da yammah har da na Turanci in nagani Dariya nake yi na goge a raina nakan ce ya manta Fa'iza ba Turanci ne Sulhu yake nema ni ko Har Abada Ishaq ya fita raina sannan yayi sanadiyar da Sauran maza suma suka fita a raina.
Rayuwata nake yi cikin Farinciki bani da matsalan komai ina sana'ata ban nemi komai na rasa ba, duk wata Abba na sakamin kudi bayan riban da nake samu,yan'uwana dukkansu yanzu Tallalina suke yi kamar kwai Goggo da mallam sai abunda nace duk kuma abunda bana so wlh suma sun bar shi kenan.
Ni da kaina na kira Hajiya na fadamata Mutuwar aurena Hajiya bataji Dadi ba ammh sai tamin Fatan alheri da kuma Fatan kada na bar sana'a ta shi zai taimakeni sannan a Satin har karofi tazo mun jima tana mgana dani shawarwarim da uwa zata bama yarta shi ta bani ta nemi na koma makaranta nace mata bani da Ra'ayi sai ta kyaleni ta kawo min kayan kwalliya sannan ta kawo ma Goggo atamfa,ni dai duk kyautar da su nayi ga su Anty Nasara har da Hafsah da Khadija na ijiyemawa,sun yi mganar har sun gaji sun san ba ruwana da kwalliya balle ina cikin iddata.
Sa'adatu ma da na fad'amata Har Karofi tazo ta jajantamin sai yammah tatafi bayan ta fadamin Haruna ya samu aikin Bijilanti,nayi mata Murna da na Rakota zaure zata tafi sai ta kalleni kafin tace"Kai Maman Amir kinga yadda kika yi kiba kika sauya kuwa..?
Ina Dariya ban yi mgana ba sai tace"Allah ya kawo bazawari nagari"
Da Sauri na Tareta ina Fadin"A'a ni yanzu namiji baya bani sha'awa kasuwancina zan bunkasa domin goben ya'yana"
Kai tsaye tace"An ya..?da kuruciyarki fa wadanda suka fiki ma ai sun yi aure"
Dariya nayi kafin nace"Bani da Ra'ayi kwata kwata kuma ina kuruciya anan Shekarata 34 fa"
Sa'adatu tace"Uhm ko dai da Baban Amir din za'a daidaita?
Mganarta yasa sai da gabana ya fadi araina nace ba Ameen ba Daganan na Sauya mganar sai itama ta barta. Dubu Biyar na bata tana ta godiya sannan na bata garin Danwake da yawa na kuma bata na ce ta kaima Habiba sun yi min abunda bazan manta da su ba.
Ina gida bana fita ko'ina ina kuma lissafin iddata ko alama ban taba mgana da wani nace masa Ishaq na damuna da kira da sako ba,gogewa ma nake yi saboda kada wani ya gani Ranar wata Jumma'a da Daddare aranar ina da kwana talatin da Hudu da Iddata,misalin karfe takwas da wani abu na Dare naga Ishaq nata kirana ban Dauka ba,Kiran ne naga yayi yawa yasa na daga sai naki mgana maimakon naji muryansa sai naji Karadin Anum tana fadin"Umma Umma"
Da Sauri nace"Na'am Anum din Umma"
Cikin zumudi tace"Umma Yaya Amir ya yi na 1st postion a makaranta. yau aka bamu Hutu an basa kyauta Umma"
Farinciki ya rufeni Cikin Dariya nacr"kai masha Allah..Amir din Umma yayi kokari ke fa nawa kika yi..?
Da zumudi tace"Umma na 8th nayi fa kinsan bamu jima da fara zuwa ba aka fara Exams"
Cikin nuna jinjinata nace"Dakyau Anun din Umma Ahmad da Musty fa..?
nan ta rika zayyanomin abunda sukaci ina saka albarka Amir bai karbi wayar ba sai Musty daga shi Sai Farhan,yana ta min hiran an bama Yaya Amir kyauta nace dakyau ina tambayan Fadil suka bashi yana min Hira da gauranci ina Dariya wayar tsakanin yaran ta fara zagayawa wani har sau biyu ma irin su Ahmad da Farhan da basa gajiya daga karshe Anum ta kwace wayar sai nake tambayata ina Amir..?tace yana Daki ta kai masa ne sai nace ta kyalesa Antynsu na tambaya tace min Tana Daki ko da yaushe daman in na Tambayeta zasu ce tana ciki na Fahimci zainab bata son yara kwata kwata.
Mamakin jimawar mu muna mgana nayi yasa nace ma Anum"Waya baki waya haka Anum..?
Kai tsaye tace"Ta Daada ce fa shiya ce bari ya kiraki mu fad'a miki"
Ba'a sirri da yaro ina ji ana mgana ban dai jin me ake fadi naji Anum tace"Me kace Daada..?
Sai araina nasan wata mganar zai ce ta fadamin kamar ina wajen sai ji nayi tace"Umma Daada yace yaushe zaki zo..?
Ban bata amsa ba na fara Hamman karya ina fadin"Oya sai da Safe barci nake ji"Ba ason ranta ba na katse wayar a fili na yi mirmishi ina mamakin Rashin kunya a wajen Ishaq sai yanzu yasan ya'yana suna da Rana.
Nasan kunya ce ta hanasa zuwa garin nan ammh a juri zuwa rafi tunda bai da kunya zai iya zuwa.
Kwana Biyu Tsakani Zainab ta Haihu aiki akayi mata An cire mata yarta mace kyakyawa nima Anty Fadila ta fadamin Tunda ita Ishaq ya taso cikin Dare sai tace ya kawota asibitin datake aiki a bakinta nake jin zainab din ta wahala karfinta ne ya kare sannan yarinyar ta karkace acikinta shiyasa akayi mata aiki.
Dole Mama ta koma Lagos itama Zainab din daga Adamawa yayar Hajiyar Halima aka tura mata ta kula da ita,aikin yayi kwana biyar suka sallameta suka koma gida,na kirata nayi mata barka tace tana jirana sai nazo barka ina Dariya nace zan bata mamaki kuwa.
Ba suna suka yi ba tunda ga nisa ga kuma kashe kudi,Sai dai Dr.Lawal da Hajiya Halima sun je sun ga yarsu da jikarsu sai kanwarta zuzu da ta gama karatu ta je aka barta achan sai Anty Fadila da yaranta,yarinya taci sunan FA'IZA.
Da Anty Fadila ta fad'amin sunan yarinyar sai da Dariya ya kamani shima yayi ta kirana ban Dauka ba.
Zainab ta kirani tace sun yi min takwara in dawo ko saboda little Fa'iza,yara kuma suna ta murna an haifa musu bby,Anty Fadila tayi bajinta kamar ni ce na Haihu, kayan alfarma tayi ma Zainab da Little Fa'iza har Abba da yaji sunan Bby sai da yayi Dariya Tausayin Ishaq kad'an ya tsirga masa.
Sai dai kuma ina! bakin alkalami ya riga da ya bushe.
*Janafty*
*KNKB3007*
*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWOWINRL ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY*
*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*
Kai Tsaye nace"Ni ba zawarci zan yi ba makaranta zan koma, na karo ilimi sannan zan bunkasa kasuwancina ke dai kiyi min fatan alheri"
Jin haka yasa sai ta bini da addu'a kawai ganin Nima ban damu ba.
Hankalina kwance abuna har yar kiba nayi ina mgana da su Anum ta wayar Zainab tunda itama ta kirani tana Fadin"Yanzu shikenan mamam Amir..?ina mirmishi nace"Ba shikenan ba Maman Fadil zumunci Allah ne ya had'a sannan akwai ya'ya tsakani ke ce kuma uwar su ko Auran su ya tashi ni yar kallo ce"
Ban bata Damar da zata rokeni ba na cikata da mgana sai ta kasa mgana Sannan yaran kuma ko da yaushe sukace Umma yaushe zaki zo..?Sai nace ina nan zuwa to sun ma Fahimci ina Fade ne kawai sun daina Damuna ammh ban yi wasa ba duk sanda mukayi waya zan ce su kula da salla da Azkar ban da kawayen banza su taimaki kannensu sannan na roki Anty Fadila dom Allah ga amanar ya'ya na nan ne tace Haba kada na Damu kamar suna gidanta ne tunda nan suke weekend.
Har Badariya sai da ta kirani tana jimami nace mata tayi min Fatan alheri a bakinta nake jin Hajiyar Dala nata Fad'an wai da na kashe aurena ina da wanda yafi Ishaq din ne.?taga mai kwasata wato ina Takama muna da Uba mai arziki.
Ban ce komai ba sai mirmishi kawai da nayi, na jima da sanin Hajiyar Dala bata kaunarmu kuma bazata taba ba shiyasa nima na shata mata Layi,ranar da Badariya ta Fad'amin ta kira Goggo tana fad'a ta kuma ce a bani waya ta maimaita min abunda Badariya tafad'amin ni ko ban yi mata shuru ba nace"Bani da shi Goggo,kuma bana Fatan samu ma. saboda sha'awan aure da Namiji dalilin ishaq yasa ya fita a raina"
Sai mgana ta yasa jikinta yayi sanyi bata kara mgana ba sai cewa tayi"To su yaran fa wa kika bar ma su.?
Nace Mata Allah sai ta kashe wayarta a raina naji Fes,duk da Ishaq din na Damuna da kira ban taba Dauka ba. Text din ban hakuri safe da yammah har da na Turanci in nagani Dariya nake yi na goge a raina nakan ce ya manta Fa'iza ba Turanci ne Sulhu yake nema ni ko Har Abada Ishaq ya fita raina sannan yayi sanadiyar da Sauran maza suma suka fita a raina.
Rayuwata nake yi cikin Farinciki bani da matsalan komai ina sana'ata ban nemi komai na rasa ba, duk wata Abba na sakamin kudi bayan riban da nake samu,yan'uwana dukkansu yanzu Tallalina suke yi kamar kwai Goggo da mallam sai abunda nace duk kuma abunda bana so wlh suma sun bar shi kenan.
Ni da kaina na kira Hajiya na fadamata Mutuwar aurena Hajiya bataji Dadi ba ammh sai tamin Fatan alheri da kuma Fatan kada na bar sana'a ta shi zai taimakeni sannan a Satin har karofi tazo mun jima tana mgana dani shawarwarim da uwa zata bama yarta shi ta bani ta nemi na koma makaranta nace mata bani da Ra'ayi sai ta kyaleni ta kawo min kayan kwalliya sannan ta kawo ma Goggo atamfa,ni dai duk kyautar da su nayi ga su Anty Nasara har da Hafsah da Khadija na ijiyemawa,sun yi mganar har sun gaji sun san ba ruwana da kwalliya balle ina cikin iddata.
Sa'adatu ma da na fad'amata Har Karofi tazo ta jajantamin sai yammah tatafi bayan ta fadamin Haruna ya samu aikin Bijilanti,nayi mata Murna da na Rakota zaure zata tafi sai ta kalleni kafin tace"Kai Maman Amir kinga yadda kika yi kiba kika sauya kuwa..?
Ina Dariya ban yi mgana ba sai tace"Allah ya kawo bazawari nagari"
Da Sauri na Tareta ina Fadin"A'a ni yanzu namiji baya bani sha'awa kasuwancina zan bunkasa domin goben ya'yana"
Kai tsaye tace"An ya..?da kuruciyarki fa wadanda suka fiki ma ai sun yi aure"
Dariya nayi kafin nace"Bani da Ra'ayi kwata kwata kuma ina kuruciya anan Shekarata 34 fa"
Sa'adatu tace"Uhm ko dai da Baban Amir din za'a daidaita?
Mganarta yasa sai da gabana ya fadi araina nace ba Ameen ba Daganan na Sauya mganar sai itama ta barta. Dubu Biyar na bata tana ta godiya sannan na bata garin Danwake da yawa na kuma bata na ce ta kaima Habiba sun yi min abunda bazan manta da su ba.
Ina gida bana fita ko'ina ina kuma lissafin iddata ko alama ban taba mgana da wani nace masa Ishaq na damuna da kira da sako ba,gogewa ma nake yi saboda kada wani ya gani Ranar wata Jumma'a da Daddare aranar ina da kwana talatin da Hudu da Iddata,misalin karfe takwas da wani abu na Dare naga Ishaq nata kirana ban Dauka ba,Kiran ne naga yayi yawa yasa na daga sai naki mgana maimakon naji muryansa sai naji Karadin Anum tana fadin"Umma Umma"
Da Sauri nace"Na'am Anum din Umma"
Cikin zumudi tace"Umma Yaya Amir ya yi na 1st postion a makaranta. yau aka bamu Hutu an basa kyauta Umma"
Farinciki ya rufeni Cikin Dariya nacr"kai masha Allah..Amir din Umma yayi kokari ke fa nawa kika yi..?
Da zumudi tace"Umma na 8th nayi fa kinsan bamu jima da fara zuwa ba aka fara Exams"
Cikin nuna jinjinata nace"Dakyau Anun din Umma Ahmad da Musty fa..?
nan ta rika zayyanomin abunda sukaci ina saka albarka Amir bai karbi wayar ba sai Musty daga shi Sai Farhan,yana ta min hiran an bama Yaya Amir kyauta nace dakyau ina tambayan Fadil suka bashi yana min Hira da gauranci ina Dariya wayar tsakanin yaran ta fara zagayawa wani har sau biyu ma irin su Ahmad da Farhan da basa gajiya daga karshe Anum ta kwace wayar sai nake tambayata ina Amir..?tace yana Daki ta kai masa ne sai nace ta kyalesa Antynsu na tambaya tace min Tana Daki ko da yaushe daman in na Tambayeta zasu ce tana ciki na Fahimci zainab bata son yara kwata kwata.
Mamakin jimawar mu muna mgana nayi yasa nace ma Anum"Waya baki waya haka Anum..?
Kai tsaye tace"Ta Daada ce fa shiya ce bari ya kiraki mu fad'a miki"
Ba'a sirri da yaro ina ji ana mgana ban dai jin me ake fadi naji Anum tace"Me kace Daada..?
Sai araina nasan wata mganar zai ce ta fadamin kamar ina wajen sai ji nayi tace"Umma Daada yace yaushe zaki zo..?
Ban bata amsa ba na fara Hamman karya ina fadin"Oya sai da Safe barci nake ji"Ba ason ranta ba na katse wayar a fili na yi mirmishi ina mamakin Rashin kunya a wajen Ishaq sai yanzu yasan ya'yana suna da Rana.
Nasan kunya ce ta hanasa zuwa garin nan ammh a juri zuwa rafi tunda bai da kunya zai iya zuwa.
Kwana Biyu Tsakani Zainab ta Haihu aiki akayi mata An cire mata yarta mace kyakyawa nima Anty Fadila ta fadamin Tunda ita Ishaq ya taso cikin Dare sai tace ya kawota asibitin datake aiki a bakinta nake jin zainab din ta wahala karfinta ne ya kare sannan yarinyar ta karkace acikinta shiyasa akayi mata aiki.
Dole Mama ta koma Lagos itama Zainab din daga Adamawa yayar Hajiyar Halima aka tura mata ta kula da ita,aikin yayi kwana biyar suka sallameta suka koma gida,na kirata nayi mata barka tace tana jirana sai nazo barka ina Dariya nace zan bata mamaki kuwa.
Ba suna suka yi ba tunda ga nisa ga kuma kashe kudi,Sai dai Dr.Lawal da Hajiya Halima sun je sun ga yarsu da jikarsu sai kanwarta zuzu da ta gama karatu ta je aka barta achan sai Anty Fadila da yaranta,yarinya taci sunan FA'IZA.
Da Anty Fadila ta fad'amin sunan yarinyar sai da Dariya ya kamani shima yayi ta kirana ban Dauka ba.
Zainab ta kirani tace sun yi min takwara in dawo ko saboda little Fa'iza,yara kuma suna ta murna an haifa musu bby,Anty Fadila tayi bajinta kamar ni ce na Haihu, kayan alfarma tayi ma Zainab da Little Fa'iza har Abba da yaji sunan Bby sai da yayi Dariya Tausayin Ishaq kad'an ya tsirga masa.
Sai dai kuma ina! bakin alkalami ya riga da ya bushe.
*Janafty*
*KNKB3007*
*TASTED & TRUSTED*
*GUDUYO NA TALLATA MUKU INGANTATUN SAIWOWIN MUTANAN CHADI DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZAR AMARE, MASU JEGO DA WADDA TAKE SON GYARA KANTA*.
*AN GWADA ANGA INGANCINSA SHIYASA NA KE TALLATA MUKU DA K'ARFIN GUIWATA*.
*ABIN BIRGEWA DA WANNAN SAIWOWINRL ZAKI YI AMFANI DA SU SAMA DA SAU DAYA.*
*AKWAI FULL PACKAGE, AKWAI RABI, TA YADDA KOWA ZAI IYA SIYA*.
*SANNAN BABU BAURI NA TASHIN HANKALI.*
*DA KANKI ZAKI DAFA ABAR KI, KOMAI ANA SAKA WA A CIKI*.
*SHIN KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR, KO KUWA KE CE KIKE SON GYARA KANKI?*.
*KAYANA NATURAL NE DOMIN SAIWOWI NE DA AKE HAKOSU A DAJIKAN CHADI. BAYAN SAUKAR DA GAMSUWA HAR YAQI SUKE YI DA DRYNESS DA KUMA INFECTIONS.*
*AKWAI NA TSUGGUNO DA YAKE HA'DE MACE TA MATSE.*
*AKWAI HADADDUN DAKA NA SHA DA MADARA KO NONO WANDA BABU ALGUS*.
*SANNAN AKWIA GADALIN MATA NA ASALI, WANDA SHA YANZU NE MAGANIN YANZU DA IKON ALLAH*
*DUKKANSU TESTED & TRUSTED NE*.
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU*
*08032773332*
*DOMIN KARIN BAYANI, SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*.
*NATION WIDE DELIVERY*
*Pay N500 Regular,Via 0552179550 Jamila Umar gt bank,Vip 1000.*
*09069067488*